ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dantsoho Ya Karbi Bakuncin Babban Jami’in Ofishin Jakadanacin Daular Larabawa

by Bello Hamza
5 months ago
NPA

Shugaban Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa na Kasa Dakta Abubakar Dantsoho, ya karbi bakuncin Babban Jami’i na Ofishin Jakadanacin Daular Larbawa wato UAE, da ke a Nijeriya Salem Al-Jaberi.

Dantsho, ya karbi bakuncinsa ne, a Shalkawar Hukumar NPA, da ke  a Marina, a jihar Lagos.

  • Cinikayyar Waje Ta Jihar Xinjiang Ta Bunkasa A Shekarar 2025
  • Binciken CGTN: Tsarin Diflomasiyyar Amurka Na Babakere Ya Tada Hankula Kan Jagorancin Duniya

Wannnan na daga cikin halartar da Nijeriya ta yi, a wani babban taro, da aka kammala a kwanan baya, a kasar Abu Dhabi, ta ci gaba da kulla alakar fadada bunkasa hada-hadar kasuwanci, a tsakanin kasashen biyu, musamman kan kayana da basu shafi, fannin Man Fetur ba da kara bunkasa fannin Tashoshin Jiragen Ruwa.

ADVERTISEMENT

Kazalika, ganawar ta su, na zuwa ne, bayan rattaba hannun yarjejeniya a tsakanin Ministan Bunkasa Tattalin Arziki na Teku,  Adegboyega Oyetola, da aka yi, a tsakanin Nijeriya, a kasar ta Abu Dhabi.

Bugu ka kari, manufar itace, domin a kirkiro da dabaru ta hanyar yin hadaka domin kara habaka fannin Tashoshin Jiragen Ruwa da safarar kaya, ta hanyar yin amfani da kimiyyar zamani.

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

A jawabinsa, yayin tattataunawar, Dakta Dantsoho ya bayyana cewa, bisa umarnin Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da kuma Ministan Ministan Bunkasa Tattalin Arziki na Teku,  Adegboyega Oyetola, Hukumar ta NPA, ta himmatu matuka, wajen ganin ana ci gaba da hada karfi da karfe da  kasar ta Abu Dhabi, domin kara fadada yawan hada-hadar kasuwanci, musamman a bangare, da bai shafi fannin Mai ba.

“Bisa umarnin  umarnin Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da kuma Ministan Ministan Bunkasa Tattalin Arziki na Teku,  Adegboyega Oyetola, muna ci gaba da mayar da hankali, wajen ganin ana ci gaba da hada karfi da karfe da  kasar ta Abu Dhabi, domin kara fadada yawan hada-hadar kasuwanci, musamman a bangare, da bai shafi fannin Mai ba, Inji Dantsoho.

A na sa jawabin Babban Jami’i na Ofishin Jakadanacin Daular Larbawa wato UAE Salem Al-Jaberi, kasancewar Nijeriya da kasar ta Abu Dhabi, abokan hadaka ne, ya sanar da cewa, kasar sa, a shirye take, ta kara karfafa hadaka, da Nijeriya.

“Nijeriya da Abu Dhabi, sun jima a matsayin abokan hadaka, a saboda haka, mu a Abu Dhabi, a shirye muke domin mu kara rubanya hadakar hada-hadar kasuwanci, da Nijeriya, ako da yaushe,” A cewarsa.

Ganawar, ta kuma samu halartar Manyan Daraktoci na Hukumar NPA, da suka hada da, Madam  Bibian Richard-Edet, da ke a sashen kudi da tafiyarda harkar mulki, sai Injiya Ibrahim Abba Umar, na sahsne kula da kere-kere da Injiya   Olalekan Badmus, na sashen gudanawa na Sufurin Jiragen Ruwa a NPA.

Tattaunawar, ta kuma mayar da hankali, kan yadda kasashen biyu, za su amfana da juna,  kan bunkasa hada-hadar kasuwanci da samar da damar zuba jari a tsakanin Nijeriya da Daular ta Larabawa.

Kazalika, sun cimma matsayar jadda kara karkafa bunkasa fannin Sufurin Jiragen Ruwa na kasashen biyu da safarar kaya wanda hakan zai sanya, kasashen biyu, su kara bunkasa tatalin arzikinsu.

NPA
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Next Post
Yadda Buƙatun Kwankwaso Suka Tarwatsa Yiwuwar Haɗin Gwuiwa Da APC

Yadda Buƙatun Kwankwaso Suka Tarwatsa Yiwuwar Haɗin Gwuiwa Da APC

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.