ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Na Fuskantar Shari’a Kan Ɓacewar Naira Biliyan 55.9 Kuɗaɗen Zaɓen 2019

by Leadership Hausa
6 months ago
Inec

Ƙungiyar kare haƙƙin tattalin arziki da bin diddigin ayyuka (SERAP) ta maka hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) a gaban kotu kan zargin ɓacewar naira biliyan 55.9 da aka ware domin sayen na’urar tantance karanta kati da takardun zaɓe da takardun sakamakon zaɓe da sauran kayan zaɓen 2019.
Zargin, wanda aka jaddada a sabon rahoton shekara-shekara na babban mai binciken kuɗi na gwamnatin tarayya da aka fitar tun a ranar 9 ga Satumbar 2025, na cewa INEC ta kasa bayar da cikakken bayani kan kuɗaɗen da aka raba wa masu aikin kwangila, tare da cewa wasu biyan kuɗin an yi su ba tare da bin ƙa’ida ba.

  • PDP Ta Maka INEC A Kotu Kan Ƙin Amincewa Da Shugabancin Turaki 
  • INEC Ta Fara Kashi Na Biyu Na Rajistar Masu Zabe

A cikin ƙarar mai lamba FHC/ABJ/CS/38/2026, wadda aka shigar a ranar Juma’a da ta gabata a babban kotun tarayya a Abuja, SERAP tana neman umarnin kotu don tilasta wa INEC bayyana cikakkun bayanai game da kuɗaɗen da suka ɓace, ciki har da sunayen duk masu kwangilar da daraktocinsu da masu hannun jari da kuma dawo da kuɗin.

A cewar SERAP, gazawar hukumar wajen tabbatar da gaskiya da riƙon amana yana tauye haƙƙin ƴan Nijeriya na samun sahihin zaɓe mai cike da ƴanci da adalci.

ADVERTISEMENT

“INEC ba za ta iya tabbatar da gudanar da sahihin zaɓe cikin gaskiya ba idan ba ta magance waɗannan zargin yadda ya kamata ba, an gurfanar da masu laifi, kuma an dawo da kuɗaɗen da ake zargin cin hanci da rashawa,” in ji ƙungiyar.

Rahoton babban mai binciken kuɗi na gwamnatin tarayya ya tayar da ƙura game da rashin daidaito da dama.

LABARAI MASU NASABA

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

An bayar da rahoton cewa an biya ɗaruruwan naira biliyan 5.3 ga sayan na’urar tantance ba
tare da amincewar hukumar kula da sayen kayayyaki gwamnati ko majalisar zartarwa ta
gwamnatin tarayya, sannnan kuma ba tare da hujjar cewa an kawo kayan ba.

INEC ta yi iƙirarin cewa ta sayen kayan ya shiga cikin tsaron ƙasa, dalilin da babban mai binciken kuɗi na gwamnatin tarayya ya ƙi yarda da shi. Biyan fiye da naira biliyan 4.5 ga ɗimbin kwangiloli guda shida kan takardun jefa ƙuri’a da takardun sakamakon zaɓe ba su da takardu na tabbatarwa, ciki har da hujjojin hanyoyin yin tayin da cancantar kwangiloli.

Ƙarin biyan kuɗaɗen da ake zargin sun haɗa da naira miliyan 331 don kwangiloli daban-daban da naira biliyan 41 don bugu kayan zaɓe ba tare da bin ƙa’ida ba, da naira miliyan 297 don sayan motocin Toyota Land Cruiser guda huɗu, wanda kuɗaɗen ya wuce farashinsu a kasuwa.
Rahotanni sun nuna cewa hukumar ba ta mayar da naira miliyan 630 a matsayin rance na kuɗi ga jami’ai ba kuma ta yi watsi da cire fiye da naira biliyan 2.1 a matsayin harajin takarda daga kwangiloli.

Ƙungiyar SERAP, ƙarƙashin jagorancin Kolawole Oluwadare, Kehinde Oyewumi, da Andrew Nwankwo, ta yi iƙirarin cewa tuhumar da ake yi tana wakiltar mummunar keta amincewar jama’a da kundin tsarin mulkin Nijeriya da ƙa’idodin yaƙi da cin hanci na duniya.” Ba a sanya ranar sauraron shari’ar ba tukuna.

Inec
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
Next Post
Komawa Makarantu: Iyaye Sun Shawarci Gwamnati Kan Tsaron Ɗalibai Da Malamai

Komawa Makarantu: Iyaye Sun Shawarci Gwamnati Kan Tsaron Ɗalibai Da Malamai

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.