Tun daga watan Afrilu, a karkashin tunzurawar ‘yan siyasa masu tsattsauran ra’ayi, Japan ta dauki matakai masu hadari a jere, ciki har da gyara “ka’idoji uku da suka yi mata tarnakin fitar da kayan tsaro ga ketare” a hukumance, inda hakan ya ba ta izinin fitar da makamai masu kisa a ka’ida, kuma ‘yan majalisa 126 sun ziyarci haikalin Yasukuni tare, wato wurin tunawa da wadanda suka aikata laifin yaki a Japan.
A wani ci gaba kuma, a yayin babban taron jam’iyyar LDP mai mulki ta kasar Japan, firaministar kasar Takaichi Sanae ta yi kira da a kammala gyaran kundin tsarin mulki kafin babban taron jam’iyyar kasar na shekara mai zuwa.
Kara karfin soja, da gyaran kundin tsarin mulki, da ziyartar haikalin Yasukuni, duk matakai ne dake bayyana yunkurin ‘yan siyasa masu tsattsauran ra’ayi na Japan na karfafa “sabon ra’ayin nuna fin karfin soja”.
Daga yin watsi da “kare kai ” zuwa fitar da makamai masu kisa, da kuma yin watsi da kundin tsarin mulkin zaman lafiya tare da halartar bikin tunawa da wadanda suka aikata laifin yaki a fili, matakan da Japan ta dauka na jefa kasar cikin yanayi mai hadari, kuma su na kalubalantar tsarin kasa da kasa da aka kafa bayan yakin duniya na biyu.
Dole ne al’ummun kasa da kasa su farka da tunanin cewa, Japan tana kan hanyar sake komawa tsohuwar manufar soja, kuma zaman lafiya da kwanciyar hankali a Asiya, da ma duniya na fuskantar daya daga cikin wasu kalubale mafiya muni tun bayan yakin duniya na biyu.
Fin karfin soja da tada yaki ba shi ne mafita ba, kuma kaucewa alkawuran zaman lafiya zai jawo wa Japan ita kanta barna. “Munafunci dodo ya kan ci mai shi”, ‘yan siyasa masu tsattsauran ra’ayi na Japan suna wasa da wuta, kuma tabbas a karshe wuta za ta kone su. (Mai zane da rubutu: MINA)















Discussion about this post