Gwamnatin Tarayya ta bayyana shirin sauya kakin NYSC da atamfar Adire da aka yi a Nijeriya, a wani ɓangare na gyaran da ake yi domin inganta shirin da kuma tallafa wa masana’antun cikin gida.
Ministan Harkokin Matasa, Ayodele Olawande ne, ya bayyana hakan a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Channels a ranar Alhamis.
Ya ce amfani da atamfar Adire, wanda ake samarwa a jihohin Ogun da Kwara, zai ƙarfafa masana’antun cikin gida tare da tabbatar da cewa kuɗin gwamnati na ci gaba da zagayawa da bunƙasa tattalin arziƙin Nijeriya.
Ministan ya kuma ce za a riƙa tura masu yi wa ƙasa hidima inda ya dace da abin da suka karanta.
Misali, waɗanda suka karanci fagen tsangayar ilimi za a tura su makarantu domin yin aikin da ya dace da ƙwarewarsu.
Dangane da tsaro, Olawande ya ce gwamnati na duba yiwuwar tura masu yi wa ƙasa hidima zuwa yankunan da suka yi karatu ko kuma suka saba da su, musamman wuraren da ake fama da matsalolin tsaro.
Ya ce hakan zai rage damuwar iyaye da masu yi wa ƙasa hidima, tare da sauƙaƙa tsarin tura su.
Ministan ya kuma ƙaryata rahotannin da ke cewa za a cire sojoji daga shirin NYSC, yana mai cewa wannan jita-jita ba gaskiya ba ce.














