ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Juyin Mulki: Jami’an Sojoji 16 Za Su Fuskanci Hukuncin Kisa

by Sani Anwar
7 months ago
Kisa

Kimanin jami’an soji 16 da ake tuhuma da laifin yunKurin kifar da Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, na fuskantar hukuncin kisa ko kuma daurin rai da rai, inji rahoton jaridar Daily Trust.

Hakan na zuwa ne, bayan da babban hafsan sojin kasar ya amince cewa; jami’an da ke tsare tun a watan Oktoban 2025, an same su da aikata wannan laifi.

  • Majalisar Dattawa Ta Kai Ta’aziyya Ga Al’ummar Kurmin Wali, Ta Yi Alkawarin Kayan Agaji
  • Hotuna: Babbar Mota Ta Hallaka Wata Bafulatana A Bauchi

Jami’an soji da suka yi ritaya, wadanda suka zanta da jaridar Daily Trust a wata tattaunawa daban-daban a daren ranar Litinin, sun ce; dokar sojan Nijeriya ta tanadi hukuncin kisa, kan yunkurin juyin mulki.

ADVERTISEMENT

A watan Oktoban 2025, an samu rahotannin cewa; jami’an da suka kama daga mukamin kyaftin zuwa birgediya-Janar, hukumar leken asiri ta tsaro (DIA) ta kama tare da tsare su, sakamakon yunkurin kifar da gwamnatin Tinubu.

Jaridar ta ruwaito cewa, kwamitin da ya binciki jami’an da aka kama, ya mika wa shugaban kasa sakamakon bincikensa.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Daraktan yada labarai na tsaro, Samaila Uba, Manjo-Janar, ya kuma tabbatar da cewa; kwamitin binciken ya mika rahotonsa ga “hukumar da ta dace”.

Jami’an Da Za Su Fuskanci Hukuncin Kotun Soja

A wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin, Uba ya ce; za a gurfanar da wadanda ke da hannun da za su bayyana a gaban kwamitin shari’a na soja, domin fuskantar shari’a kamar yadda dokar Sojoji ta tanada da sauran ka’idojin da ake da su.

Ya ce, “Rundunar Sojin Nijeriya (AFN), na son sanar da jama’a cewa; an kammala bincike a kan lamarin, sannan kuma an mika rahoton ga hukumar da ta dace daidai da ka’idojin da aka tanada.

“Tsarin binciken da aka gudanar, bisa ka’idojin soji da aka kafa, ya yi nazari sosai kan duk wani yanayi da ya dabaibaye jami’an da abin ya shafa.

“Binciken ya gano jami’ai da dama da ake zargi da yunkurin kifar da gwamnati, wanda ya saba wa ka’idoji, dabi’u da kuma ka’idojin aiki da ake bukata ga mambobin AFN.

Babban jami’in sojan ya bayyana cewa, rundunar ta bayyana wannan ci gaban a bainar jama’a, domin tabbatar da bin ka’ida tare da kiyaye ka’idojin adalci da bin doka da oda.

A cewarsa, rundunar soji ta ci gaba da jajircewa wajen kiyaye mafi girman matakan kwarewa, aminci da mutunta ikon tsarin mulki.

Uba ya kara da cewa, “AFN ta sake nanata cewa; matakan da ake dauka na ladabtarwa ne kawai, kuma wani bangare ne na ci gaba da tsare-tsare, da’a da kuma ingantaccen aiki a cikin tsari.”

 

Kisa
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027:Mata Shida Da Ke Takarar Neman Shugabancin Nijeriya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Dambarwa A Kasuwancin Iyalan Indimi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Illar Shan Taba Sigari Da Dangoginta

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Next Post
Dantsoho Ya Karbi Bakuncin Babban Jami’in Ofishin Jakadanacin Daular Larabawa

Dantsoho Ya Karbi Bakuncin Babban Jami’in Ofishin Jakadanacin Daular Larabawa

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.