Shugaba Bola Tinubu ya roki ‘yan Nijeriya, da su rungumi hadin kai, koyarwar addini, hakuri da zaman lafiya a matsayin ginshikan tsaro, kwanciyar hankali da ci gaban kasa.
Shugaban ya yi wannan kira ne a jiya a wajen taron kasa da kasa karo na 4 na Cibiyar Wayewar Musulunci da Tattaunawar Addinin Musulunci da aka gudanar a Kano.
- Za A Gudanar Da Dandalin Tattaunawa Na Masana Na Jam’iyyar JKS Da KMT A Birnin Beijing
- Akpabio: Ba A Canza Komai A Cikin Sabbin Dokokin Haraji Ba
Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a, Mohammed Idris ne ya wakilce shi a wajen taron.
Tinubu ya yaba wa wannan cibiya da masallacin Sultan Bello Kaduna, bisa yadda suke ci gaba da gudanar da cudanya da juna da nufin samar da zaman lafiya da hadin kan kasa.
“Wannan taro, yana ci gaba da tabbatar da manufofin zaman lafiya da hadin kan al’ummarmu, ta hanyar tattaunawa. Ko shakka babu, an girmama ni da wannan gayyata da aka yi min,” in ji shugaban.
Ya kuma bayyana yadda taron ya mayar da hankali a kan abubuwan da marigayi Sheikh Mahmud Abubakar Gummi ya bari na alhairi da kuma ilmantarwa, inda ya bayyana cewa; fitaccen malamin addinin musuluncin ya taka muhimmiyar rawa wajen samar da hadin kai a lokutan da suka taka muhimmiyar rawa a tarihin Nijeriya.
“Sheikh Gummi, ya fahimci mahadar imani da siyasa, sannan kuma ya yi aiki kafada da kafada da hukumomi, bayan samun ‘yancin kai da yakin basasa, don inganta hadin kai da zaman lafiya,” in ji shi.
Shugaban ya ci gaba da bayyana Sheikh Gummi a matsayin fitaccen malami, wanda ya kawo gyara, kuma jigo a kasa wanda tasirinsa yake da matukar yawa a fannin addini.
“Ya kasance malami, wanda ya kawo canje-canje, mai ba da shawara, kuma fitaccen marubuci.
Ya shawarci tsararrakinsa da su yi duk abin da ya, domin samun hadin kan Nijeriya, a aikace da kuma addinance, ”in ji shi.
Da yake magana a kan kalubalen da kasa ke fuskanta a halin yanzu, Shugaba Tinubu ya bukaci ‘yan Nijeriya, da su yi watsi da labaran da za su raba kan al’umma, musamman wadanda ke nuni da cewa; ‘yan kasar ba ta da ‘yancin yin addini.
“Dole ne mu karfafa kudurinmu na samar da kasa dunkulalliya, sannan wajibi ne a tsaya tsayin daka, wajen dakile yunkurin da ake yi na bata Nijeriya a matsayin kasa da ke tauye ‘yancin addini,” in ji shi.
Ya jaddada cewa, tsaron kasa ba ya taba rabuwa da hadin kai tare da mutunta juna a tsakanin ‘yan kasa, ba tare kuma da la’akari da bambancin addini ko kabilanci ba.
“Tsaron kasarmu, yana da nasaba da hadin kanmu, hadin kanmu da mutunta bambancin addini, dole ne mu hada karfi da karfe wajen yaki da masu neman raba kanmu,” in ji shugaban.
Da yake jaddada kudirin gwamnatinsa na kare rayuka da dukiyoyi, Tinubu ya ce; ana daukar kwararan matakai na tunkarar matsalar rashin tsaro a fadin wannan kasa.
“Gwamnatina, tana yin aiki tukuru wajen kare rayuka da dukiyoyi tare kuma da aiwatar da yaki da ta’addanci ta kowane bangare,” in ji shi.















Discussion about this post