Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya gabatar da korafin hare-haren kyamar baki da kyamar ’yan Afirka da ake kai wa ’yan Afirka da sauran ’yan kasa a Afirka ta Kudu ga Tarayyar Afirka (AU), yana mai gargadin cewa wadannan hare-hare na lalata hadin kan nahiyar, zumunci da zaman lafiya tsakanin al’ummomi.
Shugaban Kasar ya kuma bukaci shugabannin Afirka su dauki matakin gaggawa, ciki har da sanya batun cikin ajandar taro na Zama na 40 na Majalisar Tarayyar Afirka, wanda za a gudanar a watan Janairu na 2027.
Tinubu ya bayyana matsayin Nijeriya ne a wani sako da Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, ya gabatar a madadinsa a Zama na Musamman na 21 na Majalisar Tarayyar Afirka (AU) da aka gudanar a Luanda, Angola.
Da yake wakiltar Shugaban Kasa a taron, Mataimakin Shugaban Kasa Shettima ya ce Tinubu ya bukaci AU ta sanya batun cikin ajandar Zama na 40 na Majalisar AU da za a gudanar a Janairu 2027, tare da kira ga shugabannin Afirka da su sake jaddada aniyarsu ta tabbatar da tsaro, kariya da mutuncin dukkan ’yan Afirka.
Ya ce, “Nijeriya na son bayyana damuwarta game da hare-haren kyamar baki da kyamar ’yan Afirka da ake maimaitawa a kan ’yan Afirka da sauran ’yan kasa a Afirka ta Kudu.
“Duk da cewa mun amince da ’yancin Afirka ta Kudu na aiwatar da dokokinta na shige da fice, tare da amincewa da gudummawar da take bayarwa ga nahiyar, Nijeriya na jaddada cewa irin wadannan hare-hare na lalata hadin kan Afirka, hadin kai da zaman lafiya, don haka suna bukatar kulawar gaggawa daga dukkan kasashen Afirka.
“Saboda haka, Nijeriya na kira ga wannan babban taro da ya sanya batun cikin ajandar Zama na 40 na Majalisar AU da za a gudanar a Janairu 2027, domin tattaunawa da daukar matakin da ya dace.”
Tinubu ya kuma yi kira da a karfafa kokarin nahiyar wajen yaki da kyamar baki da kyamar ’yan Afirka, yana mai cewa tattaunawa, diflomasiyya da hadin gwiwa su ne muhimman hanyoyin kare hadin kan Afirka.
Dangane da halin tsaro a fadin nahiyar, Nijeriya ta goyi bayan amincewa da Shirin Aiki na Luanda (Luanda Action Plan) a matsayin taswirar hanya ta zahiri wajen karfafa rigakafin rikice-rikice, tana mai cewa hana rikici ya fi rahusa kuma ya fi dorewa fiye da magance rikici bayan ya barke.
Tinubu ya ce, “A wajen Nijeriya, hana rikici ya fi sauki ta fuskar kudi kuma ya fi dorewa fiye da magance rikici.”
Ya yi gargadin cewa rarrabuwar kai a ayyukan samar da zaman lafiya da kuma kara tsoma bakin kasashen waje ta hanyar sojojin ketare, ’yan haya da kamfanonin tsaro masu zaman kansu na iya raunana hanyoyin AU na hana rikice-rikice da kuma ka’idar cewa Afirka ce ya kamata ta mallaki al’amuranta.
Ya kuma yi kira ga kasashen da ke kerawa da fitar da makamai da su karfafa hadin gwiwa da kasashen Afirka tare da hana karkatar da makamai da harsasai da aka kera a kasashensu zuwa hannun ’yan ta’adda da sauran kungiyoyin masu dauke da makamai da ba na gwamnati ba.














