Hukumar Kula da Samar da Abinci da Aikin Noma ta Majalisar Dinkin Duniya (FAO), ta gabatar da shirin samar da daukin horar da masu kiwon kifin tarwada a Jihar Gwambe.
Ta samar da daukin ne, a karkashin shirin ACP, domin masu kiwon su kara habaka kiwon na tarwada a Gwambe, musamman domin rage yawan mutuwar tarwada a jihar da kara samar wa da masu kiwon dabarun kula da su, tare da kara samar musu da kudaden shiga.
An wanzar da wannan shiri ne, bisa hadaka da Ma’aikatar Albarkatun Ruwa, Kare Muhalli da Kula da Gandun Daji ta jihar.
Masu kiwon da suka amfana, sun fito ne daga yankin Waziri da kuma sauran wasu yankunan da ke Gwambe.
Mayowa Ajayi, mai bayar da horo a jawabinsa a wajen bayar da horon a Waziri daura da titin Kalshingi ya ce; an samar da tsarin ne, don samar da ilimin da dabarun zamani ga masu kiwon, musamman domin kaucewa yin asara da kuma kara bunkasa kiwonsu.
Ita kuwa a nata jawabin, Echezona Cynthia Ijeoma cewa ta yi, a baya mutuwar tarwada ta kai daga tsakanin kashi 40 zuwa 50, inda ta ce; amma matsalar ta ragu da kashi 10, musamman saboda samar da wannan shiri na ACF, wanda ya kasance ana gudanar da shi ne, wajen horar da masu kiwon dabarun yin kiwon zamani.
Ijeoma ta kuma yi nuni da cewa, yawan ciyar da tarwada abinci da wasu masu kiwon ke yi, na daga cikin manyan kalubale, kafin a samar da wannan dauki.
Shi kuwa, Fetrus Philip, wanda ya wakilci Daraktan Kula da Sashen Kiwon Kfi a Ma’aikatar, ya danganta wannan hadakar a matsayin mai matukar muhimmanci.
Daya daga cikin masu kiwon, wanda ya amfana da horon Ogochukwu Sunday, ya ce; shirin ya taimaka wa sana’arsa ta kiwon.
Sunday ya kuma bukaci matasa da su rungumi yin kiwon kifin, domin sama wa kansu kudaden shiga.















Discussion about this post