ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Tsarin Tattaunawa Don Kawo Karshen Rikicin Fulani Makiyaya Da Manoma

by Abubakar Abba
2 months ago
Manoma

Batun magance yawan samun rikici a tsakanin Fulani makiyaya a kasar nan, shi ne ya kasance kan gaba a taron masu ruwa da tsaki da masu yin dokoki da kuma masu zuba jari a kasar suka gudanar a babban birnin tarayyar Abuja.

Taron ya kunshi batun noman zamani da fitar da amfanin gona zuwa ketare na Afrika na shekarar 2026 (AGROMEKA EDPO 2026).

Taron wanda ya kasance na kwana biyu, cibiyar baje kolin kasuwanci da  masana’antu, reshen Abuja ce ta shirya shi, tare da hadaka da gonar JMT Plus.

ADVERTISEMENT

Manufar taron shi ne, domin samar da dauki wajen yin amfani da kayan zamani a fannin aikin noman kasar, tare kuma da fitar da amfanin da aka noma zuwa kasashen ketare.

Kazalika, taron ya wuce batu kan mayar da hankali a kan hada-hadar kasuwanci, amma ya bayar da damar tattaunawa a kan yadda za a kawo karshen rikice-rikicen da ke yawan afkuwa a tsakanin monoma da Fulani makiyaya

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

An dai shafe shekaru da dama a kasar nan, ana samun yawan afkuwar wannan matsala, wacce kuma har yanzu ta ke ci gaba afkuwa, wanda lamarin ke haddasa rasa rayukan dukkanin bangarorin biyu da haifar da dakatar da yin kiwon dabbobi da da yin noma, tare da kuma zama babbar barazana ga tsaron kasar.

Hakazalika, rikice-rikicen a tsakanin bangarorin biyu, ya fi yin kamari a yankin Nijeriya ta tsakiya, wato Middle Belt, ya kuma samo asali ne a kan batun mallakar kasar noma da albarkatun ruwa da afkuwar sauyin yanayi da yawan karuwar al’umma, tare da kuma rashin samar da kyakyawan tsari ga fannin aikin noma na kasar nan.

Cif Emeka Obegolu, shugaban cibiyar da yake bayani a kan shirin ya bayyana cewa;  shirin ya kuma hada da manyan masu ruwa da tsaki da za su tattauna a kan yadda za a lalubo da mafita a rikice-rikicen da ke afkuwa a tsakanin Fulani makiyaya da kuma manoma, musamman domin ci gaba da bunkasa fannin aikin na noma a fadin kasar nan.

Ya ci gaba da cewa, manoma da Fulani makiyaya da jagororin al’umma da ‘yan kasuwa da ke hada-hadar kasuwancin amfanin gona da kuma jami’in gwamnati, za su halarci taron na tattaunawar, domin kawo karshen kalubalen da kuma tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a tsakanin bangarorin biyu

Obegolu ya danganta baje kolin, a matsayin batun baje haja, inda ya ce; taron ya kai matakin yadda kasar za ta fara yin aikin noma da kaya na zamani.

Taken taron shi ne, yin amfani da fasahar zamani, domin zuba jari a fannin fitar da kayan amfanin gona zuwa kasashen ketare tare kara habaka fannin akin noma da kuma rage asarar da ake yi, sakamakon rikice-rikicen Fulani makiyaya da kuma manoman kasar nan.

Ya ci gaba da cewa, rungumar yin noma da kayan na zamani, ciki har da yin noman rani, zai rage yawan lalacewar kasar noma a kasar nan tare da kuma magance yawan samun rikice-rikice a tsakanin Fulani makiyaya da kuma manoman kasar.

Manoma
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Gwamnatin Jihar Katsina Za Ta Sayar Wa Da Manoma Takin Zamani Kan Farashi Mai Rahusa

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.