Batun magance yawan samun rikici a tsakanin Fulani makiyaya a kasar nan, shi ne ya kasance kan gaba a taron masu ruwa da tsaki da masu yin dokoki da kuma masu zuba jari a kasar suka gudanar a babban birnin tarayyar Abuja.
Taron ya kunshi batun noman zamani da fitar da amfanin gona zuwa ketare na Afrika na shekarar 2026 (AGROMEKA EDPO 2026).
Taron wanda ya kasance na kwana biyu, cibiyar baje kolin kasuwanci da masana’antu, reshen Abuja ce ta shirya shi, tare da hadaka da gonar JMT Plus.
Manufar taron shi ne, domin samar da dauki wajen yin amfani da kayan zamani a fannin aikin noman kasar, tare kuma da fitar da amfanin da aka noma zuwa kasashen ketare.
Kazalika, taron ya wuce batu kan mayar da hankali a kan hada-hadar kasuwanci, amma ya bayar da damar tattaunawa a kan yadda za a kawo karshen rikice-rikicen da ke yawan afkuwa a tsakanin monoma da Fulani makiyaya
An dai shafe shekaru da dama a kasar nan, ana samun yawan afkuwar wannan matsala, wacce kuma har yanzu ta ke ci gaba afkuwa, wanda lamarin ke haddasa rasa rayukan dukkanin bangarorin biyu da haifar da dakatar da yin kiwon dabbobi da da yin noma, tare da kuma zama babbar barazana ga tsaron kasar.
Hakazalika, rikice-rikicen a tsakanin bangarorin biyu, ya fi yin kamari a yankin Nijeriya ta tsakiya, wato Middle Belt, ya kuma samo asali ne a kan batun mallakar kasar noma da albarkatun ruwa da afkuwar sauyin yanayi da yawan karuwar al’umma, tare da kuma rashin samar da kyakyawan tsari ga fannin aikin noma na kasar nan.
Cif Emeka Obegolu, shugaban cibiyar da yake bayani a kan shirin ya bayyana cewa; shirin ya kuma hada da manyan masu ruwa da tsaki da za su tattauna a kan yadda za a lalubo da mafita a rikice-rikicen da ke afkuwa a tsakanin Fulani makiyaya da kuma manoma, musamman domin ci gaba da bunkasa fannin aikin na noma a fadin kasar nan.
Ya ci gaba da cewa, manoma da Fulani makiyaya da jagororin al’umma da ‘yan kasuwa da ke hada-hadar kasuwancin amfanin gona da kuma jami’in gwamnati, za su halarci taron na tattaunawar, domin kawo karshen kalubalen da kuma tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a tsakanin bangarorin biyu
Obegolu ya danganta baje kolin, a matsayin batun baje haja, inda ya ce; taron ya kai matakin yadda kasar za ta fara yin aikin noma da kaya na zamani.
Taken taron shi ne, yin amfani da fasahar zamani, domin zuba jari a fannin fitar da kayan amfanin gona zuwa kasashen ketare tare kara habaka fannin akin noma da kuma rage asarar da ake yi, sakamakon rikice-rikicen Fulani makiyaya da kuma manoman kasar nan.
Ya ci gaba da cewa, rungumar yin noma da kayan na zamani, ciki har da yin noman rani, zai rage yawan lalacewar kasar noma a kasar nan tare da kuma magance yawan samun rikice-rikice a tsakanin Fulani makiyaya da kuma manoman kasar.















Discussion about this post