ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Kai, Hakuri Da Riko Da Addini Su Ne Jigon Zaman Lafiyar Nijeriya – Tinubu

by Sani Anwar
7 months ago
Addini

LABARAI MASU NASABA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Shugaba Bola Tinubu ya roki ‘yan Nijeriya, da su rungumi hadin kai, koyarwar addini, hakuri da zaman lafiya a matsayin ginshikan tsaro, kwanciyar hankali da ci gaban kasa.

Shugaban ya yi wannan kira ne a jiya a wajen taron kasa da kasa karo na 4 na Cibiyar Wayewar Musulunci da Tattaunawar Addinin Musulunci da aka gudanar a Kano.

  • Za A Gudanar Da Dandalin Tattaunawa Na Masana Na Jam’iyyar JKS Da KMT A Birnin Beijing
  • Akpabio: Ba A Canza Komai A Cikin Sabbin Dokokin Haraji Ba 

Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a, Mohammed Idris ne ya wakilce shi a wajen taron.

Tinubu ya yaba wa wannan cibiya da masallacin Sultan Bello Kaduna, bisa yadda suke ci gaba da gudanar da cudanya da juna da nufin samar da zaman lafiya da hadin kan kasa.

“Wannan taro, yana ci gaba da tabbatar da manufofin zaman lafiya da hadin kan al’ummarmu, ta hanyar tattaunawa. Ko shakka babu, an girmama ni da wannan gayyata da aka yi min,” in ji shugaban.

Ya kuma bayyana yadda taron ya mayar da hankali a kan abubuwan da marigayi Sheikh Mahmud Abubakar Gummi ya bari na alhairi da kuma ilmantarwa, inda ya bayyana cewa; fitaccen malamin addinin musuluncin ya taka muhimmiyar rawa wajen samar da hadin kai a lokutan da suka taka muhimmiyar rawa a tarihin Nijeriya.

“Sheikh Gummi, ya fahimci mahadar imani da siyasa, sannan kuma ya yi aiki kafada da kafada da hukumomi, bayan samun ‘yancin kai da yakin basasa, don inganta hadin kai da zaman lafiya,” in ji shi.

Shugaban ya ci gaba da bayyana Sheikh Gummi a matsayin fitaccen malami, wanda ya kawo gyara, kuma jigo a kasa wanda tasirinsa yake da matukar yawa a fannin addini.

“Ya kasance malami, wanda ya kawo canje-canje, mai ba da shawara, kuma fitaccen marubuci.

Ya shawarci tsararrakinsa da su yi duk abin da ya, domin samun hadin kan Nijeriya, a aikace da kuma addinance, ”in ji shi.

Da yake magana a kan kalubalen da kasa ke fuskanta a halin yanzu, Shugaba Tinubu ya bukaci ‘yan Nijeriya, da su yi watsi da labaran da za su raba kan al’umma, musamman wadanda ke nuni da cewa; ‘yan kasar ba ta da ‘yancin yin addini.

“Dole ne mu karfafa kudurinmu na samar da kasa dunkulalliya, sannan wajibi ne a tsaya tsayin daka, wajen dakile yunkurin da ake yi na bata Nijeriya a matsayin kasa da ke tauye ‘yancin addini,” in ji shi.

Ya jaddada cewa, tsaron kasa ba ya taba rabuwa da hadin kai tare da mutunta juna a tsakanin ‘yan kasa, ba tare kuma da la’akari da bambancin addini ko kabilanci ba.

“Tsaron kasarmu, yana da nasaba da hadin kanmu, hadin kanmu da mutunta bambancin addini, dole ne mu hada karfi da karfe wajen yaki da masu neman raba kanmu,” in ji shugaban.

Da yake jaddada kudirin gwamnatinsa na kare rayuka da dukiyoyi, Tinubu ya ce; ana daukar kwararan matakai na tunkarar matsalar rashin tsaro a fadin wannan kasa.

“Gwamnatina, tana yin aiki tukuru wajen kare rayuka da dukiyoyi tare kuma da aiwatar da yaki da ta’addanci ta kowane bangare,” in ji shi.

Addini
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027:Mata Shida Da Ke Takarar Neman Shugabancin Nijeriya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Dambarwa A Kasuwancin Iyalan Indimi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Illar Shan Taba Sigari Da Dangoginta
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin
Labarai

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Next Post
An Nada Liu Xianfa Wakilin Musamman Na Gwamnatin Sin Kan Harkokin Afirka

An Nada Liu Xianfa Wakilin Musamman Na Gwamnatin Sin Kan Harkokin Afirka

LABARAI MASU NASABA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026
Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

September 9, 2026
Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai

Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai

September 9, 2026
Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa

Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa

September 9, 2026
’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.