ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, August 3, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Ta Kai Ta’aziyya Ga Al’ummar Kurmin Wali, Ta Yi Alkawarin Kayan Agaji

by Sulaiman and Shehu Yahaya
6 months ago
Majalisa

Majalisar Dattawan Nijeriya ta nuna damuwarta ga mutanen garin Kurmin Wali da ke Jihar Kaduna, bayan satar mutane Sama da 100, inda lamarin ya jefa wasu mazauna cikin tashin hankali.

 

Tawagar Majalisar sun kai ziyara ne karkashin jagorancin Sanatan Kaduna ta tsakiya Sanata Lawal Adamu Usman, wanda ya wakilci Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, a wani ziyara ta nuna ta’aziyya da kuma duba halin da al’umma ke ciki.

ADVERTISEMENT
  • Muhimmanci Da Amfanin Shan Rake Ga Lafiyar Dan Adam
  • Hotuna: Babbar Mota Ta Hallaka Wata Bafulatana A Bauchi

A yayin ziyarar, Sanata Lawal Adamu Usman ya isar da sakon damuwar Shugaban Majalisar kan wannan lamari, inda ya tabbatar wa mutane da shugabannin al’umma cewa Majalisar Dattawa na Nijeriya zata tallafawa al’ummar da abin ya shafa da kuma tabbatar da tsaron su. Haka kuma, ya yi alkawarin kawo kayan agaji ga wadanda abin ya shafa domin rage musu radadi.

 

LABARAI MASU NASABA

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

A cikin ziyarar, Sanatan ya fara ne da kai ziyara zuwa Asibitin Koyarwa na Barau Dikko, Kaduna, inda ya gana da wadanda suka ji rauni. Ya yi ta’aziyya ga wadanda suka samu rauni da iyalansu, tare da basu kalaman kwarin gwiwa da addu’o’i don samun saukin murmurewa.

 

Bayan ziyarar asibiti, Sanata Lawal Adamu Usman ya nufi Fadar Agum Adara, inda ya gana da shugabannin al’umma, ciki har da Agum Adara da Mai Unguwar Kurmin Idom. Sanatan ya yi ta’aziyya ga shugabannin gargajiya da mazauna garin kan wannan mummunan lamari, inda ya bayyana abin a matsayin abin takaici da damuwa sosai.

 

Ya kuma tabbatar da cewa Majalisar Dattawa, karkashin jagorancin Sanata Godswill Akpabio, za ta ci gaba da tattaunawa da hukumomin tsaro domin karfafa tsaro a yankin da kuma hana faruwar irin wannan lamari a nan gaba.

 

A yayin ziyarar, Agum Adara ya gode wa Majalisar Dattawa da Sanata Lawal Adamu Usman saboda nuna damuwa da al’ummar a wannan mawuyacin lokaci.

 

Ya bayyana cewa ziyarar ta kasance wata shaidar hadin kai, inda kasancewar wakilan Majalisar ta ba al’umma sabon kwarin gwiwa da tabbacin samun goyon baya.

 

Mazauna Kurmin Wali sunyi marabi da tawagar Majalisar Dattawa tare da rokon ci gaba da tallafin gwamnati, ciki har da karin jami’an tsaro da kuma kayan agaji ga wadanda abin ya shafa.

Majalisa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina
  • Sulaiman
    Iran Ta Musanta Iƙirarin Trump Kan Sabbin Tattaunawa da Amurka
  • Sulaiman
    ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara
  • Sulaiman
    Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga
Majalisa
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Rashin Tsaro: ACI Zata Kira Taron Gaggawa Na Masu Ruwa Da Tsaki A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    2027: Ƙungiyar Musulman Kudancin Kaduna Ta Yi Gargaɗi Kan Siyasantar Da Addini
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Jinin Waɗanda Aka Kashe Wajen Haƙar Ma’adanai a Birnin Gwari Ba Zai Tafi Banza Ba – Hon. Bashir Zubairu
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

MASU ALAKA

DSS
Manyan Labarai

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

August 3, 2026
Zamfara
Labarai

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

August 3, 2026
Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

August 3, 2026
Next Post
Za A Gudanar Da Dandalin Tattaunawa Na Masana Na Jam’iyyar JKS Da KMT A Birnin Beijing

Za A Gudanar Da Dandalin Tattaunawa Na Masana Na Jam’iyyar JKS Da KMT A Birnin Beijing

LABARAI MASU NASABA

DSS

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

August 3, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Musanta Iƙirarin Trump Kan Sabbin Tattaunawa da Amurka

August 3, 2026
Zamfara

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

August 3, 2026
Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

August 3, 2026
Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

August 3, 2026
Majalisa

WAFCON 2026: Ƴan Wasan Nijeriya 2 Ba Zasu Buga Wasan Ƙarshe Na Rukunin C Ba

August 2, 2026
Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

August 2, 2026
Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

August 2, 2026
Majalisa

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Ceto Mutane 9 A Zamfara

August 2, 2026
Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

August 2, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.