ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Tuhumar Mutum Biyu Kan Dala 461,600 Da Suka Yi Ɓatan Dabo A Filin Jirgin Saman Kano

by Rabi'u Ali Indabawa
1 month ago

Hukumar EFCC ta fara bincike kan wasu maza biyu, Jamilu Shuaibu Waya da Usman Namadi, bisa zargin rashin bayyana jimillar Dala 461,600 a Filin Jirgin Sama na Malam Aminu Kano da ke Jihar Kano.

Mai magana da yawun hukumar EFCC ya bayyana a wata sanarwa ranar Litinin cewa an kama waɗanda ake zargin ne a ranar Juma’a, 8 ga Mayun 2026, bayan sun iso Nijeriya daga Dubai cikin jirgin Ethiopian Airlines ET941.

Rahoton ya ce jami’an Kwastom shiyyar Kano/Jigawa ne suka tare su yayin binciken bayyana kuɗaɗen waje da ake gudanarwa a filin jirgin.

ADVERTISEMENT

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta bayyana cewa da farko waɗanda ake zargin sun bayyana Dala 130,000 da kuma Dala 180,000 bi da bi a wajen rajistar bayyana kuɗaɗe.

Sai dai bayan ƙarin bincike da jami’an kwastam suka gudanar, an gano wasu ƙarin kuɗaɗe da ba a bayyana ba da aka ɓoye a jikinsu.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

Hukumar ta ce an gano ƙarin Dala 120,000 a wajen wanda ake zargi na farko, wanda ya sa jimillar kuɗin da ke hannunsa ta kai Dala 250,000, yayin da aka gano ƙarin Dala 31,600 a wajen na biyun, wanda ya sa jimillar kuɗinsa ta kai Dala 211,600.

Rahoton ya ce kuɗaɗen da ba a bayyana ba sun saɓa wa sashe na 3 da na 4 na dokar hana safarar kuɗaɗe ta haramtacciyar hanya ta shekarar 2022.

Da yake jawabi yayin miƙa waɗanda ake zargin ga EFCC, muƙaddashin Kwanturola na Kwastam na yankin, Mataimakin Kwanturola UU Adamu, ya yaba da haɗin gwiwar da ke tsakanin Hukumar Kwastam da EFCC wajen yaƙi da laifukan kuɗi da safarar kuɗaɗe ba bisa ƙa’ida ba a ƙasar nan.

Adamu ya ce: “Bari na nuna godiya bisa ci gaba da haɗin gwiwa da Daraktan EFCC na shiyyar Kano saboda goyon bayan da suke bayarwa wajen cimma manufofinmu na yaƙi da safarar kuɗaɗe ba bisa ƙa’ida ba.”

Daraktan EFCC na shiyyar Kano, Mataimakin Kwamandan EFCC, ACE1 Friday S. Ebelo, ya tabbatar wa Hukumar Kwastam cewa za su gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

“EFCC za ta gudanar da cikakken bincike ba tare da sassauci ba a kan wannan batu. Za mu gurfanar da lamarin yadda ya kamata domin tabbatar da cewa masu karya dokokin hana safarar kuɗaɗe sun fuskanci hukunci yadda ya dace,” in ji Ebelo.

Ya kuma yaba wa Hukumar Kwastam bisa ci gaba da haɗin gwiwa da EFCC, yana mai cewa haɗin kai tsakanin hukumomi na da muhimmanci wajen yaƙi da laifukan kuɗi.

Ebelo ya ƙara da cewa haɗin gwiwar tsakanin hukumomin biyu na ƙara ƙarfafa ƙoƙarin da ake yi wajen daƙile safarar kuɗaɗe ba bisa ƙa’ida ba a kan iyakokin Nijeriya.

Bayan miƙa waɗanda ake zargin a hukumance, an kai su tare da kuɗaɗen da aka ƙwato da sauran kayayyakin shaida zuwa ofishin EFCC na shiyyar Kano, inda ake ci gaba da bincike.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi
Tsaro

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

June 19, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Manyan Labarai

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

June 17, 2026
Next Post
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya

An Kama ‘Yan Nijeriya Huɗu A Indiya Bisa Zargin Damfara Ta Intanet

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026
Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

June 23, 2026
'Yan Bindiga

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.