ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jiga-jigan ‘Yan Siyasa A Kano Na Ci Gaba Da Fafatawa Don Dorewar Siyasarsu

by Yusuf Shuaibu
3 months ago

Yanayin siyasa a Jihar Kano ya shiga wani hali da ya fi tashin hankali da rashin tabbas a tarihin siyasar jihar, yayin da jiga-jigan ‘yan siyasa ke ci gaba da fafatawa don dorewar siyasarsu, wanda suke sauya sheka daga wannan jam’iyya zuwa wancan, a matsayin wata dabara na samu damar dorewar siyasa a 2027.

Abin da ya fara a matsayin kunkuri na jiga-jigan ‘yan siyasan Kano, wanda ya zama sake tsara kawance tsakanin manyan ‘yan siyasan don samun tasiri a Kano da ma kasa baki daya.

A tsakiyar wannan hadin gwiwar siyasar da ke bayyana Gwamnan Jihar Kano, Abba Yusuf da tsohon gwamnan Rabiu Kwankwaso, da tsohon mataimakin gwamna Nasiru Gawuna, mutanen nan guda uku suna da tasiri, wadanda suka sauya ra’ayinsu da ke ci gaba da sake fasalin siyasa a jihar.

ADVERTISEMENT

A cikin sauyin tsarin siyasa da ke faruwa, abin da ya fito fili shi ne, sauyin da ya jawo cece-kuce shi ne na Gwamna Yusuf, wanda ya taso a karkashin kungiyar siyasa ta Kwankwasiyya da Kwankwaso ke jagoranta, ya sake daidaita matsayinsa ta hanyar hadawa da tsarin siyasa na tsohon gwamna Abdullahi Ganduje, ta dawowarsa cikin jam’iyyar APC.

An fassara wannan mataki a matsayin yunkurin dabarun hada mulki da karfafa samun goyon bayan tarayya.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

A bangaren daya kuma, Gawuna, wanda a baya ya kasance mutum mai muhimmanci a cikin APC kuma dan takarar gwamna a 2023, ya sake tsara matsayinsa a cikin hadakar ‘yan adawa a jam’iyyar ADC. Sauyin da ya yi ana ganin shi ne a matsayin daya daga cikin manyan sauye-sauyen siyasa masu muhimmanci a tarihin Kano a baya-bayan nan.

Girgizar siyasa ta karu lokacin da Kwankwaso ya fice hukuma daga jam’iyyar NNPP kuma ya shiga ADC, wannan mataki ya haddasa girgizar siyasa a cikin tsarin jam’iyya da kuma hanyoyin kasa da aka gina a kan dogon tasirinsa.

Yayin da yake magana a lokacin rajistarsa a hukuma a gidansa, Kwankwaso ya bayyana wannan mataki a matsayin mai ciwo amma ya zama wajibi.

“Ina sanar da sauya shekata daga jam’iyyar NNPP nan take,” in ji shi. Yana kara da cewa wannan mataki ta samo asali ne daga bukatar samun hadin kan siyasa mafi fadi a cikin kasa nan.

Taron ya samu halartar shahararrun ‘yan siyasa, ciki har da Dabid Mark da Aminu Tambuwal da Rotimi Amaechi da Peter Obi, wanda ke nuna bayyana sabuwar hadin gwiwar ‘yan adawa mai fadi a cikin jam’iyyar ADC.

A tsakanin wadannan sauye-sauyen, shugaban jam’iyyar ADC na Jihar Kano, Musa Ungogo, ya ce jam’iyyar na amfani da dabaru wajen jawo hankalin sababbin mambobi da kuma kiyaye hadin kai a ciki.

A cewar Ungogo, hankalin ADC bai tsaya kan harkokin siyasa ba, yana karkata kan warware matsalolin al’umma da ci gaban tattalin arziki.

“Ba mun tsaya game da kwace mulki ba ne, har ma da yadda za a ceto mutane daga ‘yan fashi da yunwa da talauci,” in ji shi. Ya kara da cewa shigar Kwankwaso cikin jam’iyyar ta kara karfafa tsarin jam’iyyar kuma ta kara inganta kiraye-kiraye na hadin kai.

Ya bayyana cewa shugabannin jam’iyya sun yarda su yi amfani da yarjejeniya wajen zabar ‘yan takara, inda ya lura cewa irin wannan hanya zai hana rikice-rikice a ciki da kuma tabbatar da adalci kafin shekarar 2027.

Yanayin ya kara sake tsare-tsare a matakin farko. Kungiyar Kwankwasiyya, ta bakin mai magana da yawun kungiyar, Mansur Kurugu, ya tabbatar da cewa sauye shekan sun karfafa jam’iyyar ADC kuma sun kara kwarin gwiwa a tsakanin magoya baya.

Lamarin siyasar Jihar Kano ta kara rikicewa, musamman a cikin APC, biyo bayan yin murabus na mataimakin gwamna, Aminu Gwarzo, wanda ya haifar da tsananin shawarwarin siyasa da sake fitowa da muhawara kan wanda zai maye gurbinsa.

