ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ka’idojin Mu’amala Da Mutane Guda (2)

Ka Ba Wa Mutane, Amma Karka Nema Daga Wajansu

by Dakta Jamil Zarewa
4 years ago
Mu'amala

Annabi tsira da amincin Allaah sutabbata agate shi yana cewa: “kuyiwa juna kyauta za’a so ku”, mutane suna son wanda zai basu abin dunia, wannan ya sa Allaah ya shar’anta bada zakka ga wanda ake fatan shigarsa Musulinci, kamar yadda ya zo a suratu Attaubah, Manzon tsira ya bawa wasu dukia don su tabbata a Musulinci, Imaaninsu ya inganta.

Duk mai kudin da yakeyiwa mutane kyauta dawuya suyi masa hassada, kullum za su dinga murna da ganinsa, suna masa fatan alkhairi.

  • Yaya Matsayin Tsotson Farjin Mace Yayin Saduwa A Musulunci? (Fatawa)

Idan muka duba suratun Namli zamu ga lokacin da Alhud-huda ya jefawa Bilkisu Sarauniyar sabi’i wasika wacce ta kunshi wajabcin mika wuya ga Annabi Sulaiman, ta shawarci mutananta game da matakin da ya kamata a dauka, sun bata shawarar ayi amfani da karfi, amma ita kuma sai ta ce zata aikawa da shugaba sulaiman kyauta, saboda ta San kyauta tana sanyaya zukata, ta kuma kusanto sa da kusa.

ADVERTISEMENT

Annabi tsira da aminchin Allaah su tabbata a gare shi yana cewa: “Nakasance cikin bukatar dan ‘uwana shi yafi mini alkhairi fiye da na yi’itikafi a wannan masallacin nawa.”
Sai dai duk haka Allaah yayi dan’Adam da son dukia, wannan ya sa baya iya jure roko, in muka duba Al-kur’ani ko Allaah in zai tambayi zakka ko sadaka yakan gorantawa mutane, a cikin suratun Nuur “Kuma kubasu daga dukiar da Allaah yaba ku” a suratun Nisa’i yace ;

“Kuma an sanyawa zucia kwauro” Idan zai bi muminai yakan ce, kuma suna ciyarwa daga abin da muka azurta su.
“Dayanku yayi sammako ya yo icce a bayansa, ya yi sadaka da shi ya kuma wadatu daga mutane, shiyafi masa daya tambayi wani mutum ya ba shi ko ya hana shi, hannun dayake bayarwa yafi hannun da yake amsa, ka fara da wanda kake daukar nauyi.” Duk wanda yakeson zaman lpia toh karya yadinga rokon mutane wani abu, wani mawakin larabawa yana cewa; “Allaah yana fushi idan kadaina rokon sa, shi kuma dan’Adam lokacin da kake rokonsa yake fushi.”

LABARAI MASU NASABA

Falalar Haɗa Basmala da Suratul Fatiha

Falalar Neman Tsari Daga Sharrin Shaidan

Annabi tsira da amincin Allaah su tabbata agare shi yayi alkawari da wasu daga cikin sahabbansa karsu roki kowa wani abu, don haka bulalar daya daga cikinsu takan fadi yana kan abin hawansa amma bazai ce amiko masa ba, sai dai ya sauko da kansa ya dauka. Yawancin yan’Adama basa son bambadanci, an ruwaito hadisi cewa ; “In kanason mutane su so ka, toh ka guji abin da yake hannunsu” wani Balarabe yana cewa ; “Idan za’a tambayi mutane tur6aya, su durkusa su ya fito su baka, da sunce bazasu bada ba, Muhammadul Amin Ash-Sahankidi wanda ya rasu a shekara ta 1393 H yan cewa: “Nazo da wata taska daga wadda da wuya ka samu wanda yake da irinta, ita ce :dangana da wadatar Zuci” Haka haka malami magabata suke.

