Yayin da ‘yan bindiga suka sace fasinjoji 20 a kan hanyar Wawa–Luma da ke Karamar Hukumar Borgu a Jihar Neja, gwamnan Jihar Kwara kuma shugaban Kungiyar Gwamnaonin Nijeriya (NGF), Abdulrahman Abdulrazak, ya kai ziyara jihar domin hada kai da takwaransa wAajen dakile hare-haren ‘yan bindiga a kauyukan jihohin biyu.
Baya ga mutum 27 da aka kashe a Konkonso, Pissa da Tunga-Makeri a karshen mako, ‘yan bindigar sun kuma sace fasinjoji 20 a jiya a kan hanyar Wawa–Luma, inda aka tare su a cikin motocin Sharon guda biyu da kuma Golf guda biyu.
Jaridar LEADERSHIP ta rawaito cewa lamarin ya faru ne da safiyar jiya, inda aka tafi da fasinjojin zuwa cikin dajin Tafkin Ka’inji.
Wani shaidar gani da ido ya ce, “’Yan bindigar na aiki babu tangarda, suna kwashe mutanenmu kamar dabbobi zuwa cikin daji.”
A halin da ake ciki, gwamnan Jihar Kwara ya kai ziyarar jaje ga gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, kan sabbin hare-haren ta’addanci da aka kai a wasu al’ummomi da ke karkashin Masarautar Borgu a Jihar Neja, inda ya bayyana hare-haren a matsayin abin takaici da tada hankali.
A nasa Bangaren, Gwamna Bago ya gode wa takwaransa na Kwara bisa wannan ziyara, yana mai cewa abin farin ciki ne kuma alamar hadin kai, musamman ganin cewa jihohin biyu na da iyaka a yankin Masarautar Borgu kuma dukkansu na fuskantar kalubalen tsaro iri daya.















Discussion about this post