ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kiwon Awakan Alfarma Na Ƙara Haɓaka A Jihar Kano

by Abubakar Abba
4 months ago
Kiwo

Kiwon Awakai na cikin gida, musamman a Jihar Kano ya fara fusknatar ƙalubale, musamman saboda yadda wasu a ƙauyukan jihar, suka fara raja’a wajen fara kiwon wasu nau’ikan Awaki da aka fi sani da na alfarama.

Kusan za a iya cewa, a ɗaukacin wasu ƙauyukan da ke jihar ta Kano, kiwon Shanu na ɗaya daga cikin fannin da ya yi fice a jihar, duba da cewa; ana samun kuɗaɗen shiga da samar da wadataccen abinci da kuma inganta rayuwar masu kiwonsu.

  • Bukukuwan Ƙarshen Shekara: NSCDC Ta Tura Jami’anta 4,000 Don Tsaro A FCT
  • Abubuwan Da Ya Kamata A Lura Da Su Kafin Fara Kiwon Agwagwa (Geese)

Sai dai, a yanzu fannin kiwon Akuyoyin na alfarama a ƙauyukan jihar, za a iya cewa; ya shiga gaban kiwon na Shanu, musamman duba da cewa; wasu nau’ikan Akuyoyin da ake shigowa da su cikin ƙasar, wasu masu kiwon, sun mayar da hankali wajen kiwata su, musamman domin su sama wa kansu kuɗaɗen shiga masu yawa.

ADVERTISEMENT

An shafe shekaru ana kiwon Akuyoyi a ƙasar nan, waɗanda akasari ana kiwata su ne, domin cin namansu a gida.

Amma sai dai a yau, akwai wasu nau’ikan na Akuyoyi na daban da aka fi mayar da hankali wajen kiwata su, musamman kamar irin nau’ikan Saanen, Damascus da kuma Gulabi waɗanda kuma sun rungumi kiwonsu ne, domin samar da kuɗaɗen shiga.

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

Akasarin waɗannan nau’ikan na Akuyoyi, masu kuɗi ne suka fi sayen su, domin kiwata su da kuma wasu masu sha’awar yin kiwo.

Ɗaya daga cikin masu kiwata irin waɗannan Akuyoyi, wanda kuma ya kasance ɗaya a kan gaba wajen rungumar kiwata su, mai suna Malam Sunusi Ali Musa, da ke Jihar Kano ya bayyana cewa; kwatsam ya tsinci kansa a cikin sana’ar fara kiwata wannan nau’i na Akuyoyi.

“Mun fara kiwata su ne, a bisa sha’awa kawai, daga baya sai muka lura jama’a sun fara nuna ra’ayinsu na kiwata su, inda ya ƙara da cewa; irin waɗannan Akuyoyin na alfarma, ana kiwata su ne domin kasuwanci a babban mataki” in ji shi.

A cewarsa, ya fara zuba jarin da a kiwata nau’in Saanen, a waɗanda ana shigo da su ne daga Gabas ta Tsakiya, kuma ana samun nono a jikinsu mai yawan gaske.

Ya ƙara da cewa, wasu na sayen nononsu, domin sarrafa shi zuwa magunguna, inda kuma wasu ke kiwata irin waɗannan Akuyoyi domin ado a gida.

Shi ma wani wanda ya rungumi irin wannan kiwo, mai suna Malam Isma’ila Ahmad, a yanzu nau’in Akuyar na Damascus, shi ne ya fi yin tashe kuma suna samar da ingantaccen nama.

Kazalika, Ahmad ya kuma bayyana wani nau’in Akuwar wanda ake kira da Gulabi, kuma akasarinsu farare ne da aka shigo da su daga ƙasar Pakistan.

Samun irin waɗannan nau’ikan na Akuya, ba abu ne mai sauƙi ba, kuma akasarinsu ana safarar su ne daga ƙasashe kamar irin su Libiya da Jamhuriyar Nijar.

An ruwaito cewa, nau’in Akuya na Damascus ana sayar da su ne a kan naira miliyan 3.5, inda kuma nau’in Gulabi ake sayar da su a kan naira miliyan 3 .

Wasu daga cikin masu sana’ar, Alhaji Usman Baba Gara, ya bayyana cewa; kiwon irin waɗannan Akuyoyin a Jihar Kano, na ƙara tumbatsa, musamman ganin cewa, ana samun riba mai yawa, wanda hakan ya sanya ake ƙara samun wasu masu son shiga fannin kiwon nasu.

Sai dai, ya yi gargaɗin cewa; dole ne ga duk mai son kiwata su ya tabbatar da yana bin ƙa’aida, musamman domin kare su daga kamuwa da cututtuka daban-daban.

Bugu da ƙari, su ma wasu ƙwararrun likitocin dabbobi a jihar, sun tabbatar da hakan, inda suka sanar da cewa; irin waɗannan Akuyoyin na alfarma, suna buƙatar son kulawa matuƙa da gaske.

Kiwo
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Matatar Ɗangote Ta Ƙaryata Iƙirarin Dillalan Man Fetur 

MASU ALAKA

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 
Noma Da Kiwo

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
Next Post
Yaƙin Iran: Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Matakan Tsaro A Yankin Gabas

Babu Tabbacin Za Mu Iya Gudanar Da Sahihin Zaɓe A 2027 —Shugaban INEC

LABARAI MASU NASABA

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

July 8, 2026
Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

July 8, 2026
Dole Ne Mace Ta Gaya Wa Mijinta Gaskiya Domin Ranar Hisabi – Matar Gwamnan Jigawa

Gwamnatin Jigawa Ta Ɗaga Mafi Ƙarancin Fansho Zuwa Naira 20,000

July 8, 2026
Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.