ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Kai, Hakuri Da Riko Da Addini Su Ne Jigon Zaman Lafiyar Nijeriya – Tinubu

by Sani Anwar
4 months ago
Addini

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Shugaba Bola Tinubu ya roki ‘yan Nijeriya, da su rungumi hadin kai, koyarwar addini, hakuri da zaman lafiya a matsayin ginshikan tsaro, kwanciyar hankali da ci gaban kasa.

Shugaban ya yi wannan kira ne a jiya a wajen taron kasa da kasa karo na 4 na Cibiyar Wayewar Musulunci da Tattaunawar Addinin Musulunci da aka gudanar a Kano.

  • Za A Gudanar Da Dandalin Tattaunawa Na Masana Na Jam’iyyar JKS Da KMT A Birnin Beijing
  • Akpabio: Ba A Canza Komai A Cikin Sabbin Dokokin Haraji Ba 

Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a, Mohammed Idris ne ya wakilce shi a wajen taron.

Tinubu ya yaba wa wannan cibiya da masallacin Sultan Bello Kaduna, bisa yadda suke ci gaba da gudanar da cudanya da juna da nufin samar da zaman lafiya da hadin kan kasa.

“Wannan taro, yana ci gaba da tabbatar da manufofin zaman lafiya da hadin kan al’ummarmu, ta hanyar tattaunawa. Ko shakka babu, an girmama ni da wannan gayyata da aka yi min,” in ji shugaban.

Ya kuma bayyana yadda taron ya mayar da hankali a kan abubuwan da marigayi Sheikh Mahmud Abubakar Gummi ya bari na alhairi da kuma ilmantarwa, inda ya bayyana cewa; fitaccen malamin addinin musuluncin ya taka muhimmiyar rawa wajen samar da hadin kai a lokutan da suka taka muhimmiyar rawa a tarihin Nijeriya.

“Sheikh Gummi, ya fahimci mahadar imani da siyasa, sannan kuma ya yi aiki kafada da kafada da hukumomi, bayan samun ‘yancin kai da yakin basasa, don inganta hadin kai da zaman lafiya,” in ji shi.

Shugaban ya ci gaba da bayyana Sheikh Gummi a matsayin fitaccen malami, wanda ya kawo gyara, kuma jigo a kasa wanda tasirinsa yake da matukar yawa a fannin addini.

“Ya kasance malami, wanda ya kawo canje-canje, mai ba da shawara, kuma fitaccen marubuci.

Ya shawarci tsararrakinsa da su yi duk abin da ya, domin samun hadin kan Nijeriya, a aikace da kuma addinance, ”in ji shi.

Da yake magana a kan kalubalen da kasa ke fuskanta a halin yanzu, Shugaba Tinubu ya bukaci ‘yan Nijeriya, da su yi watsi da labaran da za su raba kan al’umma, musamman wadanda ke nuni da cewa; ‘yan kasar ba ta da ‘yancin yin addini.

“Dole ne mu karfafa kudurinmu na samar da kasa dunkulalliya, sannan wajibi ne a tsaya tsayin daka, wajen dakile yunkurin da ake yi na bata Nijeriya a matsayin kasa da ke tauye ‘yancin addini,” in ji shi.

Ya jaddada cewa, tsaron kasa ba ya taba rabuwa da hadin kai tare da mutunta juna a tsakanin ‘yan kasa, ba tare kuma da la’akari da bambancin addini ko kabilanci ba.

“Tsaron kasarmu, yana da nasaba da hadin kanmu, hadin kanmu da mutunta bambancin addini, dole ne mu hada karfi da karfe wajen yaki da masu neman raba kanmu,” in ji shugaban.

Da yake jaddada kudirin gwamnatinsa na kare rayuka da dukiyoyi, Tinubu ya ce; ana daukar kwararan matakai na tunkarar matsalar rashin tsaro a fadin wannan kasa.

“Gwamnatina, tana yin aiki tukuru wajen kare rayuka da dukiyoyi tare kuma da aiwatar da yaki da ta’addanci ta kowane bangare,” in ji shi.

Addini
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
An Nada Liu Xianfa Wakilin Musamman Na Gwamnatin Sin Kan Harkokin Afirka

An Nada Liu Xianfa Wakilin Musamman Na Gwamnatin Sin Kan Harkokin Afirka

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.