Ajiye aiki, wanda aka sanar a ranar Juma’a, 27 ga Maris, a cikin wata sanarwa biyo bayan ci gaba da shirin korar Gwarzo da majalisar dokokin Jihar Kano ta fara.

Murabus din mataimakin gwamnan ya haifar da zazzafar muhawara a tsakanin jam’iyyun siyasa da bangarorin siyasa kan wanda ya kamata ya gaje shi, tare da mabambantan muradu a cikin APC da waje suna neman samun tasiri a cikin lamarin.

Sai dai kuma, an ruwaito cewa Ganduje ya amince da Murtala Garo a matsayin mataimakin gwamna.

Wata sahihiyar majiya wanda ta nemi a sakaye sunanta, ta bayyana cewa Ganduje ya ne hakan yayin wani taro na musamman da Shugaban kasa, Bola Tinubu a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Shugaba Tinubu ya yi ganawar sirri da Ganduje da tsohon ministan tsaro, Badaru Abubakar, a taruka daban-daban a fadar shugaban kasa, wanda ake ganin wani bangare ne na ci gaba da shawarwarin siyasa a manyan jihohi kafin zaben 2027.

A cewar majiyar, Ganduje ya gabatar da Garo a matsayin abokin siyasa mai aminci tare da karfi wajen motsa mutane a matakin kasa a duk fadin Jihar Kano. Ya bayyana shi a matsayin mutum mai dogaro a cikin tsarin APC kuma wanda zai iya karfafa nasarorin siyasar jam’iyyar.

Majiyar ta ambaci tsohon gwamna yana bayyana amincewa da Garo na hada tsarin jam’iyya da kuma kirkiro goyon baya a cikin rukunoni masu muhimmanci na zabe, musamman a matakin farko, sakamakon cewa a lokuta da dama yana da tasiri a siyasar Jihar Kano.

Garo, wanda a baya ya yi aiki a matsayin kwamishina kananan hukumomi da masarautu na Jihar                    Kano a karkashin gwamnatin Ganduje, ana ganin shi a matsayin daya daga cikin kusoshi na siyasa mafi kusa ga tsohon gwamnan, tare da tasiri mai yawa a dukkanin kananan hukumomi a jihar.

Haka kuma shi ne mataimakin dan takarar gwamna na APC a zaben 2023, wanda ya yi takara da Gawuna.

Sai dai kuma ko kafin rahoton goyon bayan Ganduje, masu ruwa da tsaki na siyasa a cikin Kano ta Kudu sun fara gudanar da shawarwarin cikin gida, suna bayyana damuwa kan yin watsi da tsarin yankuna, inda suke ganin a yi la’akari da tsarin yankuna wajen zabar sabon mataimakin gwamna.

A cewar majiyar, masu ruwa da tsaki sun yi ikirarin cewa matsayin mataimakin gwamna a tarihi yana canzawa tsakanin Kano ta Arewa da Kano Tsakiya, wanda hakan ya bar Kano Kudu a baya.

Bayan matsayi na jam’iyya, masana harkokin siyasa suna cewa abubuwan da ke faruwa suna nuna sauye-sauye masu zurfi a tsarin siyasar Kano.

Wani masanin siyasa a jami’ar Bayero Kano, Kamilu Fagge, ya bayyana cewa sauye-sauyen suna faruwa ne galibi saboda son kai fiye da ra’ayin siyasa.

“Abin da muka shaida a Kano shi ne, yanayin siyasa mai juyawa inda biyayya ta zama na biyu. Babban abin da ke motsawa shi ne, tsira da burin siyasa na kashin kai,” in ji shi.

Fagge ya yi gargadin game da rikice-rikicen cikin gida a cikin APC, yana nuna cewa rukunonin da ke fafatawa da Ganduje, Barau Jibrin, da sauran sababbin masu zuwa, duk suna kokarin samun tasiri ne kafin zaben 2027.

Yayin da Jihar Kano ke kusantar shekarar 2027, jihar na ci gaba da kasancewa a cikin yanayin siyasa mai canzawa wanda aka bayyana shi da sauyin kawance, sake tsara dabaru, da karuwar gasa.

Duk da APC na nuna kwarin gwiwar samun nasara, kungiyar Kwankwasiyya tana cewa tana da rinjaye a matakin farko, kuma ADC na ci gaba da jan hankalin masu tasiri da ke neman sabbin jam’iyyar siyasa.

Abin da ke bayyana shi ne, an fara fafata siyasar 2027 a kawai a matsayin gasa don samun kuri’u ba, amma a matsayin gwagwarmaya don samun muhimmancin siyasa, tsarin mulki, da dorewar siyasa a daya daga cikin mafi karfi wuraren siyasa a Nijeriya.

Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Kafafen Yada Labarai Na Jamus Da Birtaniya: Kasar Sin Na Da Karfin Jure Mummunan Tasirin Matsalar Makamashi Ta Duniya

Kafafen Yada Labarai Na Jamus Da Birtaniya: Kasar Sin Na Da Karfin Jure Mummunan Tasirin Matsalar Makamashi Ta Duniya

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.