ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kiwon Awakan Alfarma Na Ƙara Haɓaka A Jihar Kano

by Abubakar Abba
6 months ago
Kiwo

Kiwon Awakai na cikin gida, musamman a Jihar Kano ya fara fusknatar ƙalubale, musamman saboda yadda wasu a ƙauyukan jihar, suka fara raja’a wajen fara kiwon wasu nau’ikan Awaki da aka fi sani da na alfarama.

Kusan za a iya cewa, a ɗaukacin wasu ƙauyukan da ke jihar ta Kano, kiwon Shanu na ɗaya daga cikin fannin da ya yi fice a jihar, duba da cewa; ana samun kuɗaɗen shiga da samar da wadataccen abinci da kuma inganta rayuwar masu kiwonsu.

  • Bukukuwan Ƙarshen Shekara: NSCDC Ta Tura Jami’anta 4,000 Don Tsaro A FCT
  • Abubuwan Da Ya Kamata A Lura Da Su Kafin Fara Kiwon Agwagwa (Geese)

Sai dai, a yanzu fannin kiwon Akuyoyin na alfarama a ƙauyukan jihar, za a iya cewa; ya shiga gaban kiwon na Shanu, musamman duba da cewa; wasu nau’ikan Akuyoyin da ake shigowa da su cikin ƙasar, wasu masu kiwon, sun mayar da hankali wajen kiwata su, musamman domin su sama wa kansu kuɗaɗen shiga masu yawa.

ADVERTISEMENT

An shafe shekaru ana kiwon Akuyoyi a ƙasar nan, waɗanda akasari ana kiwata su ne, domin cin namansu a gida.

Amma sai dai a yau, akwai wasu nau’ikan na Akuyoyi na daban da aka fi mayar da hankali wajen kiwata su, musamman kamar irin nau’ikan Saanen, Damascus da kuma Gulabi waɗanda kuma sun rungumi kiwonsu ne, domin samar da kuɗaɗen shiga.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Akasarin waɗannan nau’ikan na Akuyoyi, masu kuɗi ne suka fi sayen su, domin kiwata su da kuma wasu masu sha’awar yin kiwo.

Ɗaya daga cikin masu kiwata irin waɗannan Akuyoyi, wanda kuma ya kasance ɗaya a kan gaba wajen rungumar kiwata su, mai suna Malam Sunusi Ali Musa, da ke Jihar Kano ya bayyana cewa; kwatsam ya tsinci kansa a cikin sana’ar fara kiwata wannan nau’i na Akuyoyi.

“Mun fara kiwata su ne, a bisa sha’awa kawai, daga baya sai muka lura jama’a sun fara nuna ra’ayinsu na kiwata su, inda ya ƙara da cewa; irin waɗannan Akuyoyin na alfarma, ana kiwata su ne domin kasuwanci a babban mataki” in ji shi.

A cewarsa, ya fara zuba jarin da a kiwata nau’in Saanen, a waɗanda ana shigo da su ne daga Gabas ta Tsakiya, kuma ana samun nono a jikinsu mai yawan gaske.

Ya ƙara da cewa, wasu na sayen nononsu, domin sarrafa shi zuwa magunguna, inda kuma wasu ke kiwata irin waɗannan Akuyoyi domin ado a gida.

Shi ma wani wanda ya rungumi irin wannan kiwo, mai suna Malam Isma’ila Ahmad, a yanzu nau’in Akuyar na Damascus, shi ne ya fi yin tashe kuma suna samar da ingantaccen nama.

Kazalika, Ahmad ya kuma bayyana wani nau’in Akuwar wanda ake kira da Gulabi, kuma akasarinsu farare ne da aka shigo da su daga ƙasar Pakistan.

Samun irin waɗannan nau’ikan na Akuya, ba abu ne mai sauƙi ba, kuma akasarinsu ana safarar su ne daga ƙasashe kamar irin su Libiya da Jamhuriyar Nijar.

An ruwaito cewa, nau’in Akuya na Damascus ana sayar da su ne a kan naira miliyan 3.5, inda kuma nau’in Gulabi ake sayar da su a kan naira miliyan 3 .

Wasu daga cikin masu sana’ar, Alhaji Usman Baba Gara, ya bayyana cewa; kiwon irin waɗannan Akuyoyin a Jihar Kano, na ƙara tumbatsa, musamman ganin cewa, ana samun riba mai yawa, wanda hakan ya sanya ake ƙara samun wasu masu son shiga fannin kiwon nasu.

Sai dai, ya yi gargaɗin cewa; dole ne ga duk mai son kiwata su ya tabbatar da yana bin ƙa’aida, musamman domin kare su daga kamuwa da cututtuka daban-daban.

Bugu da ƙari, su ma wasu ƙwararrun likitocin dabbobi a jihar, sun tabbatar da hakan, inda suka sanar da cewa; irin waɗannan Akuyoyin na alfarma, suna buƙatar son kulawa matuƙa da gaske.

Kiwo
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Yaƙin Iran: Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Matakan Tsaro A Yankin Gabas

Babu Tabbacin Za Mu Iya Gudanar Da Sahihin Zaɓe A 2027 —Shugaban INEC

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.