Tsohon sanatan Kaduna ta tsakiya, Sanata Shehu Sani, ya bayyana cewa matsalolin tsaro da ake fama da su a sassan Arewacin kasar nan ba za su yi sauki ba sai lokacin da Musulmi da Kirista suka daura damarar hada kai wuri guda wajen dinke duk wata baraba a tsakaninsu.
Shehu Sani ya bayyana haka ne a zantawarsa da manema labarai a taron nuna kayan al’adu wanda gidan adana kayan tarihi da ke Jihar Kaduna ya shirya. Ya ce rashin jituwa tsakanin al’ummomi daban-daban na daga cikin abubuwan da suka ba wa miyagun kungiyoyi damar kara samun karfi a yankunan da ke fama da rashi tsaro.
Ya jaddada cewa babu wata dabara da za ta yi tasiri idan babu hadin kai da yardar juna tsakanin daukacin jama’ar kasa.
- Idan Jonathan Ya Tsaya Takara A 2027, Girmansa Zai Faɗi – Shehu Sani
- Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu
A cewarsa, “Idan muka tsaya bisa bambancin addini ko kabilaci, to babu wani shirin tsaro ko makami mai karfi da zai magance matsalar da ke addabar jama’a. Dole ne Musulmai da Kirista su fahimci cewa dukkaninsu su ne ke fuskantar barazanar kuma su ne za su iya shawo kanta idan suka hada kai.”
Sanatan ya kuma bukaci shugabanni na addinai da su ci gaba da taka rawar gani wajen wayar da kan mabiya tare da jaddada muhimmancin zaman lafiya da tabbatar da adalci a dukkan matakai.
Da yake bayani dangane da jirgin sojan Nijeriya da kasar Burkino Faso ta kama, ya ce babu wani dalilin kama jirgin sojan Nijeriya, yana mai cewa duk wata kasa ta san cewa idan jirgi ya samu matsala yana iya yada zango a kasarta daga bisani idan aka gano matsalar sai ya tashi ya tafi. Akan hakan ya gargadi mahukunta kasar da su gaggauta sakin jirgin sojan Nijeriya ba tare da wani bata loka
ci ba.














