ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wacce Kasa Ce Za Ta Lashe Gasar Kofin Afirka

by Abba Ibrahim Wada
6 months ago
Kofin

Gasar cin kofin nahiyar Afirka ta shekarar 2025, wadda aka shirya gudanarwa a Morocco daga ranar 21 ga watan Disamba, 2025 zuwa ranar 18 ga watan Janairun 2026, tana daga cikin gasannin da ba a iya hasashen kasar da za ta lashe ba a tarihin gasar.

Kuma tun da aka fara buga gasar a shekarar 1957 ba a taba samun gasar da ake hasashen kasashe biyar ko shida na iya lashewa ba kamar ta bana saboda yadda kasashe da dama suke da manyan ‘yan wasa. Baya ga Morocco mai masaukin baki, akwai wasu kasashe da dama da ake ganin suna kan gaba cikin jerin wadanda ka iya nasara, wato Senegal da Masar da Ibory Coast da kuma Aljeriya, wadanda tuni suka samu tikitin shiga gasar cin kofin duniya ta 2026.

  • Za A Fara Gasar Wasanni Ta Nakasassu Da Masu Bukata Ta Musamman Ta Sin
  • Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Taimaka Wa Kasashen Yankin Tsakiyar Afrika Karfafa Tsaronsu

Daya daga cikin abubuwan al’ajabi a gasar cin kofin nahiyar Afirka shi ne yadda ba a iya samun tabbacin kasar da za ta lashe ta. A karo na takwas na baya-bayan nan dai an samu zakaru bakwai daban-daban, inda Ibory Coast ce kadai ta samu kambu sau biyu daga cikin gasa biyar da suka gabata, a 2015 da 2024.

ADVERTISEMENT

Karkashin jagorancin mai koyarwa Walid Regragui, Morocco, kasar da ke kan gaba a jerin kasashen Afirka a jadawalin FIFA, ta taka rawar gani a fagen kwallon kafa a duniya a shekarar 2022, inda ta zama tawagar Afirka ta farko da ta buga wasan kusa da na karshe a gasar cin kofin duniya.

Ba kasancewa a gida ba ne kadai abin da ke kara wa tawagar kasar Morocoo kwarin gwiwa ba a gasar bana, amma tawagar na da babban buri na tabbatar da lashe gasar cin kofin kasashen Afirka karo na biyu tun shekarar 1976.

LABARAI MASU NASABA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

A gaban al’ummar kasarta, tawagar Morocco na da burin samun makoma irin ta Ibory Coast, wato nasara a gida amma ba tare da fargabar da ta fuskanta a zagayen farko ba.

Amma karbar bakuncin gasar ba lallai ba ne ya zame riba ba. A cikin karo 34 da aka gudanar da gasar tun daga shekarar 1957 (ciki har da gasar farko), sau 12 ne kacal kasar da ta karbi bakuncin gasar ta yi nasara, wato kusan kashi 35% cikin dari. Tun daga 2000, Tunisia (2004), da Masar (2006) da Ibory Coast (2024) ne kawai suka yi nasara a gida.

Kasar da ta fi fice a Afirka na da burin lashe kambu na takwas don kawar da bakin cikin kashin da ta sha a hannun Senegal a wasan karshen gasar 2022. ‘Yan wasan tawagar Masar na da ta hadin matasa da kuma gogaggu. Wannan garwayen ‘yan wasan na ba ta damar taka muhimmiyar rawa a wasannin nahiyoyi a kusan kodayaushe. Karkashin jagorancin Hossam Hassan, Masar tana wasa da sauri, yayin da ta ci gaba da amfani da dabarun wasa da aka san ta da su.

Omar Marmoush da Mostafa Mohamed su ne misalan ‘sabbin jini’ a tawagar, yayin da suke daukar darasi daga tauraron tawagar Mohamed Salah wanda ake hasashen zai taka muhimmiyar rawa a gasar bana a Morocco.

Bayan da ta lashe gasar cin kofin nahiyar Afirka a gida a shekarar 2024, tawagar Elepahants ta shiga gasar bana a matsayin mai rike da kambun gasar. Nan da nan wannan ya sanya ta zama cikin jerin wadanda ake kyautatawa zaton lashe gasar, wadda ta taba lashewa sau uku, ciki har da sau biyu a gasanni biyar na baya bayan nan.

A karkashin jagorancin Emerse Faé, tawagar Elephants ta isa Morocco da burin ci gaba da rike kambunta. Amma akwai alamun za ta fuskanci kalubale da dama daga wasu kasashen.

Tun lokacin da aka fara gasar cin kofin nahiyar Afirka (AFCON) a shekarar 1957, kasashe uku ne kawai suka iya kare kambunsu. Masar ta yi haka a shekarar 1957 da 1959, sannan kuma ta sake yi a 2006, 2008, da 2010. Ghana ta yi nasara a 1963 da 1965, Kamaru a 2000 da 2002.

Senegal, wadda ta lashe kambunta na farko shekara hudu da suka gabata bayan dogon jira da kuma rashin nasara biyu a matakin wasan karshe (2002 da 2019), ta kasance ‘yar takarar da za ta taka muhimmiyar rawa a gasar.

