Hukumar EFCC ta fara bincike kan wasu maza biyu, Jamilu Shuaibu Waya da Usman Namadi, bisa zargin rashin bayyana jimillar Dala 461,600 a Filin Jirgin Sama na Malam Aminu Kano da ke Jihar Kano.
Mai magana da yawun hukumar EFCC ya bayyana a wata sanarwa ranar Litinin cewa an kama waɗanda ake zargin ne a ranar Juma’a, 8 ga Mayun 2026, bayan sun iso Nijeriya daga Dubai cikin jirgin Ethiopian Airlines ET941.
Rahoton ya ce jami’an Kwastom shiyyar Kano/Jigawa ne suka tare su yayin binciken bayyana kuɗaɗen waje da ake gudanarwa a filin jirgin.
Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta bayyana cewa da farko waɗanda ake zargin sun bayyana Dala 130,000 da kuma Dala 180,000 bi da bi a wajen rajistar bayyana kuɗaɗe.
Sai dai bayan ƙarin bincike da jami’an kwastam suka gudanar, an gano wasu ƙarin kuɗaɗe da ba a bayyana ba da aka ɓoye a jikinsu.
Hukumar ta ce an gano ƙarin Dala 120,000 a wajen wanda ake zargi na farko, wanda ya sa jimillar kuɗin da ke hannunsa ta kai Dala 250,000, yayin da aka gano ƙarin Dala 31,600 a wajen na biyun, wanda ya sa jimillar kuɗinsa ta kai Dala 211,600.
Rahoton ya ce kuɗaɗen da ba a bayyana ba sun saɓa wa sashe na 3 da na 4 na dokar hana safarar kuɗaɗe ta haramtacciyar hanya ta shekarar 2022.
Da yake jawabi yayin miƙa waɗanda ake zargin ga EFCC, muƙaddashin Kwanturola na Kwastam na yankin, Mataimakin Kwanturola UU Adamu, ya yaba da haɗin gwiwar da ke tsakanin Hukumar Kwastam da EFCC wajen yaƙi da laifukan kuɗi da safarar kuɗaɗe ba bisa ƙa’ida ba a ƙasar nan.
Adamu ya ce: “Bari na nuna godiya bisa ci gaba da haɗin gwiwa da Daraktan EFCC na shiyyar Kano saboda goyon bayan da suke bayarwa wajen cimma manufofinmu na yaƙi da safarar kuɗaɗe ba bisa ƙa’ida ba.”
Daraktan EFCC na shiyyar Kano, Mataimakin Kwamandan EFCC, ACE1 Friday S. Ebelo, ya tabbatar wa Hukumar Kwastam cewa za su gudanar da cikakken bincike kan lamarin.
“EFCC za ta gudanar da cikakken bincike ba tare da sassauci ba a kan wannan batu. Za mu gurfanar da lamarin yadda ya kamata domin tabbatar da cewa masu karya dokokin hana safarar kuɗaɗe sun fuskanci hukunci yadda ya dace,” in ji Ebelo.
Ya kuma yaba wa Hukumar Kwastam bisa ci gaba da haɗin gwiwa da EFCC, yana mai cewa haɗin kai tsakanin hukumomi na da muhimmanci wajen yaƙi da laifukan kuɗi.
Ebelo ya ƙara da cewa haɗin gwiwar tsakanin hukumomin biyu na ƙara ƙarfafa ƙoƙarin da ake yi wajen daƙile safarar kuɗaɗe ba bisa ƙa’ida ba a kan iyakokin Nijeriya.
Bayan miƙa waɗanda ake zargin a hukumance, an kai su tare da kuɗaɗen da aka ƙwato da sauran kayayyakin shaida zuwa ofishin EFCC na shiyyar Kano, inda ake ci gaba da bincike.















Discussion about this post