Gwamnatin Jihar Kaduna ta sake jaddada kudirinta na tabbatar da cewa duk wani yaro da ya kai shekarun zuwa makaranta, zai samu ingantaccen ilimi kyauta, tana mai bayyana ilimi a matsayin hakki na asali, ba wata dama ce ta musamman ga wasu ba.
Shugaban Hukumar Ilimin Bai-daya ta Jihar Kaduna (SUBEB), Malam Mubarak Mohammed, ne ya bayyana hakan ranar Laraba yayin yakin wayar da kan jama’a kan shirin sanya yara makaranta na shekarar 2026/2027, wanda aka gudanar a kasuwar Sheikh Abubakar Gumi da ke Kaduna.
Malam Mohammed, wanda ya yi jawabi ga mazauna yankin da masu ruwa da tsaki a yayin yakin neman sanya yara makaranta, ya ce gwamnatin Gwamna Uba Sani ta kuduri aniyar tabbatar da cewa babu wani yaro da ya kai shekarun makaranta da za a hana shi damar samun ilimin bai-daya.
Ya bayyana damuwa kan yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a Arewacin Nijeriya, sai dai ya ce Jihar Kaduna ta samu gagarumin ci gaba wajen magance wannan matsala ta hanyar ci gaba da sanya hannun gwamnati da daukar matakan da suka dace.
Malam Mohammed ya bukaci iyaye da masu kula da yara da su tabbatar da cewa sun sanya yaran da suka kai shekarun makaranta a makarantu, domin su amfana da damar samun ilimi tare da samun makoma mai kyau.














