ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harin Ƴan Bindiga A Zamfara: Gwamna Lawal Ya Jagoranci Taron Gaggawa Kan Tsaro

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jajanta wa al’ummomi da iyalan waɗanda hare-haren ’yan bindiga suka shafa a sassa daban-daban na jihar, yana mai tabbatar da ƙudurin gwamnatinsa na kawo ƙarshen matsalar tsaro da ta daɗe tana addabar yankin.

Gwamnan Lawal ya kira tare da jagorantar wani taron gaggawa na Majalisar Tsaron Jihar a ɗakin taro na Gidan Gwamnati da ke Gusau.

  • Kiwon Awakan Alfarma Na Ƙara Haɓaka A Jihar Kano
  • Rigakafin Cutar Shanyewar Barin Jiki

Taron ya haɗa shugabannin hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki domin duba halin da ake ciki da kuma ɗaukar matakan gaggawa.

ADVERTISEMENT

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, an bayyana cewa kiran taron ya biyo bayan rahotanni masu tayar da hankali, musamman sahihan bayanai kan zargin dasa bama-bamai na na’urorin fashewa (IED) a kan wasu manyan hanyoyin jihar.

Sanarwar ta ce, gwamnan ya umarci shugabannin hukumomin tsaro da su sake nazari kan tsarin tsaron da ake da shi a halin yanzu, tare da samar da ingantaccen tsari na aiki mai ma’ana, tsari da haɗin gwiwa domin daƙile wannan sabon salo na barazana.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

“Taron ya nuna haɗin kai da ɗaukar alhakin bai ɗaya tsakanin gwamnatin jihar da hukumomin tsaro wajen kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Zamfara,” in ji sanarwar.

Gwamna Lawal ya buƙaci hukumomin tsaro da su ƙara ƙaimi wajen tattara bayanan sirri, ƙara sanya ido da ɗaukar matakan haɗin gwiwa cikin gaggawa domin hana miyagun mutane ƙara samun galaba.

Ya jaddada muhimmancin kasancewa a gaba da masu aikata laifi, tare da taƙaita musu damar motsi da murƙushe duk wata barazana ba tare da jinkiri ba.

Bugu da ƙari, gwamnan ya miƙa saƙon ta’aziyya ga hukumomin tsaro bisa rasuwar jami’ansu da suka sadaukar da rayukansu wajen kare al’umma, tare da yi wa waɗanda suka jikkata fatan samun sauƙi cikin gaggawa.

Haka kuma, ya jajanta wa iyalan waɗanda suka rasa rayukansu da al’ummomin da hare-haren suka shafa, yana mai tabbatar da cewa gwamnati za ta ba da cikakken goyon baya na kayan aiki, dabaru da tsari domin ƙara ƙarfin hukumomin tsaro.

Gwamnatin Zamfara ta jaddada cewa za ta ci gaba da saukar dukkan matakan da suka dace domin dawo da zaman lafiya mai ɗorewa a faɗin jihar, tare da tabbatar da cewa tsaro ya zama ginshiƙin ci gaban al’umma.

Zamfara
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Katsina

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.