ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Tsarin Tattaunawa Don Kawo Karshen Rikicin Fulani Makiyaya Da Manoma

by Abubakar Abba
1 month ago
Manoma

Batun magance yawan samun rikici a tsakanin Fulani makiyaya a kasar nan, shi ne ya kasance kan gaba a taron masu ruwa da tsaki da masu yin dokoki da kuma masu zuba jari a kasar suka gudanar a babban birnin tarayyar Abuja.

Taron ya kunshi batun noman zamani da fitar da amfanin gona zuwa ketare na Afrika na shekarar 2026 (AGROMEKA EDPO 2026).

Taron wanda ya kasance na kwana biyu, cibiyar baje kolin kasuwanci da  masana’antu, reshen Abuja ce ta shirya shi, tare da hadaka da gonar JMT Plus.

ADVERTISEMENT

Manufar taron shi ne, domin samar da dauki wajen yin amfani da kayan zamani a fannin aikin noman kasar, tare kuma da fitar da amfanin da aka noma zuwa kasashen ketare.

Kazalika, taron ya wuce batu kan mayar da hankali a kan hada-hadar kasuwanci, amma ya bayar da damar tattaunawa a kan yadda za a kawo karshen rikice-rikicen da ke yawan afkuwa a tsakanin monoma da Fulani makiyaya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

An dai shafe shekaru da dama a kasar nan, ana samun yawan afkuwar wannan matsala, wacce kuma har yanzu ta ke ci gaba afkuwa, wanda lamarin ke haddasa rasa rayukan dukkanin bangarorin biyu da haifar da dakatar da yin kiwon dabbobi da da yin noma, tare da kuma zama babbar barazana ga tsaron kasar.

Hakazalika, rikice-rikicen a tsakanin bangarorin biyu, ya fi yin kamari a yankin Nijeriya ta tsakiya, wato Middle Belt, ya kuma samo asali ne a kan batun mallakar kasar noma da albarkatun ruwa da afkuwar sauyin yanayi da yawan karuwar al’umma, tare da kuma rashin samar da kyakyawan tsari ga fannin aikin noma na kasar nan.

Cif Emeka Obegolu, shugaban cibiyar da yake bayani a kan shirin ya bayyana cewa;  shirin ya kuma hada da manyan masu ruwa da tsaki da za su tattauna a kan yadda za a lalubo da mafita a rikice-rikicen da ke afkuwa a tsakanin Fulani makiyaya da kuma manoma, musamman domin ci gaba da bunkasa fannin aikin na noma a fadin kasar nan.

Ya ci gaba da cewa, manoma da Fulani makiyaya da jagororin al’umma da ‘yan kasuwa da ke hada-hadar kasuwancin amfanin gona da kuma jami’in gwamnati, za su halarci taron na tattaunawar, domin kawo karshen kalubalen da kuma tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a tsakanin bangarorin biyu

Obegolu ya danganta baje kolin, a matsayin batun baje haja, inda ya ce; taron ya kai matakin yadda kasar za ta fara yin aikin noma da kaya na zamani.

Taken taron shi ne, yin amfani da fasahar zamani, domin zuba jari a fannin fitar da kayan amfanin gona zuwa kasashen ketare tare kara habaka fannin akin noma da kuma rage asarar da ake yi, sakamakon rikice-rikicen Fulani makiyaya da kuma manoman kasar nan.

Ya ci gaba da cewa, rungumar yin noma da kayan na zamani, ciki har da yin noman rani, zai rage yawan lalacewar kasar noma a kasar nan tare da kuma magance yawan samun rikice-rikice a tsakanin Fulani makiyaya da kuma manoman kasar.

Manoma
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Gwamnatin Jihar Katsina Za Ta Sayar Wa Da Manoma Takin Zamani Kan Farashi Mai Rahusa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.