ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Tsarin Tattaunawa Don Kawo Karshen Rikicin Fulani Makiyaya Da Manoma

by Abubakar Abba
2 months ago
Manoma

Batun magance yawan samun rikici a tsakanin Fulani makiyaya a kasar nan, shi ne ya kasance kan gaba a taron masu ruwa da tsaki da masu yin dokoki da kuma masu zuba jari a kasar suka gudanar a babban birnin tarayyar Abuja.

Taron ya kunshi batun noman zamani da fitar da amfanin gona zuwa ketare na Afrika na shekarar 2026 (AGROMEKA EDPO 2026).

Taron wanda ya kasance na kwana biyu, cibiyar baje kolin kasuwanci da  masana’antu, reshen Abuja ce ta shirya shi, tare da hadaka da gonar JMT Plus.

ADVERTISEMENT

Manufar taron shi ne, domin samar da dauki wajen yin amfani da kayan zamani a fannin aikin noman kasar, tare kuma da fitar da amfanin da aka noma zuwa kasashen ketare.

Kazalika, taron ya wuce batu kan mayar da hankali a kan hada-hadar kasuwanci, amma ya bayar da damar tattaunawa a kan yadda za a kawo karshen rikice-rikicen da ke yawan afkuwa a tsakanin monoma da Fulani makiyaya

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

An dai shafe shekaru da dama a kasar nan, ana samun yawan afkuwar wannan matsala, wacce kuma har yanzu ta ke ci gaba afkuwa, wanda lamarin ke haddasa rasa rayukan dukkanin bangarorin biyu da haifar da dakatar da yin kiwon dabbobi da da yin noma, tare da kuma zama babbar barazana ga tsaron kasar.

Hakazalika, rikice-rikicen a tsakanin bangarorin biyu, ya fi yin kamari a yankin Nijeriya ta tsakiya, wato Middle Belt, ya kuma samo asali ne a kan batun mallakar kasar noma da albarkatun ruwa da afkuwar sauyin yanayi da yawan karuwar al’umma, tare da kuma rashin samar da kyakyawan tsari ga fannin aikin noma na kasar nan.

Cif Emeka Obegolu, shugaban cibiyar da yake bayani a kan shirin ya bayyana cewa;  shirin ya kuma hada da manyan masu ruwa da tsaki da za su tattauna a kan yadda za a lalubo da mafita a rikice-rikicen da ke afkuwa a tsakanin Fulani makiyaya da kuma manoma, musamman domin ci gaba da bunkasa fannin aikin na noma a fadin kasar nan.

Ya ci gaba da cewa, manoma da Fulani makiyaya da jagororin al’umma da ‘yan kasuwa da ke hada-hadar kasuwancin amfanin gona da kuma jami’in gwamnati, za su halarci taron na tattaunawar, domin kawo karshen kalubalen da kuma tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a tsakanin bangarorin biyu

Obegolu ya danganta baje kolin, a matsayin batun baje haja, inda ya ce; taron ya kai matakin yadda kasar za ta fara yin aikin noma da kaya na zamani.

Taken taron shi ne, yin amfani da fasahar zamani, domin zuba jari a fannin fitar da kayan amfanin gona zuwa kasashen ketare tare kara habaka fannin akin noma da kuma rage asarar da ake yi, sakamakon rikice-rikicen Fulani makiyaya da kuma manoman kasar nan.

Ya ci gaba da cewa, rungumar yin noma da kayan na zamani, ciki har da yin noman rani, zai rage yawan lalacewar kasar noma a kasar nan tare da kuma magance yawan samun rikice-rikice a tsakanin Fulani makiyaya da kuma manoman kasar.

Manoma
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Gwamnatin Jihar Katsina Za Ta Sayar Wa Da Manoma Takin Zamani Kan Farashi Mai Rahusa

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.