ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

by Leadership Hausa
7 months ago
Aiki

A kwanan baya ne, Shuagaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ya nada Manyan Hafsoshin Tsaron Kasar, inda hakan ya nuna wata alama, na kokarin da Gwamnatinsa ke kan yi, na magance kalubalen rashin tsaro, da ya yi wa kasar daurin Demon Minta.

Akasarin masu ruwa da tsaki a kasar, sun yi maraba da wannan nadin, duba da cewa, akwi matukar bukatar sojin kasr su tashi haikan, domin kawo karshen ayyukan ‘yan bindiga daji da masu sace mutane domin karbar kudin fansa da magance rikice-rikecen da suka shafia addini da ke hair da hallaka ‘yan kasar da kuma aikata, saurn manyan laifuka.

  • An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu
  • NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

A ra’ayin wannan Jaridar mun yi tuanin cewa, wannan nadin na su, ya nuna cewa, akwai jan aiki a gaban manyan hafshoshin tsaron kasar, kuma dole su tashi tsaye, domin sauke nauyin da aka dora masu.

ADVERTISEMENT

Aikin na sun a farko shi, samar da daidaito a cikin aikin na soji, musamman wajen kawar da rarrabuwar kawuna a gidan soji, wanda idan suka magance hakan, zai kara dawo da karasashin dakarun sojin da kuma kawar da duk wani banbanci, a tsakaninsu.

Muna sane da irin gagarumain namijin kokari da sadaukar da kan da dakarun ke ci gaba da yi a fagen daga, musamman domin magance kalubalen rashin tsaro da ke ci gaba da addabar kasar.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

A bisa wannan dalilin, ya kuma zama waji, manyan hafsohin tsaron su mayar da hankali, wajen ingnata jin dadi da walwalar dakarun sojin, musamman duba da cewa, manyan hafsoshin tsaron, su ba baki ne, kan wadannan kalubalen ba, domin kuwa kafin nada su, a baya an nada su kan makamai da ban da ban.

Kwarewar da kuma ilimin da suke da shi, a aikin soji, abu ne da zai taimaka masu wajen sauke nauyin da aka dora masu.

Abu na biyu shi ne, akwai bukatar a tsakaninsu, su hada karfi da karfe, domin su samu nasarar tunkarar aikin da ke a gabasu na tabbatar da tsaro a kasar, ba wai su rinka yi aiki, a daidaikunsu ba.

Kazalika, dole na rundunar sojin sama ta taimaka wa rundunar soji na kasa da kuma na ruwa, a yayin duka wani farmaki, tare da kuma yin musayar bayanai, a tsakansu.

Na ukun shi ne, dole ne su mayar da hankali kan samar dabaru, yayin gudanar da ayyukansu, musamman duba da irin sarkakiyar da ke tattare da yanayin kalubalen rashin tsaron kasar, misali duba da irin salon ayyukan ‘yan bindiga daji da masu garkuwa da mutane da kuma ayyukan ‘yan ta’adda, na kai hare –hare, wanda a yanayi irin wannan akwai matukar a dauki dabarun magance wannan barazanar ta su.

Yakar ta ‘yan bindiga daji da masu garkuwa da mutane da kuma masu aikata manyan laifuka, ya zarce ace manyan hafsoshin tsaro ne kadai za su yi hakan, domin kuwa, akwai kuma bukatar su tabbatar da sun samu goyon bayan alummar gari, musamman ta hanyar samun bayanan sirri.

Bugu da kari, na hudun shi ne, su tabbatar da dakarunsu na kai farmaki ta kasa duba da cewa, akasarin kalubalen rashin rashin tsaron ya ta’allaka ne na kasa, musamman duba da cewa maboyar ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga daji, a kan doron kasa suke.

Dole ne manyan hafsoshin tsaron su sanya a zuciyarsu na cewa, su masu yin biyayya ne, ga kundun tsarin mulkin kasar kuma dole ne su kare su tabbatar da sun kare dorewar mulkin dimokaradiyyar kasar.

Kazalika, ya zama wajbi, a tantace a tsakanin ayyukan soji na kuma na siyasa.

A saboda haka ne, ba ma goyon bayan soji yin kutse a cikin batun abinda ya shafi fanin siyasa, musamman duba da cewa, kasashen da soji suka shiga cikin lamarin siyasa, sun kasance, ba su ji dadi ba, kuma bai kamata Nijeriya ta kasance a cikin jerin irin wadannan kasashen ba.

Wannan Jaridar na shawartar ‘yan siyasar kasar nan, kar su kutsa kansu kan batun da ya shafi lamuran ayyukan sojin kasar, musamman gwamnonin jihohin kasar, musamman duba da cewa, mun lura da irin wannan shishigin na wasu ‘yan siyasar kasar inda suke bayyana gazawar da sojin kasar ke yi, na tabbatar da tsaro a kasar.

Aiki
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.