ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Ana Yin Allah-wadai Da Cin Amanar Da Aka Yi Wa Kwankwaso – Hon. MB Aliyu

by Sani Anwar
3 months ago
Kwankwaso

A wannan mako da muke ciki ne, wakilinmu SANI ANWAR, ya zanta da Ɗan Majalisar Jihar Kano, mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Nassarawa, Injiniya Yusuf Bello Aliyu, wanda tattaunawar tasu ta ƙunshi batutuwa da dama, ciki har da batun zarge-zargen da suke yi wa gwamnan Jihar Kano, na cin amanar jagoransu na Kwankwasiyya da sauran wasu batutuwa da dama da suka shafi siyasar Kano da ma ƙasa baki-ɗaya. Ga dai yadda hirar ta kasance:

Ko za ka gabatarwa da masu karatu kanka?

Sunana Hon. Injiniya Yusuf Bello Aliyu, ɗan majalisa mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Nassarawa, a zauren majalisa ta goma a Jihar Kano.

ADVERTISEMENT

Kwankwaso

Za mu so ka ɗan tsakuro mana kaɗan daga cikin gwagwarmayar siyasarka, sannan wane ne jagoranka na siyasa?

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

  • Binciken CGTN: Yaki Ya Mayar Da Amurka Saniyar Ware Fiye Da Kowane Lokaci
  • Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Alhamdu lillahi, muna gode wa Allah SWT, mai yin yadda ya so a lokacin da ya so. Tun muna jami’a muka fara gwagwarmayar siyasa, ba zan manta ba, muna jami’ar Wudil, na fara riƙe muƙamin ‘Social Director na Ciɓil Engineering’, daga bisani kuma na zama ‘Welfare Officer na Nigerian Uniɓersity of Engineering Student’, daga nan kuma na yi Sanata har sau biyu a ƙungiyar NAKSS (Kano State Sutudents Association), na kuma riƙe muƙamin ‘Speaker’ sau biyu a lokacin da ina aji huɗu a jami’ar.

A lokacin da ina aji huɗun dai a jami’a, akwai ƙungiya ta Kwankwasiyya a mazaɓata ta Gama da na tsunduma, muke kuma ba da gudunmawa a ƙungiyance. Bayan na kammala jami’a, sai na ɗora daga inda muka tsaya, wato wannan tsari na Kwankwasiyya da har gobe muke ciki.

A matsayina na Injina, a lokacin da nake aiki da kamfanonin gine-gine, akwai manya-manyan ayyuka da muka yi, lokacin da mai girma Dakta Rabi’u Musa Kwankwaso yana gwamna. Mu ne muka gina jami’ar North West da sauran wasu manya-manya ayyuka, ina yin wannan aiki, ina kuma yin siyasa. Daga nan ne, sai na kafa wata ƙungiya na sa mata suna ‘MB Foundation’, a ƙarƙashin gidauniyar ne muke bai wa matasa aikin yi tare da bayar da tallafi, musamman ga waɗanda ba su da abin yi kwata-kwata.

Wannan dalili ne ya haska mana buƙatar shiga gwamnati, ta hanyar yin takara, duk da cewa; a lokacin ban ma san wace takara ya kamata na yi ba, kwamitin da muke zama da su a wannan ƙungiya ne suka ce lallai sai na yi takarar ɗan majalisar tarayya. Bayan nan ne, muka sake fitowa muka kafa wata ƙungiyar mai suna ‘Kwankwasiyya Youth Mobilization’, wadda har yanzu tana nan da ita muke yin aiki a ko’ina, tun daga matakin jiha, ƙaramar hukuma da kuma mazaɓa.

Bayan mun shiga jam’iyyar NNPP ne, Allah ya ba mu nasara, duk da ba mu samu takarar majalisar tarayya ba, sai muka samu ta majalisar jiha, inda muka samu nasarar cin zaɓe da ƙuri’u masu gagarumin rinjaye. Domin kuwa, a duk Kano, babu ɗan majalisar da ya samu yawan ƙuri’un da na samu da suka kai kimanin sama da 50,000, wanda yake biye min, ratata da shi ta ƙuri’a ta kai kimanin 25,000, shi yasa ko kutu ma bai kai ƙara ba, saboda zaɓe ne na kece raini.

Haka zalika, ba ni da wani jagora ko mudubi da muke kallo, tamkar Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso, dukkannin nasarorin da muka samu, albarkacinsa muka ci, domin shi ne ya ba mu takara, ya yi gwagwarmayar tallata mu har muka samu gwamnati. Shi yasa na sha faɗa cewa, ko yanzu ya umarce ni da kada na fito takara, to wallahi zan haƙura ba zan fito ba.

Kwankwaso
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

MASU ALAKA

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano
Labarai

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci
Labarai

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Labarai

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Next Post
Har Yanzu Ana Yin Allah-wadai Da Cin Amanar Da Aka Yi Wa Kwankwaso – Hon. MB Aliyu

Har Yanzu Ana Yin Allah-wadai Da Cin Amanar Da Aka Yi Wa Kwankwaso – Hon. MB Aliyu

LABARAI MASU NASABA

Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.