ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Imanin Sin Kan Ci Gaban Tattalin Arzikinta Zai Haifar Da Tasiri Mai Kyau

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Tattalin arziki

Yanzu haka, wasu kafofin yada labaru na kasashen yamma sun saba da yada labarin wai “Tattalin arzikin Sin na tafiyar hawainiya, abun da zai haifar da illa ga tattalin arzikin kasashen Afirka.” Ko haka batun ya ke?

 

A wajen wani taron manema labaru da wasu hukumomin Sin suka kira a birnin Beijing a yau, wani wakilin kamfanin Reuters mai dillancin labarai na kasar Birtaniya ya yi tambaya cewa, shin kasar Sin za ta iya cimma burinta na samun karuwar tattalin arziki da ta kai kimanin kashi 5% a bana? Daga baya, wani jami’i mai kula da tsare-tsaren tattalin arziki na kasar Sin ya amsa cewa, “Muna da sharadi, da kwarewar da ake bukata, gami da cikakken imani kan cewar za mu cimma burin da muka sanya a gaba, na raya tattalin arziki.”

ADVERTISEMENT
  • Fu Cong: Kasar Sin Tana Goyon Bayan MDD Don Kara Himma Da Inganci
  • Sin Za Ta Dauki Jerin Matakai Don Ingiza Bunkasuwar Tattalin Arzikinta

To, me ya sa kasar Sin samun cikakken imani kan bunkasuwar tattalin arzikinta?

 

LABARAI MASU NASABA

Aminu Bayero Ya Samu Nakasu Ta Ɓangaren Siyasa

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

Dalili na farko shi ne, yanayi mai kyau na tattalin arzikinta cikin watannin da suka gabata. An ce, saurin karuwar tattalin arzikin kasar a watanni 6 na farko na bana ya kai kashi 5%, kana yanayin samar da guraben aikin yi, da na farashin kayayyaki, dukkansu na da karko.

 

Kana dalili na biyu, shi ne dimbin matakan da gwamnatin kasar ta dauka don sa kaimi ga karuwar tattalin arziki. Misali, samar da alfanu ga al’umma don habaka bukatun da ake samu cikin kasuwannin gidan kasar, da taimakawa kamfanonin da suka fada cikin mawuyacin hali, da neman farfado da kasuwar sayen gidaje, da inganta yanayin kasuwar hannayen jari, da dai sauransu. Bisa yadda aka samu dimbin zirga-zirgar masu yawon shakatawa a kasar Sin, da kyautatuwar yanayin kasuwar gidaje a Beijing da sauran birane daban daban, da hauhawar farashin hannayen jari, a kwanakin baya, za a iya ganin kyakkyawan tasirin matakan da aka dauka a kasar.

 

Sa’an nan ko imanin kasar Sin kan yanayin tattalin arzikinta zai yi wani tasiri kan kasashen Afirka, da sauran kasashe masu tasowa? A ganina, wannan imani zai haifar da kyakkyawan tasiri da hasashe mai yakini kan karuwar tattalin arzikin kasashe daban daban. Sa’an nan, za a iya tabbatar da gaskiyar maganar, ta hanyar duba wasu alkaluma masu alaka da kasar Sin:

 

A fannin samar da gudunmowa ga tattalin arzikin duniya, tun daga shekarar 1979 zuwa ta 2023, kasar Sin ta samar da gudunmowar kashi 24.8% na karuwar tattalin arzikin duniya, wadda ta kai matsayin koli a duniya.

 

Kana a fannin zuba jari ga kasashen waje, yawan jarin da kasar Sin ta zuba wa kasashen ketare da ba na fannin hada-hadar kudi ba, ya kai dalar Amurka biliyan 130.1, a shekarar 2023, jimillar da ta ninka ta shekarar 2003 sau 61, tare da kiyaye wata matsakaiciyar karuwa ta kashi 23% a duk shekara. Ban da haka, ya zuwa karshen shekarar 2023, adadin kudin da kasar Sin ta zuba wa kasashen Afirka kai tsaye ya zarce dalar Amurka biliyan 40. Ta haka, kasar ta zama daya daga cikin manyan kasashen da suka fi zuba jari a nahiyar Afirka.

 

Ban da haka, a fannin ba da tallafi ga sauran kasashe, tsakanin shekarar 2004 da ta 2009, yawan kudin da kasar Sin ta ba kasashe daban daban a matsayin tallafi ya kan karu da kashi 29.4% a duk shekara. Sa’an nan, daga shekarar 2013 zuwa ta 2018, yawan kudin da Sin ta ba sauran kasashe ya kai kimanin dalar Amurka biliyan 28.3, inda a cikinsu kudin da aka ba kasashen Afirka ya kai kashi 44.65%.

 

Wadannan alkaluma sun shaida cewa, “Idan kasar Sin ta samu ci gaba, to, duk kasashen duniya ma za su samu cikakkiyar damar raya kansu”. Kana wasu manufofi da kasar Sin ta gabatar, irinsu gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya, da gina “Ziri Daya da Hanya Daya”, da shawarar raya daukacin duniya, da dai sauransu, dukkansu sun nuna yadda Sin take nacewa kan more damar raya tattalin arziki tare da kasashe daban daban. Ta haka, maufofin kasar Sin sun samu amincewa da goyon baya daga dimbin kasashe, da kungiyoyin kasa da kasa.

 

Don tinkarar yanayin hawa da saukar tattalin arzikin duniya, dabarar da kasar Sin ta dauka ita ce, raya tattalin arzikinta, sannan daga baya ta sa kasashe daban daban samun ci gaba tare. Sabanin yadda wasu kasashen dake yammacin duniya suka saba yi, wato ta da rikici da lallata tattalin arzikin sauran kasashe, don neman samun karuwar tattalin arzikinsu. Wannan bambanci, babban dalili ne da ya sanya imanin Sin da hasashenta mai kyau ke ci gaba da haifar da tasiri mai yakini kan tattalin arzikin duniya. (Bello Wang)

Tattalin arziki
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Tattalin arziki
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Aminu Bayero Ya Samu Nakasu Ta Ɓangaren Siyasa
Ra'ayi Riga

Aminu Bayero Ya Samu Nakasu Ta Ɓangaren Siyasa

June 15, 2026
Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Next Post
Yadda ‘Yan Bindiga Suka Sake Kashe Basarake A Arewa

Yadda 'Yan Bindiga Suka Sake Kashe Basarake A Arewa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.