Kasar Sin ta sabunta alkawarin da ta yi na karfafa kawancenta da Nijeriya yayin da jakadan kasar Yu Dunhai ya gana da shugaba Bola Ahmed Tinubu a fadar shugaban kasa da ke Abuja a ranar Jumma’ar nan da ta gabata.
A cewar jakada Yu, dangantakar kasashen biyu ta shiga wani lokaci na samun ci gaba cikin hanzari wanda ya samo asali daga gudanar da mu’amala mai zurfi a matakin koli da kuma manyan tsare-tsare na bai-daya. Yu ya yi nuni da cewa, kasar Sin da Nijeriya sun ci gaba da tallafa wa juna kan batutuwan da suka shafi muhimman muradun kasarsu.
Ya kuma jaddada cewa, Sin na ci gaba da goyon bayan kokarin Nijeriya a kan inganta tsaro, gami da shirye-shiryen da aka bullo da su da nufin yaki da ta’addanci da kuma karfafa kwanciyar hankali. Jakadan ya kuma jaddada kudurin kasar Sin na hanzarta aiwatar da soke haraji ga kayayyakin da Nijeriya ke fitarwa zuwa kasar, wadda manufa ce da aka tsara don bunkasa cinikayya da kuma bude sabbin hanyoyin hadin gwiwa a fannin tattalin arziki.
A nasa bangaren, shugaba Tinubu ya yi maraba da sabbin tabbacin da kasar Sin ta bayar, yana mai nuna amincewa da rawar da kasar ta taka wajen tallafa wa burin ci gaban Nijeriya. Ya bayyana kudurin Nijeriya na kara zurfafa mu’amala da kasar Sin, musamman a fannoni da ke kawo sauyi ga tattalin arziki, da inganta tsaro, da kuma bunkasa samun wadata tare. (Abdulrazaq Yahuza Jere)














