Ministan kula da bunƙasa fanin tattalin arzki na Teku Dakta Adegboyega Oyetola, ya ƙaddamar da ƙungiyar Daraktocin makuntan ƙungiyar kula da hada-hadar sufurin Jiragen Ruwa ta Gabas da kuma Afirka ta Tsakiya wato PMAWCA.
Oyetola wanda ya ƙaddamar da ƙungiyar a ranar Litinin ya sanar da cewa, ƙasar nan na ci gaba da ƙara faɗaɗa Tashoshin Jiragen Ruwan ƙasar, tare da kuma wanzar da sabbin sauye-sauye a fannin.
Minisntan wanda ya bayyana haka, a cikin sanarwar da Mai Bashi Shawara ta Musamman Dakta Bolaji Akinola ya fitar a madadin Ministan, ya ce, manufar sauye-sauyen shi ne, domin a saita ɓangaren sufurin na Jiragen Ruwan ƙasar, duba da cewa, Nijeriya, na ci gaba da zama kan gaba, a ɓangaren hada-hadar jigilar kaya ta Ruwa, a tsakanin Gabas da kuma a Afirka ta Tsakiya.
Dakta Oyetola, ya sanar da haka ne, yayin da buɗe fagen taron ƙungiyar, na tsakiyar shekarar 2026, da ya gudana a yankin Ɓictoria Island da ke a jihar Legas.
Taken taron: Bunƙasa Makomar Tashoshin Jiragen Ruwa, Da Haɓaka Safarar Kaya Tare Da Inganta Ruwar Alumma.”
Kazalika, Ministan ya ƙara da cewa, Gwamnatin Taryya, ta amince da a ƙara samar da wasu ƙananan Tashoshin Jiragen Ruwa, a ɗaukacin faɗin ƙasar, domin a ƙara haɓaka hada-hadar safarar kaya, wanda hakan zai ƙara bai wa ƙasar, damar yin tafiya kafaɗa da kafaɗa, da sauran Tashoshin Jiragen Ruwa na faɗin duniya.
Ya ci gaba da cewa, Gwamnatin Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, na ci gaba da yin ƙoƙari, wajen ƙara zamanantar da Tashoshin Jiragen Ruwa na ƙasar.
Tun da farko, a jawabinsa na maraba a wajen taron Shugaban Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Ruwa na ƙasa NPA Dakta Abubakar Ɗantsoho, ya bayyana cewa, ana ci gaba da samun gagarumin, ƙaruwar zuja jari a fannin sufurin Jiragen Ruwa, a Gabas da kuma Afirka ta Tsakiya, tare da kuma wasu da ayyukan da ke tafe, da kuɗinsu ya kai na sama da dala biliyan 27, a ɗaukacin faɗin yankin.
Ɗantsoho wanda kuma shi ne har ila yau shugaban ƙungiyar ta PMAWCA, ya buƙa misali da wasu akkyan da suka kai na dala biliayan 20, kamar dai na ƙananan Tashin Jiragen Ruwa na Simandou-Morebaya da ke a ƙasar Guinea.
Ya ci gaba da cewa, akwai kuma aikin Tashar San Pedro da ke a ƙasar Côte d’Iɓoire, da kuɗinsa ya kai na dala bilyana biyu 2, sai kuma na Tashar Lekki da ke a jihar Legas, da kuɗin ya kai na dala biliyan 1.5.
A cewarsa, ana kuma kan ci gaba da bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa na ƙasasehn Ghana da Senegal.
Ya kuma Ambato batun zuba jari a Tashoshin Apapa da Tin Can Island, tare da na jarin guraren ajiya kaya na APM da ya kai na dala miliyan 600.
Shugaban ya yi nuni da cewa, lokaci ya yi da za a wuce batun gudanar da ayyuka a ɓangaren sufurin Jiragen Ruwa a Gabasa da kuma Afirka ta Yamma, ta hanyar gargajiya, musamman duba da cewa, hanyoyin Ruwa, sun kasance tamkar wasu ginshiƙan ƙara haɓaka hada-hadar kasuwanci na Teku.
A cewarsa, fannin na kuma ci gaba da bunƙasa samar da makamashi, aikin noma gudanar da harkar kamun Kifi, da sauransu
Wasu daga cikin manyan baƙin da suka halrci taron ƙaddamawar na kwana biyu, sun haɗa da, Gwamnonin jihohin Taraba, Dakta Kefas Agbu; da takwaransa na Legas wanda kwamishinan Sufuri Mista Oluwaseun Osiyemi; ya wakilce shi.
Sauran baƙin su ne, Shugaban Kamfanin Rukunonin Ɗangote Group, Alhaji Aliko Ɗangote da kuma Hadiza Bala Usman, Babbar Mai Bai Wa shugaban ƙasa shawara, kan tsare-tsare da sauransu.














Discussion about this post