ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Na Fuskantar Shari’a Kan Ɓacewar Naira Biliyan 55.9 Kuɗaɗen Zaɓen 2019

by Leadership Hausa
5 months ago
Inec

Ƙungiyar kare haƙƙin tattalin arziki da bin diddigin ayyuka (SERAP) ta maka hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) a gaban kotu kan zargin ɓacewar naira biliyan 55.9 da aka ware domin sayen na’urar tantance karanta kati da takardun zaɓe da takardun sakamakon zaɓe da sauran kayan zaɓen 2019.
Zargin, wanda aka jaddada a sabon rahoton shekara-shekara na babban mai binciken kuɗi na gwamnatin tarayya da aka fitar tun a ranar 9 ga Satumbar 2025, na cewa INEC ta kasa bayar da cikakken bayani kan kuɗaɗen da aka raba wa masu aikin kwangila, tare da cewa wasu biyan kuɗin an yi su ba tare da bin ƙa’ida ba.

  • PDP Ta Maka INEC A Kotu Kan Ƙin Amincewa Da Shugabancin Turaki 
  • INEC Ta Fara Kashi Na Biyu Na Rajistar Masu Zabe

A cikin ƙarar mai lamba FHC/ABJ/CS/38/2026, wadda aka shigar a ranar Juma’a da ta gabata a babban kotun tarayya a Abuja, SERAP tana neman umarnin kotu don tilasta wa INEC bayyana cikakkun bayanai game da kuɗaɗen da suka ɓace, ciki har da sunayen duk masu kwangilar da daraktocinsu da masu hannun jari da kuma dawo da kuɗin.

A cewar SERAP, gazawar hukumar wajen tabbatar da gaskiya da riƙon amana yana tauye haƙƙin ƴan Nijeriya na samun sahihin zaɓe mai cike da ƴanci da adalci.

ADVERTISEMENT

“INEC ba za ta iya tabbatar da gudanar da sahihin zaɓe cikin gaskiya ba idan ba ta magance waɗannan zargin yadda ya kamata ba, an gurfanar da masu laifi, kuma an dawo da kuɗaɗen da ake zargin cin hanci da rashawa,” in ji ƙungiyar.

Rahoton babban mai binciken kuɗi na gwamnatin tarayya ya tayar da ƙura game da rashin daidaito da dama.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

An bayar da rahoton cewa an biya ɗaruruwan naira biliyan 5.3 ga sayan na’urar tantance ba
tare da amincewar hukumar kula da sayen kayayyaki gwamnati ko majalisar zartarwa ta
gwamnatin tarayya, sannnan kuma ba tare da hujjar cewa an kawo kayan ba.

INEC ta yi iƙirarin cewa ta sayen kayan ya shiga cikin tsaron ƙasa, dalilin da babban mai binciken kuɗi na gwamnatin tarayya ya ƙi yarda da shi. Biyan fiye da naira biliyan 4.5 ga ɗimbin kwangiloli guda shida kan takardun jefa ƙuri’a da takardun sakamakon zaɓe ba su da takardu na tabbatarwa, ciki har da hujjojin hanyoyin yin tayin da cancantar kwangiloli.

Ƙarin biyan kuɗaɗen da ake zargin sun haɗa da naira miliyan 331 don kwangiloli daban-daban da naira biliyan 41 don bugu kayan zaɓe ba tare da bin ƙa’ida ba, da naira miliyan 297 don sayan motocin Toyota Land Cruiser guda huɗu, wanda kuɗaɗen ya wuce farashinsu a kasuwa.
Rahotanni sun nuna cewa hukumar ba ta mayar da naira miliyan 630 a matsayin rance na kuɗi ga jami’ai ba kuma ta yi watsi da cire fiye da naira biliyan 2.1 a matsayin harajin takarda daga kwangiloli.

Ƙungiyar SERAP, ƙarƙashin jagorancin Kolawole Oluwadare, Kehinde Oyewumi, da Andrew Nwankwo, ta yi iƙirarin cewa tuhumar da ake yi tana wakiltar mummunar keta amincewar jama’a da kundin tsarin mulkin Nijeriya da ƙa’idodin yaƙi da cin hanci na duniya.” Ba a sanya ranar sauraron shari’ar ba tukuna.

Inec
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Komawa Makarantu: Iyaye Sun Shawarci Gwamnati Kan Tsaron Ɗalibai Da Malamai

Komawa Makarantu: Iyaye Sun Shawarci Gwamnati Kan Tsaron Ɗalibai Da Malamai

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.