Shugaba Bola Tinubu ya buƙaci ‘yan Nijeriya su rungumi haɗin kai, zaman lafiya da yafiya yayin da Musulmi suka fara azumin Ramadan.
Ya yi wannan jawabi ne a lokacin Tafsirin Ramadan da aka gudanar a Masallacin Fadar Gwamnati da ke Abuja.
- DSS Ta Kama El-Rufai Bayan EFCC Ta Bayar Da Belinsa
- Saka Ya Rattaba Hannu Akan Karin Kwantiragin Shekaru 5 A Arsenal
Shugaban ya ce wata mai alfarma lokaci ne na yin nazari, aikata alheri da komawa ga kyawawan ɗabi’u a tsakanin al’umma.
Ya kuma nemi jama’a su riƙa yafiya ga juna tare da yin aiki tare domin zaman lafiya da juna.
“Mun fara wannan Ramadan da darusan da yake koyarwa, kusanci da Allah, aikata alheri ga mutane, yaɗa ƙauna da imani, da kuma yafiya.
“Idan na taɓa ɓata wa wank rai, ina roƙon a yafe min. Dole mu koyi rayuwa cikin zaman lafiya da juna,” in ji Tinubu.
Shugaban ya ƙara da cewa azumin watan Ramadan ya kamata ya ƙarfafa ayyukan alheri da haɗin kai domin ci gaban Nijeriya.















Discussion about this post