ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kiwon Awakan Alfarma Na Ƙara Haɓaka A Jihar Kano

by Abubakar Abba
3 months ago
Kiwo

Kiwon Awakai na cikin gida, musamman a Jihar Kano ya fara fusknatar ƙalubale, musamman saboda yadda wasu a ƙauyukan jihar, suka fara raja’a wajen fara kiwon wasu nau’ikan Awaki da aka fi sani da na alfarama.

Kusan za a iya cewa, a ɗaukacin wasu ƙauyukan da ke jihar ta Kano, kiwon Shanu na ɗaya daga cikin fannin da ya yi fice a jihar, duba da cewa; ana samun kuɗaɗen shiga da samar da wadataccen abinci da kuma inganta rayuwar masu kiwonsu.

  • Bukukuwan Ƙarshen Shekara: NSCDC Ta Tura Jami’anta 4,000 Don Tsaro A FCT
  • Abubuwan Da Ya Kamata A Lura Da Su Kafin Fara Kiwon Agwagwa (Geese)

Sai dai, a yanzu fannin kiwon Akuyoyin na alfarama a ƙauyukan jihar, za a iya cewa; ya shiga gaban kiwon na Shanu, musamman duba da cewa; wasu nau’ikan Akuyoyin da ake shigowa da su cikin ƙasar, wasu masu kiwon, sun mayar da hankali wajen kiwata su, musamman domin su sama wa kansu kuɗaɗen shiga masu yawa.

ADVERTISEMENT

An shafe shekaru ana kiwon Akuyoyi a ƙasar nan, waɗanda akasari ana kiwata su ne, domin cin namansu a gida.

Amma sai dai a yau, akwai wasu nau’ikan na Akuyoyi na daban da aka fi mayar da hankali wajen kiwata su, musamman kamar irin nau’ikan Saanen, Damascus da kuma Gulabi waɗanda kuma sun rungumi kiwonsu ne, domin samar da kuɗaɗen shiga.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

Akasarin waɗannan nau’ikan na Akuyoyi, masu kuɗi ne suka fi sayen su, domin kiwata su da kuma wasu masu sha’awar yin kiwo.

Ɗaya daga cikin masu kiwata irin waɗannan Akuyoyi, wanda kuma ya kasance ɗaya a kan gaba wajen rungumar kiwata su, mai suna Malam Sunusi Ali Musa, da ke Jihar Kano ya bayyana cewa; kwatsam ya tsinci kansa a cikin sana’ar fara kiwata wannan nau’i na Akuyoyi.

“Mun fara kiwata su ne, a bisa sha’awa kawai, daga baya sai muka lura jama’a sun fara nuna ra’ayinsu na kiwata su, inda ya ƙara da cewa; irin waɗannan Akuyoyin na alfarma, ana kiwata su ne domin kasuwanci a babban mataki” in ji shi.

A cewarsa, ya fara zuba jarin da a kiwata nau’in Saanen, a waɗanda ana shigo da su ne daga Gabas ta Tsakiya, kuma ana samun nono a jikinsu mai yawan gaske.

Ya ƙara da cewa, wasu na sayen nononsu, domin sarrafa shi zuwa magunguna, inda kuma wasu ke kiwata irin waɗannan Akuyoyi domin ado a gida.

Shi ma wani wanda ya rungumi irin wannan kiwo, mai suna Malam Isma’ila Ahmad, a yanzu nau’in Akuyar na Damascus, shi ne ya fi yin tashe kuma suna samar da ingantaccen nama.

Kazalika, Ahmad ya kuma bayyana wani nau’in Akuwar wanda ake kira da Gulabi, kuma akasarinsu farare ne da aka shigo da su daga ƙasar Pakistan.

Samun irin waɗannan nau’ikan na Akuya, ba abu ne mai sauƙi ba, kuma akasarinsu ana safarar su ne daga ƙasashe kamar irin su Libiya da Jamhuriyar Nijar.

An ruwaito cewa, nau’in Akuya na Damascus ana sayar da su ne a kan naira miliyan 3.5, inda kuma nau’in Gulabi ake sayar da su a kan naira miliyan 3 .

Wasu daga cikin masu sana’ar, Alhaji Usman Baba Gara, ya bayyana cewa; kiwon irin waɗannan Akuyoyin a Jihar Kano, na ƙara tumbatsa, musamman ganin cewa, ana samun riba mai yawa, wanda hakan ya sanya ake ƙara samun wasu masu son shiga fannin kiwon nasu.

Sai dai, ya yi gargaɗin cewa; dole ne ga duk mai son kiwata su ya tabbatar da yana bin ƙa’aida, musamman domin kare su daga kamuwa da cututtuka daban-daban.

Bugu da ƙari, su ma wasu ƙwararrun likitocin dabbobi a jihar, sun tabbatar da hakan, inda suka sanar da cewa; irin waɗannan Akuyoyin na alfarma, suna buƙatar son kulawa matuƙa da gaske.

Kiwo
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

MASU ALAKA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
Noma Da Kiwo

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

June 12, 2026
Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
Noma Da Kiwo

Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT

June 6, 2026
Next Post
Yaƙin Iran: Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Matakan Tsaro A Yankin Gabas

Babu Tabbacin Za Mu Iya Gudanar Da Sahihin Zaɓe A 2027 —Shugaban INEC

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.