ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyun Adawa Sun Hada Kai Don Tsayar Da Dan Takara Guda A Zaben 2027

by Yusuf Shuaibu
2 months ago
Adawa

Jam’iyyun adawa a fadin Nijeriya sun ajiye bambance-bambancensu, sun nuna niyyarsu ta gabatar da dan takarar shugaban kasa daya a zaben 2027, wajen kwace mulki daga hannun jam’iyyar APC.

Sun yi gargadin cewa abin da ake ganin rinjayar jam’iyyar APC, na iya zama barazana ga zabe mai zuwa. Sun dauki wannan matakin ne a cikin wata sanarwa da aka fitar bayan taron kolin da ya gudana a garin Ibadan.

A taron, wanda manyan ‘yan adawa suka halarta ciki har da Atiku Abubakar, Rabiu Musa Kwankwaso, Rotimi Amaechi, Peter Obi da Rauf Aregbesola, sun hadu don tsara wata dabarar hadin gwiwa.

ADVERTISEMENT

Bayan karanta sanarwar, shugaban zagin jam’iyyar PDP, Taminu Turaki, ya ce, “Za mu yi adawa da duk wani shiri na APC don tilasta wa Nijeriya tsarin jam’iyyar guda daya kuma mu yi yaki don tsiratar da jam’iyyu da dama a kasarmu. Duk da hare-hare da dabarun jam’iyyar gwamnati, za mu tura ‘yan takara mu yi gogayya a zaben shugaban kasa da sauran zabuka a 2027.

“Za mu yi aiki tare don fitar da dan takarar shugabacc kasa a zaben shekara ta 2027, wanda dukkan jam’iyyun adawa masu halartar wannan taro sun goyi baya don ceto kasarmu da talakawanta da suka dadde suna wahala.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Joash Ojo Amupitan, wanda ya nuna son rai da nuna bangaranci wajen taimakon APC mai mulki, bai kamata ya jagoranci zaben 2027 ba. Ci gaba da kasancewarsa a ofis yana haifar da damuwa kuma yana iya jawo rikice-rikice a fadin kasar nan. Majalisar dokoki ta kasa ya kamata ta sake duba dokar zabe ta 2026 nan take, don cire duk sashe-sashen da ke barazana ga sahihincin zabuka.

“Muna daukar sabbin ka’idodin da INEC ta fitar a matsayin shinge, wanda aka tsara su da niyya sanya sharudda da wa’adin lokaci ga jam’iyyun adawa. INEC ya kamata ta kara wa’adin gudanar da zabukan fitar da gwani har zuwa karshen watan Yulin 2026.”

A farkon jawabinsa, gwamna mai masaukin baki, Seyi Makinde, ya yi gargadin cewa dimokuradiyyar Nijeriya na fuskantar rushewa a hankalin yanzu, saboda raunana jam’iyyun adawa.

Ya ce, “A fadin Nijeriya a yau, muna shaida wani irin matakin na siyasa wanda ya kamata ya dame mu duka. Suna nuna wani tsari wanda ya saba wa gasar siyasar kasar nan.”

Makinde ya gargadin cewa dimokiradiyya ba a hallaka ta cikin dare daya ba, amma ana raunana ta a hankali-hankali. Ya jaddada cewa lokacin da adawa ta zama mara tasiri, dimokiradiyya kanta tana fara rasa ma’ana.

Ya jaddada cewa dole ne a fayyace dimokuradiyya ta hanyar kasancewar zabuka na gaskiya, kuma ya yi gargadin cewa ba tare da wannan ba, “abin da muke da shi na iya ci gaba da kiran sa dimokuradiyya, ba zai ci gaba da aiki a matsayi daya ba.”

Gwamnan ya kuma fayyace manufar taron, yana mai cewa, “Ba wani yunkurin haduwa ne don kai hari ga mutum guda ba. Kuma ba game da buri na mutum daya na zama shugaban kasa ba. Abin da yake magana a kai shi ne, buri na hadin gwiwar ‘yan Nijeriya don samun dimokuradiyya mai kyau wanda aka ayyana daidai.

Ya karfafa masu ruwa da tsaki su yi tunani mai kyau, su yi magana da gaskiya, kuma su yi aiki da hadin kai da ya zarce iyakokin jam’iyya.

Da yake magana a taron, shugaban jam’iyyar ADC, Dabid Mark, ya bayyana taron a matsayin wani lokaci mai muhimmanci a tarihin Nijeriya, inda ya kira shi da suna, “wani gaggawar amsa kiran kasarmu na yi aiki tare.”

Ya ce: “Addu’ata ita ce tarihi ya maimaita kansa a gare mu, cewa lokacin da kasa ta yi ihu don a ceci ta, mun amsa. Lokacin da yara suka kwanta barci da yunwa, mun amsa, lokacin da ‘yan kasa masu aiki tukuru suka koma bara, mun amsa.

“A fadin kasarmu, rashin tsaro ya zama wani bangare na rayuwar yau da kullum. Nijeriya na fuskantar wani babban kalubale na tarihi. A shekarar 2025 kadai, Nijeriya ta samu fiye da mutuwar mutane 12,000 sakamakon rikice-rikice. Yanzu haka Nijeriya ta kasance ta hudu a cikin jerin kasashe masu fuskantar ta’addanci na duniya. Akalla ‘yan Nijeriya 15 ake kashewa kullum, yayin da kusan mutane 19 ake sacewa.

“Muna cikin wata kasa da kullum tana cikin bakin ciki, amma gwamnatin APC ta yi kamar komai lafiya lau. Ta mayar da hankali ga harkokin zabe da siyasa gaba daya.

“Wannan zabe zai kasance ne a tsakanin jam’iyyar mulki ta APC, da mutanen Nijeriya. Muna tare da mutanen kasar nan. ‘Yan Nijeriya sun rasa amincewa ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa. Bari wannan taron ya shiga tarihi a matsayin lokaci da kome ya canza. Mun zabi hadin kai a kan rarrabuwar kai, sadaukarwa ga kasa sama da komai.”

Adawa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Sabon Tsarin Tattaunawa Don Kawo Karshen Rikicin Fulani Makiyaya Da Manoma

Sabon Tsarin Tattaunawa Don Kawo Karshen Rikicin Fulani Makiyaya Da Manoma

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.