Shugaban Hukumar Gwamnatin Tarayya da ke da alhakin kafawa, lasisi, duba, da kuma tsara duk wani tsari na Shiyyoyin Kasuwanci na Musamman wato NEPZA, na shiyar garin Kalaba, Dakta Olufemi Ogunyemi, ci gaba da ba su goyon bayanta.
Ogunyemi ya sanar da haka ne, yayin ganawar da yayi, da masu zuba jari da wasu hukumimin gwamnati, a garin Kalaba.
Ya bayyana ƙudurin NEPZA, na samar da kyakyawan yanayin, ci gaba da gudanar da hada-hadar kasuwanci a shiyyar Hukumar, ta garin Kalaba.
“Nuyin da ke a kan Hukumar shi ne, na ci gaba da sanya ido, a shiyoyin da ake gudanar da hada-hadar kasuwanci, haka kuma akwai nauyin kan Hukumar, na taimaka wa, masu zuba jari, a fannin, domin su samu nasara.
“Na saurarin abinda kuke da damuwa akai na kuma fahimci ƙalubalen da ku ke fuskanta, muna kuma kan aiki, domin lalubo da mafita, a kansu,” Inji Shugaban.
Shugaban ya ƙara da cewa, shiyyar ta Kalaba, ta kasance ta farko, daga cikin sauran shiyyoyin Hukumar da ke a ƙasar, musamman, a bangaren masana’antu da ɗaga darajar, fitar da kaya, zuwa ƙetare.
A cewarsa, masu zuba jari da dama, na nuna damuwarsu, kan gibin da ake da shi, n rashin samar da kayan aiki, da batun sauyin yanayi, wanda hakan, ke zame masu, ƙalubalen gudanar da kasuwancinsu.
Ya ci gaba da cewa, wasu daga cikin buƙatun masu zuba jarin, sun haɗa da; sanya Fitilolin haskaka hanyoyi a shiyyar ta Kalaba, saboda ƙalubalen rashin tsaro.















Discussion about this post