Jam’iyyun adawa a fadin Nijeriya sun ajiye bambance-bambancensu, sun nuna niyyarsu ta gabatar da dan takarar shugaban kasa daya a zaben 2027, wajen kwace mulki daga hannun jam’iyyar APC.
Sun yi gargadin cewa abin da ake ganin rinjayar jam’iyyar APC, na iya zama barazana ga zabe mai zuwa. Sun dauki wannan matakin ne a cikin wata sanarwa da aka fitar bayan taron kolin da ya gudana a garin Ibadan.
A taron, wanda manyan ‘yan adawa suka halarta ciki har da Atiku Abubakar, Rabiu Musa Kwankwaso, Rotimi Amaechi, Peter Obi da Rauf Aregbesola, sun hadu don tsara wata dabarar hadin gwiwa.
Bayan karanta sanarwar, shugaban zagin jam’iyyar PDP, Taminu Turaki, ya ce, “Za mu yi adawa da duk wani shiri na APC don tilasta wa Nijeriya tsarin jam’iyyar guda daya kuma mu yi yaki don tsiratar da jam’iyyu da dama a kasarmu. Duk da hare-hare da dabarun jam’iyyar gwamnati, za mu tura ‘yan takara mu yi gogayya a zaben shugaban kasa da sauran zabuka a 2027.
“Za mu yi aiki tare don fitar da dan takarar shugabacc kasa a zaben shekara ta 2027, wanda dukkan jam’iyyun adawa masu halartar wannan taro sun goyi baya don ceto kasarmu da talakawanta da suka dadde suna wahala.
Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Joash Ojo Amupitan, wanda ya nuna son rai da nuna bangaranci wajen taimakon APC mai mulki, bai kamata ya jagoranci zaben 2027 ba. Ci gaba da kasancewarsa a ofis yana haifar da damuwa kuma yana iya jawo rikice-rikice a fadin kasar nan. Majalisar dokoki ta kasa ya kamata ta sake duba dokar zabe ta 2026 nan take, don cire duk sashe-sashen da ke barazana ga sahihincin zabuka.
“Muna daukar sabbin ka’idodin da INEC ta fitar a matsayin shinge, wanda aka tsara su da niyya sanya sharudda da wa’adin lokaci ga jam’iyyun adawa. INEC ya kamata ta kara wa’adin gudanar da zabukan fitar da gwani har zuwa karshen watan Yulin 2026.”
A farkon jawabinsa, gwamna mai masaukin baki, Seyi Makinde, ya yi gargadin cewa dimokuradiyyar Nijeriya na fuskantar rushewa a hankalin yanzu, saboda raunana jam’iyyun adawa.
Ya ce, “A fadin Nijeriya a yau, muna shaida wani irin matakin na siyasa wanda ya kamata ya dame mu duka. Suna nuna wani tsari wanda ya saba wa gasar siyasar kasar nan.”
Makinde ya gargadin cewa dimokiradiyya ba a hallaka ta cikin dare daya ba, amma ana raunana ta a hankali-hankali. Ya jaddada cewa lokacin da adawa ta zama mara tasiri, dimokiradiyya kanta tana fara rasa ma’ana.
Ya jaddada cewa dole ne a fayyace dimokuradiyya ta hanyar kasancewar zabuka na gaskiya, kuma ya yi gargadin cewa ba tare da wannan ba, “abin da muke da shi na iya ci gaba da kiran sa dimokuradiyya, ba zai ci gaba da aiki a matsayi daya ba.”
Gwamnan ya kuma fayyace manufar taron, yana mai cewa, “Ba wani yunkurin haduwa ne don kai hari ga mutum guda ba. Kuma ba game da buri na mutum daya na zama shugaban kasa ba. Abin da yake magana a kai shi ne, buri na hadin gwiwar ‘yan Nijeriya don samun dimokuradiyya mai kyau wanda aka ayyana daidai.
Ya karfafa masu ruwa da tsaki su yi tunani mai kyau, su yi magana da gaskiya, kuma su yi aiki da hadin kai da ya zarce iyakokin jam’iyya.
Da yake magana a taron, shugaban jam’iyyar ADC, Dabid Mark, ya bayyana taron a matsayin wani lokaci mai muhimmanci a tarihin Nijeriya, inda ya kira shi da suna, “wani gaggawar amsa kiran kasarmu na yi aiki tare.”
Ya ce: “Addu’ata ita ce tarihi ya maimaita kansa a gare mu, cewa lokacin da kasa ta yi ihu don a ceci ta, mun amsa. Lokacin da yara suka kwanta barci da yunwa, mun amsa, lokacin da ‘yan kasa masu aiki tukuru suka koma bara, mun amsa.
“A fadin kasarmu, rashin tsaro ya zama wani bangare na rayuwar yau da kullum. Nijeriya na fuskantar wani babban kalubale na tarihi. A shekarar 2025 kadai, Nijeriya ta samu fiye da mutuwar mutane 12,000 sakamakon rikice-rikice. Yanzu haka Nijeriya ta kasance ta hudu a cikin jerin kasashe masu fuskantar ta’addanci na duniya. Akalla ‘yan Nijeriya 15 ake kashewa kullum, yayin da kusan mutane 19 ake sacewa.
“Muna cikin wata kasa da kullum tana cikin bakin ciki, amma gwamnatin APC ta yi kamar komai lafiya lau. Ta mayar da hankali ga harkokin zabe da siyasa gaba daya.
“Wannan zabe zai kasance ne a tsakanin jam’iyyar mulki ta APC, da mutanen Nijeriya. Muna tare da mutanen kasar nan. ‘Yan Nijeriya sun rasa amincewa ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa. Bari wannan taron ya shiga tarihi a matsayin lokaci da kome ya canza. Mun zabi hadin kai a kan rarrabuwar kai, sadaukarwa ga kasa sama da komai.”















Discussion about this post