ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Tuhumar Mutum Biyu Kan Dala 461,600 Da Suka Yi Ɓatan Dabo A Filin Jirgin Saman Kano

by Rabi'u Ali Indabawa
2 weeks ago

Hukumar EFCC ta fara bincike kan wasu maza biyu, Jamilu Shuaibu Waya da Usman Namadi, bisa zargin rashin bayyana jimillar Dala 461,600 a Filin Jirgin Sama na Malam Aminu Kano da ke Jihar Kano.

Mai magana da yawun hukumar EFCC ya bayyana a wata sanarwa ranar Litinin cewa an kama waɗanda ake zargin ne a ranar Juma’a, 8 ga Mayun 2026, bayan sun iso Nijeriya daga Dubai cikin jirgin Ethiopian Airlines ET941.

Rahoton ya ce jami’an Kwastom shiyyar Kano/Jigawa ne suka tare su yayin binciken bayyana kuɗaɗen waje da ake gudanarwa a filin jirgin.

ADVERTISEMENT

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta bayyana cewa da farko waɗanda ake zargin sun bayyana Dala 130,000 da kuma Dala 180,000 bi da bi a wajen rajistar bayyana kuɗaɗe.

Sai dai bayan ƙarin bincike da jami’an kwastam suka gudanar, an gano wasu ƙarin kuɗaɗe da ba a bayyana ba da aka ɓoye a jikinsu.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi

NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano

Hukumar ta ce an gano ƙarin Dala 120,000 a wajen wanda ake zargi na farko, wanda ya sa jimillar kuɗin da ke hannunsa ta kai Dala 250,000, yayin da aka gano ƙarin Dala 31,600 a wajen na biyun, wanda ya sa jimillar kuɗinsa ta kai Dala 211,600.

Rahoton ya ce kuɗaɗen da ba a bayyana ba sun saɓa wa sashe na 3 da na 4 na dokar hana safarar kuɗaɗe ta haramtacciyar hanya ta shekarar 2022.

Da yake jawabi yayin miƙa waɗanda ake zargin ga EFCC, muƙaddashin Kwanturola na Kwastam na yankin, Mataimakin Kwanturola UU Adamu, ya yaba da haɗin gwiwar da ke tsakanin Hukumar Kwastam da EFCC wajen yaƙi da laifukan kuɗi da safarar kuɗaɗe ba bisa ƙa’ida ba a ƙasar nan.

Adamu ya ce: “Bari na nuna godiya bisa ci gaba da haɗin gwiwa da Daraktan EFCC na shiyyar Kano saboda goyon bayan da suke bayarwa wajen cimma manufofinmu na yaƙi da safarar kuɗaɗe ba bisa ƙa’ida ba.”

Daraktan EFCC na shiyyar Kano, Mataimakin Kwamandan EFCC, ACE1 Friday S. Ebelo, ya tabbatar wa Hukumar Kwastam cewa za su gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

“EFCC za ta gudanar da cikakken bincike ba tare da sassauci ba a kan wannan batu. Za mu gurfanar da lamarin yadda ya kamata domin tabbatar da cewa masu karya dokokin hana safarar kuɗaɗe sun fuskanci hukunci yadda ya dace,” in ji Ebelo.

Ya kuma yaba wa Hukumar Kwastam bisa ci gaba da haɗin gwiwa da EFCC, yana mai cewa haɗin kai tsakanin hukumomi na da muhimmanci wajen yaƙi da laifukan kuɗi.

Ebelo ya ƙara da cewa haɗin gwiwar tsakanin hukumomin biyu na ƙara ƙarfafa ƙoƙarin da ake yi wajen daƙile safarar kuɗaɗe ba bisa ƙa’ida ba a kan iyakokin Nijeriya.

Bayan miƙa waɗanda ake zargin a hukumance, an kai su tare da kuɗaɗen da aka ƙwato da sauran kayayyakin shaida zuwa ofishin EFCC na shiyyar Kano, inda ake ci gaba da bincike.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi

June 1, 2026
NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
Tsaro

NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano

May 31, 2026
Yadda Muka Kashe Masu Garkuwa 4 Da Suke Shirin Kai Hari Kan Attajirai A Legas —CP
Tsaro

Yadda Muka Kashe Masu Garkuwa 4 Da Suke Shirin Kai Hari Kan Attajirai A Legas —CP

May 31, 2026
Next Post
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya

An Kama ‘Yan Nijeriya Huɗu A Indiya Bisa Zargin Damfara Ta Intanet

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.