Ƙungiyar kare haƙƙin tattalin arziki da bin diddigin ayyuka (SERAP) ta maka hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) a gaban kotu kan zargin ɓacewar naira biliyan 55.9 da aka ware domin sayen na’urar tantance karanta kati da takardun zaɓe da takardun sakamakon zaɓe da sauran kayan zaɓen 2019.
Zargin, wanda aka jaddada a sabon rahoton shekara-shekara na babban mai binciken kuɗi na gwamnatin tarayya da aka fitar tun a ranar 9 ga Satumbar 2025, na cewa INEC ta kasa bayar da cikakken bayani kan kuɗaɗen da aka raba wa masu aikin kwangila, tare da cewa wasu biyan kuɗin an yi su ba tare da bin ƙa’ida ba.
- PDP Ta Maka INEC A Kotu Kan Ƙin Amincewa Da Shugabancin Turaki
- INEC Ta Fara Kashi Na Biyu Na Rajistar Masu Zabe
A cikin ƙarar mai lamba FHC/ABJ/CS/38/2026, wadda aka shigar a ranar Juma’a da ta gabata a babban kotun tarayya a Abuja, SERAP tana neman umarnin kotu don tilasta wa INEC bayyana cikakkun bayanai game da kuɗaɗen da suka ɓace, ciki har da sunayen duk masu kwangilar da daraktocinsu da masu hannun jari da kuma dawo da kuɗin.
A cewar SERAP, gazawar hukumar wajen tabbatar da gaskiya da riƙon amana yana tauye haƙƙin ƴan Nijeriya na samun sahihin zaɓe mai cike da ƴanci da adalci.
“INEC ba za ta iya tabbatar da gudanar da sahihin zaɓe cikin gaskiya ba idan ba ta magance waɗannan zargin yadda ya kamata ba, an gurfanar da masu laifi, kuma an dawo da kuɗaɗen da ake zargin cin hanci da rashawa,” in ji ƙungiyar.
Rahoton babban mai binciken kuɗi na gwamnatin tarayya ya tayar da ƙura game da rashin daidaito da dama.
An bayar da rahoton cewa an biya ɗaruruwan naira biliyan 5.3 ga sayan na’urar tantance ba
tare da amincewar hukumar kula da sayen kayayyaki gwamnati ko majalisar zartarwa ta
gwamnatin tarayya, sannnan kuma ba tare da hujjar cewa an kawo kayan ba.
INEC ta yi iƙirarin cewa ta sayen kayan ya shiga cikin tsaron ƙasa, dalilin da babban mai binciken kuɗi na gwamnatin tarayya ya ƙi yarda da shi. Biyan fiye da naira biliyan 4.5 ga ɗimbin kwangiloli guda shida kan takardun jefa ƙuri’a da takardun sakamakon zaɓe ba su da takardu na tabbatarwa, ciki har da hujjojin hanyoyin yin tayin da cancantar kwangiloli.
Ƙarin biyan kuɗaɗen da ake zargin sun haɗa da naira miliyan 331 don kwangiloli daban-daban da naira biliyan 41 don bugu kayan zaɓe ba tare da bin ƙa’ida ba, da naira miliyan 297 don sayan motocin Toyota Land Cruiser guda huɗu, wanda kuɗaɗen ya wuce farashinsu a kasuwa.
Rahotanni sun nuna cewa hukumar ba ta mayar da naira miliyan 630 a matsayin rance na kuɗi ga jami’ai ba kuma ta yi watsi da cire fiye da naira biliyan 2.1 a matsayin harajin takarda daga kwangiloli.
Ƙungiyar SERAP, ƙarƙashin jagorancin Kolawole Oluwadare, Kehinde Oyewumi, da Andrew Nwankwo, ta yi iƙirarin cewa tuhumar da ake yi tana wakiltar mummunar keta amincewar jama’a da kundin tsarin mulkin Nijeriya da ƙa’idodin yaƙi da cin hanci na duniya.” Ba a sanya ranar sauraron shari’ar ba tukuna.















Discussion about this post