ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Kai, Hakuri Da Riko Da Addini Su Ne Jigon Zaman Lafiyar Nijeriya – Tinubu

by Sani Anwar
5 months ago
Addini

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Shugaba Bola Tinubu ya roki ‘yan Nijeriya, da su rungumi hadin kai, koyarwar addini, hakuri da zaman lafiya a matsayin ginshikan tsaro, kwanciyar hankali da ci gaban kasa.

Shugaban ya yi wannan kira ne a jiya a wajen taron kasa da kasa karo na 4 na Cibiyar Wayewar Musulunci da Tattaunawar Addinin Musulunci da aka gudanar a Kano.

  • Za A Gudanar Da Dandalin Tattaunawa Na Masana Na Jam’iyyar JKS Da KMT A Birnin Beijing
  • Akpabio: Ba A Canza Komai A Cikin Sabbin Dokokin Haraji Ba 

Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a, Mohammed Idris ne ya wakilce shi a wajen taron.

Tinubu ya yaba wa wannan cibiya da masallacin Sultan Bello Kaduna, bisa yadda suke ci gaba da gudanar da cudanya da juna da nufin samar da zaman lafiya da hadin kan kasa.

“Wannan taro, yana ci gaba da tabbatar da manufofin zaman lafiya da hadin kan al’ummarmu, ta hanyar tattaunawa. Ko shakka babu, an girmama ni da wannan gayyata da aka yi min,” in ji shugaban.

Ya kuma bayyana yadda taron ya mayar da hankali a kan abubuwan da marigayi Sheikh Mahmud Abubakar Gummi ya bari na alhairi da kuma ilmantarwa, inda ya bayyana cewa; fitaccen malamin addinin musuluncin ya taka muhimmiyar rawa wajen samar da hadin kai a lokutan da suka taka muhimmiyar rawa a tarihin Nijeriya.

“Sheikh Gummi, ya fahimci mahadar imani da siyasa, sannan kuma ya yi aiki kafada da kafada da hukumomi, bayan samun ‘yancin kai da yakin basasa, don inganta hadin kai da zaman lafiya,” in ji shi.

Shugaban ya ci gaba da bayyana Sheikh Gummi a matsayin fitaccen malami, wanda ya kawo gyara, kuma jigo a kasa wanda tasirinsa yake da matukar yawa a fannin addini.

“Ya kasance malami, wanda ya kawo canje-canje, mai ba da shawara, kuma fitaccen marubuci.

Ya shawarci tsararrakinsa da su yi duk abin da ya, domin samun hadin kan Nijeriya, a aikace da kuma addinance, ”in ji shi.

Da yake magana a kan kalubalen da kasa ke fuskanta a halin yanzu, Shugaba Tinubu ya bukaci ‘yan Nijeriya, da su yi watsi da labaran da za su raba kan al’umma, musamman wadanda ke nuni da cewa; ‘yan kasar ba ta da ‘yancin yin addini.

“Dole ne mu karfafa kudurinmu na samar da kasa dunkulalliya, sannan wajibi ne a tsaya tsayin daka, wajen dakile yunkurin da ake yi na bata Nijeriya a matsayin kasa da ke tauye ‘yancin addini,” in ji shi.

Ya jaddada cewa, tsaron kasa ba ya taba rabuwa da hadin kai tare da mutunta juna a tsakanin ‘yan kasa, ba tare kuma da la’akari da bambancin addini ko kabilanci ba.

“Tsaron kasarmu, yana da nasaba da hadin kanmu, hadin kanmu da mutunta bambancin addini, dole ne mu hada karfi da karfe wajen yaki da masu neman raba kanmu,” in ji shugaban.

Da yake jaddada kudirin gwamnatinsa na kare rayuka da dukiyoyi, Tinubu ya ce; ana daukar kwararan matakai na tunkarar matsalar rashin tsaro a fadin wannan kasa.

“Gwamnatina, tana yin aiki tukuru wajen kare rayuka da dukiyoyi tare kuma da aiwatar da yaki da ta’addanci ta kowane bangare,” in ji shi.

Addini
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
An Nada Liu Xianfa Wakilin Musamman Na Gwamnatin Sin Kan Harkokin Afirka

An Nada Liu Xianfa Wakilin Musamman Na Gwamnatin Sin Kan Harkokin Afirka

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.