ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Na Fuskantar Shari’a Kan Ɓacewar Naira Biliyan 55.9 Kuɗaɗen Zaɓen 2019

by Leadership Hausa
5 months ago
Inec

Ƙungiyar kare haƙƙin tattalin arziki da bin diddigin ayyuka (SERAP) ta maka hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) a gaban kotu kan zargin ɓacewar naira biliyan 55.9 da aka ware domin sayen na’urar tantance karanta kati da takardun zaɓe da takardun sakamakon zaɓe da sauran kayan zaɓen 2019.
Zargin, wanda aka jaddada a sabon rahoton shekara-shekara na babban mai binciken kuɗi na gwamnatin tarayya da aka fitar tun a ranar 9 ga Satumbar 2025, na cewa INEC ta kasa bayar da cikakken bayani kan kuɗaɗen da aka raba wa masu aikin kwangila, tare da cewa wasu biyan kuɗin an yi su ba tare da bin ƙa’ida ba.

  • PDP Ta Maka INEC A Kotu Kan Ƙin Amincewa Da Shugabancin Turaki 
  • INEC Ta Fara Kashi Na Biyu Na Rajistar Masu Zabe

A cikin ƙarar mai lamba FHC/ABJ/CS/38/2026, wadda aka shigar a ranar Juma’a da ta gabata a babban kotun tarayya a Abuja, SERAP tana neman umarnin kotu don tilasta wa INEC bayyana cikakkun bayanai game da kuɗaɗen da suka ɓace, ciki har da sunayen duk masu kwangilar da daraktocinsu da masu hannun jari da kuma dawo da kuɗin.

A cewar SERAP, gazawar hukumar wajen tabbatar da gaskiya da riƙon amana yana tauye haƙƙin ƴan Nijeriya na samun sahihin zaɓe mai cike da ƴanci da adalci.

ADVERTISEMENT

“INEC ba za ta iya tabbatar da gudanar da sahihin zaɓe cikin gaskiya ba idan ba ta magance waɗannan zargin yadda ya kamata ba, an gurfanar da masu laifi, kuma an dawo da kuɗaɗen da ake zargin cin hanci da rashawa,” in ji ƙungiyar.

Rahoton babban mai binciken kuɗi na gwamnatin tarayya ya tayar da ƙura game da rashin daidaito da dama.

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

An bayar da rahoton cewa an biya ɗaruruwan naira biliyan 5.3 ga sayan na’urar tantance ba
tare da amincewar hukumar kula da sayen kayayyaki gwamnati ko majalisar zartarwa ta
gwamnatin tarayya, sannnan kuma ba tare da hujjar cewa an kawo kayan ba.

INEC ta yi iƙirarin cewa ta sayen kayan ya shiga cikin tsaron ƙasa, dalilin da babban mai binciken kuɗi na gwamnatin tarayya ya ƙi yarda da shi. Biyan fiye da naira biliyan 4.5 ga ɗimbin kwangiloli guda shida kan takardun jefa ƙuri’a da takardun sakamakon zaɓe ba su da takardu na tabbatarwa, ciki har da hujjojin hanyoyin yin tayin da cancantar kwangiloli.

Ƙarin biyan kuɗaɗen da ake zargin sun haɗa da naira miliyan 331 don kwangiloli daban-daban da naira biliyan 41 don bugu kayan zaɓe ba tare da bin ƙa’ida ba, da naira miliyan 297 don sayan motocin Toyota Land Cruiser guda huɗu, wanda kuɗaɗen ya wuce farashinsu a kasuwa.
Rahotanni sun nuna cewa hukumar ba ta mayar da naira miliyan 630 a matsayin rance na kuɗi ga jami’ai ba kuma ta yi watsi da cire fiye da naira biliyan 2.1 a matsayin harajin takarda daga kwangiloli.

Ƙungiyar SERAP, ƙarƙashin jagorancin Kolawole Oluwadare, Kehinde Oyewumi, da Andrew Nwankwo, ta yi iƙirarin cewa tuhumar da ake yi tana wakiltar mummunar keta amincewar jama’a da kundin tsarin mulkin Nijeriya da ƙa’idodin yaƙi da cin hanci na duniya.” Ba a sanya ranar sauraron shari’ar ba tukuna.

Inec
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Next Post
Komawa Makarantu: Iyaye Sun Shawarci Gwamnati Kan Tsaron Ɗalibai Da Malamai

Komawa Makarantu: Iyaye Sun Shawarci Gwamnati Kan Tsaron Ɗalibai Da Malamai

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.