ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Juyin Mulki: Jami’an Sojoji 16 Za Su Fuskanci Hukuncin Kisa

by Sani Anwar
6 months ago
Kisa

Kimanin jami’an soji 16 da ake tuhuma da laifin yunKurin kifar da Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, na fuskantar hukuncin kisa ko kuma daurin rai da rai, inji rahoton jaridar Daily Trust.

Hakan na zuwa ne, bayan da babban hafsan sojin kasar ya amince cewa; jami’an da ke tsare tun a watan Oktoban 2025, an same su da aikata wannan laifi.

  • Majalisar Dattawa Ta Kai Ta’aziyya Ga Al’ummar Kurmin Wali, Ta Yi Alkawarin Kayan Agaji
  • Hotuna: Babbar Mota Ta Hallaka Wata Bafulatana A Bauchi

Jami’an soji da suka yi ritaya, wadanda suka zanta da jaridar Daily Trust a wata tattaunawa daban-daban a daren ranar Litinin, sun ce; dokar sojan Nijeriya ta tanadi hukuncin kisa, kan yunkurin juyin mulki.

ADVERTISEMENT

A watan Oktoban 2025, an samu rahotannin cewa; jami’an da suka kama daga mukamin kyaftin zuwa birgediya-Janar, hukumar leken asiri ta tsaro (DIA) ta kama tare da tsare su, sakamakon yunkurin kifar da gwamnatin Tinubu.

Jaridar ta ruwaito cewa, kwamitin da ya binciki jami’an da aka kama, ya mika wa shugaban kasa sakamakon bincikensa.

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Daraktan yada labarai na tsaro, Samaila Uba, Manjo-Janar, ya kuma tabbatar da cewa; kwamitin binciken ya mika rahotonsa ga “hukumar da ta dace”.

Jami’an Da Za Su Fuskanci Hukuncin Kotun Soja

A wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin, Uba ya ce; za a gurfanar da wadanda ke da hannun da za su bayyana a gaban kwamitin shari’a na soja, domin fuskantar shari’a kamar yadda dokar Sojoji ta tanada da sauran ka’idojin da ake da su.

Ya ce, “Rundunar Sojin Nijeriya (AFN), na son sanar da jama’a cewa; an kammala bincike a kan lamarin, sannan kuma an mika rahoton ga hukumar da ta dace daidai da ka’idojin da aka tanada.

“Tsarin binciken da aka gudanar, bisa ka’idojin soji da aka kafa, ya yi nazari sosai kan duk wani yanayi da ya dabaibaye jami’an da abin ya shafa.

“Binciken ya gano jami’ai da dama da ake zargi da yunkurin kifar da gwamnati, wanda ya saba wa ka’idoji, dabi’u da kuma ka’idojin aiki da ake bukata ga mambobin AFN.

Babban jami’in sojan ya bayyana cewa, rundunar ta bayyana wannan ci gaban a bainar jama’a, domin tabbatar da bin ka’ida tare da kiyaye ka’idojin adalci da bin doka da oda.

A cewarsa, rundunar soji ta ci gaba da jajircewa wajen kiyaye mafi girman matakan kwarewa, aminci da mutunta ikon tsarin mulki.

Uba ya kara da cewa, “AFN ta sake nanata cewa; matakan da ake dauka na ladabtarwa ne kawai, kuma wani bangare ne na ci gaba da tsare-tsare, da’a da kuma ingantaccen aiki a cikin tsari.”

 

Kisa
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

MASU ALAKA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Next Post
Dantsoho Ya Karbi Bakuncin Babban Jami’in Ofishin Jakadanacin Daular Larabawa

Dantsoho Ya Karbi Bakuncin Babban Jami’in Ofishin Jakadanacin Daular Larabawa

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.