Umarnin shugaban ƙasa na janye jami’an ƴansanda da aka ɗora wa mutane masu muhimmanci na musamman (ƁIPs) waɗanda ba su da izini, yana fuskantar aiwatarwa iri-iri a jihohi daban-daban. Binciken da LEADERSHIP Sunday ta gudanar ya nuna cewa ƴan siyasa da dama, ƴan kasuwa da sauran manyan mutane har yanzu suna tafiya tare da rakiyar ƴansanda duk da wannan umarni.
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarnin ne a ranar 23 ga Nuwamba, 2025, yayin wani babban taron tsaro da aka gudanar a Abuja.
Ya ce ya kamata a janye jami’an ƴansanda da aka ɗora wa aikin gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya, sannan a mayar da su aikin tsaron al’umma na yau da kullum.
Shugaban ƙasar ya kuma bayyana cewa ƁIPs da ke buƙatar rakiyar jami’an tsaro ya kamata su nemi jami’an ɗauke da makamai daga Hukumar Tsaron Farar Hula, Gyaran Hali, Kashe Gobara da Sabis na Kurkuku ta Nijeriya (NSCDC).
Umarnin, wanda Rundunar Ƴansandan Nijeriya (NPF) ta ƙarfafa ta hanyar umarnin aiki, ya buƙaci a gaggauta janye jami’an ƴansanda daga rakiyar ƁIPs waɗanda ba su da izini. Haka kuma, an bayar da umarnin kama jami’an ƴansanda da aka samu suna yin aikin rakiyar ƁIPs ba bisa ƙa’ida ba.
Domin tabbatar da bin wannan umarni, Sufeto-Janar na Ƴansanda (IGP) ya umurci kwamandojin tsaron filayen jiragen sama na Abuja da Legas da su kama duk wani jami’in ɗansanda da aka gani yana rakiyar ƁIP da ba shi da izini.
Sai dai, binciken LEADERSHIP Sunday a wasu jihohi ya nuna cewa duk da cewa ana aiwatar da umarnin a ƙa’ida, aiwatar da shi a aikace ba ya tafiya daidai a ko’ina. An bayyana matsalolin tsaro da kuma wasu keɓantattun izini a matsayin dalilan da suka sa har yanzu ake ci gaba da amfani da rakiyar ƴansanda.
Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar Ƴansandan (PPRO), Henry Okoye, ya ce:
“Mun janye sama da kashi 60 cikin 100 na jami’an ƴansanda da aka ɗora wa ƴan siyasa, ƴan kasuwa da sarakunan gargajiya waɗanda ba su cancanci samun wannan kariya ba. Sai dai gwamna, mataimakin gwamna, kakakin majalisa, babban jojin jihar da sarakunan gargajiya masu daraja ta farko waɗanda ke fuskantar barazanar tsaro ne kawai suka ci gaba da samun kariyar da doka ta tanada.”














