Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, ta bayyana cewa ta kammala dukkan shirye-shiryen gudanar da zaɓen gwamnan Jihar Ekiti da zaɓukan cike gurbi da za a gudanar a ranar Asabar a wasu jihohin ƙasar nan.
Zaɓukan sun haɗa da na gwamnan Jihar Ekiti da kuma na cike gurbi a mazaɓar tarayya ta Dawaki Kudu/Warawa a Jihar Kano, da mazaɓar Zuru a Jihar Kebbi, tare da wasu mazaɓun Sanata a jihohin Ondo, Rivers, Nasarawa da Enugu.
Mataimakin Daraktan Wayar da Kai da Ilimantar da Masu Zaɓe na INEC, Wilfred Ifogah, ya ce hukumar ta horas da ma’aikatanta da jami’an wucin gadi tare da ɗaukar matakan da suka dace domin tabbatar da gudanar da sahihin zaɓe cikin lumana. Ya ce jami’an tsaro za su kasance a cibiyoyin kaɗa ƙuri’a da wuraren ajiyar kayan zaɓe, yayin da aka umurci jami’an zaɓe su isa wuraren aikinsu da ƙarfe 7:30 na safe kafin fara kaɗa ƙuri’a da ƙarfe 8:30.
A wani ɓangare kuma, INEC ta bayyana cewa an ƙarbi katunan zaɓe na dindindin (PVC) guda 1,028,929 a faɗin Jihar Ekiti, adadin da ya kai kashi 97.1 cikin 100 na masu rajistar zaɓe. Hukumar ta ce wannan ya fi adadin da aka samu a zaɓen shekarar 2023, inda aka karɓi katuna 958,052.
Hukumar ta kuma ce yawan masu rajistar zaɓe a Ekiti ya ƙaru daga 987,647 a shekarar 2023 zuwa 1,059,360 a shekarar 2026 bayan kammala aikin sabunta rajistar masu zaɓe. INEC ta buƙaci jam’iyyun siyasa da magoya bayansu su guji duk wani abu da ka iya tayar da rikici, tare da kira ga masu zaɓe da suka karɓi katunansu da su fito cikin lumana su kaɗa ƙuri’unsu.















Discussion about this post