Bayan lashe gasar AFCON 2021, amma an fidda ta da wuri shekara biyu bayan haka, da alama ta fara samun daidaito a karkashin jagorancin Pape Thiaw, wanda ya gaji Aliou Cissé.

Yayin da tawagar ke dauke gogaggun ‘yan wasa kamar Sadio Mane da Kalidou Koulibaly da Idrissa Gueye, Lions na Teranga za su iya yin la’akari da cewa ta na da matasan ‘yan wasa masu hazaka da ke da gogewar yin nisa na gasar nahiyar.

Tawagar Senegal, da ta Morocco, su ne manyan tawagogin Afirka biyu a saman jadawalin FIFA, a matsayi na 18 da 12 bi da bi. Senegal, wadda ta mamaye rukuninta na neman tikitin shiga gasar cin kofin duniya ta 2026, za ta dogara kan ci gaban da ta ke samu ta fannin ‘yan wasa da don maimaita nasarar da ta samu a 2022.

Bayan rashin nasara sau biyu a gasar AFCON na 2021 da 2023 inda aka fitar da ita a matakin rukuni, tawagar Fennecs na son bude wani sabon babi a tarihinta na gasar. Bayan zamanin Belmadi, inda ta yi farin cikin nasara a 2019 sannan kuma ta yi rashin nasara biyu (CAN 2021 da Gasar Cin Kofin Duniya 2022), Algeria ta tunkari CAN 2025 da babban burin: sake kasancewa tawagar kwallon kafa da ke kololuwar wasa a nahiyar.

Domin cimma wannan burin, hukumar kwallon kafar kasar ta dogara ga koci Bladimir Petkobić, da kasar Serbia wanda ya yi suna bayan da ya horas da tawagar Switzerland da ta yi gogayya da manyan kasashen Turai. ‘Yan wasan da suka lashe gasar cin kofin Afrika a 2019 sannu a hankali sun dusashwewa, suna ba da dama ga sabbin matasan ‘yan wasa da suka hada da Fares Chaïbi da Houssem Aouar da Rayan Aït Nouri, da Badredine Bouanani.

Aljeriya ta kasance babbar abokiyar hamayya ga tawagogin ‘yan wasan nahiyar da dama, wadda za ta iya tabuka abin kirki a kowace gasa. Idan Petkobic ya sami nasarar daidaita tawagarsa, Fennecs na iya sake zama kamar tawagar da ta mamaye fagen wasan kwallon kafan Afirka a 2019.

 

Ko Nijeriya Za Ta Iya Taka Rawar Gani?

Tawagar Super Eagles ta Nijeriya ta tsinci kanta a rukunnin C a gasar bana inda za ta fafata da Tunisia da Uganda da kuma Tanzania. Super Eagles dai za ta nemi kawar da bakin cikin da ta fuskanta a wasan karshen gasar da ta gabata inda ta yi rashin nasara a hannun Ibory Coast a wasan karshe duk da cewa ita ta fara jefa kwallo a raga a wasan.

Nijeriya wadda ta ke da kambun AFCON guda uku, a shekarun 1980, 1994, da 2013, wanda hakan ya sanya ta zama daya daga cikin kasashen da suka fi samun nasara a gasar ta Afirka.

Kasancewa tana da manyan ‘yan wasa kamar su Bictor Osimhen da Ademola Lookman da ke buga wasa a manyan kungiyoyin kasashen Turai ana ganin cewa kasar za ta iya tabuka abin a zo a gani a gasar bana, duk da cewa dai rashin nasarar da ta yi a yunkurinta na samun gurbi a gasar cin kofin duniya na 2026 na sanya alamar tambaya kan rawar da za ta iya takawa.

Kociyan tawagar ta Nijeriya, Eric Chelle, na shirin kara inganta tawagar tasa da wasu sabbin ‘yan wasa guda hudu ko biyar domin tabbatar da cewa Super Eagles din ta kai bantanta a Moroko.

Wasu daga cikin sababbin ‘yan wasan da za a iya kira shi ne dan wasan baya na Blackburn Robers Ryan Alebiosu, wanda tsohon dan wasan bangaren matasa na Arsenal ne kuma a halin yanzu yana taka rawar gani a gasar Championship ta Ingila. Wani sabon dan wasan da aka sanya wa ido shi ne dan wasan tsakiya Ebenezer Akinsanmiro da ke zaman aro a kungiyar Pisa daga Inter a gasar Serie A ta Italiya.

Rauni zai hana dan wasan Nottingham Forest Ola Aina buga gasar, yayin da Bright Osayi-Samuel ke fama da rashin tagomashi a kungiyarsa ta Birmingham City ta Ingila.

Amma duk da haka ba za a iya cire rai cewa Super Eagles za ta taka rawar gani a gasar ba, saboda dimbin tarihin da ta ke da ita a gasar, kuma ana ganin ‘yan wasan za su zo da niyyar huce fushin rashin samun gurbi a gasar cin kofin duniya ta 2026.

Kofin
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Next Post
Kofin

Samarwa Sojoji Manyan Makamai Ne Mafita - Shugaban Ƙaramar Hukumar Bukuyum

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.