ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Ta Kai Ta’aziyya Ga Al’ummar Kurmin Wali, Ta Yi Alkawarin Kayan Agaji

by Sulaiman and Shehu Yahaya
6 months ago
Majalisa

Majalisar Dattawan Nijeriya ta nuna damuwarta ga mutanen garin Kurmin Wali da ke Jihar Kaduna, bayan satar mutane Sama da 100, inda lamarin ya jefa wasu mazauna cikin tashin hankali.

 

Tawagar Majalisar sun kai ziyara ne karkashin jagorancin Sanatan Kaduna ta tsakiya Sanata Lawal Adamu Usman, wanda ya wakilci Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, a wani ziyara ta nuna ta’aziyya da kuma duba halin da al’umma ke ciki.

ADVERTISEMENT
  • Muhimmanci Da Amfanin Shan Rake Ga Lafiyar Dan Adam
  • Hotuna: Babbar Mota Ta Hallaka Wata Bafulatana A Bauchi

A yayin ziyarar, Sanata Lawal Adamu Usman ya isar da sakon damuwar Shugaban Majalisar kan wannan lamari, inda ya tabbatar wa mutane da shugabannin al’umma cewa Majalisar Dattawa na Nijeriya zata tallafawa al’ummar da abin ya shafa da kuma tabbatar da tsaron su. Haka kuma, ya yi alkawarin kawo kayan agaji ga wadanda abin ya shafa domin rage musu radadi.

 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

A cikin ziyarar, Sanatan ya fara ne da kai ziyara zuwa Asibitin Koyarwa na Barau Dikko, Kaduna, inda ya gana da wadanda suka ji rauni. Ya yi ta’aziyya ga wadanda suka samu rauni da iyalansu, tare da basu kalaman kwarin gwiwa da addu’o’i don samun saukin murmurewa.

 

Bayan ziyarar asibiti, Sanata Lawal Adamu Usman ya nufi Fadar Agum Adara, inda ya gana da shugabannin al’umma, ciki har da Agum Adara da Mai Unguwar Kurmin Idom. Sanatan ya yi ta’aziyya ga shugabannin gargajiya da mazauna garin kan wannan mummunan lamari, inda ya bayyana abin a matsayin abin takaici da damuwa sosai.

 

Ya kuma tabbatar da cewa Majalisar Dattawa, karkashin jagorancin Sanata Godswill Akpabio, za ta ci gaba da tattaunawa da hukumomin tsaro domin karfafa tsaro a yankin da kuma hana faruwar irin wannan lamari a nan gaba.

 

A yayin ziyarar, Agum Adara ya gode wa Majalisar Dattawa da Sanata Lawal Adamu Usman saboda nuna damuwa da al’ummar a wannan mawuyacin lokaci.

 

Ya bayyana cewa ziyarar ta kasance wata shaidar hadin kai, inda kasancewar wakilan Majalisar ta ba al’umma sabon kwarin gwiwa da tabbacin samun goyon baya.

 

Mazauna Kurmin Wali sunyi marabi da tawagar Majalisar Dattawa tare da rokon ci gaba da tallafin gwamnati, ciki har da karin jami’an tsaro da kuma kayan agaji ga wadanda abin ya shafa.

Majalisa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma
  • Sulaiman
    Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani
  • Sulaiman
    Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana
  • Sulaiman
    Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?
Majalisa
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”
Manyan Labarai

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Next Post
Za A Gudanar Da Dandalin Tattaunawa Na Masana Na Jam’iyyar JKS Da KMT A Birnin Beijing

Za A Gudanar Da Dandalin Tattaunawa Na Masana Na Jam’iyyar JKS Da KMT A Birnin Beijing

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026
Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.