Ada’u dan abi Rabah- daya daga cikin malamai magabata nagari -bawa ne aka ‘yanta shi, Baki ne, ana cewa yana da siffofi na muni, yana da shanyayyen hannu, yana da cin zan-zana, amma lokacin da suka hadu da sulaiman Bn Abdil-Malik daya daga cikin halifofin daular Umawiyya wanda yaga mahaifinsa a shekara ta 99, kuma a shekarar ya mutu, ya hadu da Ada Bin Abi Rabah a harami, sai ya ce masa: “Malam ka tambayeni duk abinda kake so” sai Ada’u ya ce; “Dan jirani, Inaso zanje nayi dawafi”, yajira shi yaje yayi dawafi ya fito. dayafito sai yasake maimata masa tambayar: “Ka tambaye ni duk abinda ka keso.” Sai yace masa “Wallahi har nashiga na fito ban roki Allaah ko abu daya na dunia ba, don haka kaima bazan tambaye ka ba.”

Haka Hisham Bin Abdil-Malik, shi ma daya ne daga cikin halifofin Daular Umawiyya, sun hadu da Bajimin malami Salim dan Abdallah dan Umar a masallaci, ya ce masa: “Allaah ya gafarta Malam, in kana da bukata ka tambaya a yi maka.” Sai yace; “Wallahi ina jin kunyar na tambayi wanda ba Allaah ba a masallaci” saboda haka bayan an gama sallah sai ya fita waje ya jira shi a wajen masallaci.

Da suka fito sai ya sake maimata masa waccar maganar a wajen masallaci, ya ce : “Duk abin da kake so ka fada a maka” sai ya ce masa: “Har nagama nafito daga masallacin ban roki Allaah komai na dunia ba, saboda haka tunda ban roki Allaah ba, kai ma bazan rokeka ba.”

Haruna Ar-rashid wani lokaci ya gama aikin hajji, sai ya ce a dan zagaya da shi wajen malamai su yi masa wa’azi, duk malamin da ya je gurinsa sai ya tambaye shi: ana bin ka bashi? Sai ya ce: “EH”, sai a dau jakar kudi a ba shi, har suka je gurin Fudhail Bin Eyadh ya ce ya masa wa’azi, sai ya yi masa wa’azi mai shiga jiki. Sai ya fashe da kuka, yayi ta ruri.

Bayan ya gama sai ya ce da Fudhail dan Eyadh: “Ko ana bin ka bashi? Sai Fudhail Bin Eyadh ya ce: “Eh, akwai bashin da ake bi na in za ka iya biya, akwai bashin da na dauko a gurin Allaah na farillai da sunnoni, su ne ba na iya biyan su yadda ya kamata, idan za ka iya biya sai ka biya min”, ya shiga cikin gida yayi ta kuka. Baiwarsa ta ce: Ina ma ka dan kar6i wani abu, tunda Muna cikin talauci, ka gazai taimaka mana.

Ya yi ta rusa ruri, ita da kanta ta fito waje ta ce da Haruna Ar-rashid: “Don Allaah ka tafi, saboda ka cutar da bawan Allaah nan. A lokacin fa shi Haruna Ar-rashid shine shugaban duniar musulmai baki daya.
Mawallafi: Dr Jamilu Yusuf Zarewa
Bita: Dr Abdul-kadir Isma’il, Bayero Unibersity kano

Mu'amala
Dakta Jamil Zarewa
+ postsBio
  • Dakta Jamil Zarewa
    https://hausa.leadership.ng/author/dakta-jamil-zarewa/
    Zan Iya Cin Bashin Banki Na Biya Aikin Hajji?
  • Dakta Jamil Zarewa
    https://hausa.leadership.ng/author/dakta-jamil-zarewa/
    Mene Ne Hukuncin Koyon Ilimin Taurari A Shari’a?
  • Dakta Jamil Zarewa
    https://hausa.leadership.ng/author/dakta-jamil-zarewa/
    Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?
  • Dakta Jamil Zarewa
    https://hausa.leadership.ng/author/dakta-jamil-zarewa/
    Idan Mace Ta Yi Barin Cikin Wata Biyu, Za Ta Dakatar Da Yin Sallah?

MASU ALAKA

Manzon Allah
Dausayin Musulunci

Falalar Haɗa Basmala da Suratul Fatiha

June 19, 2026
Falalar Neman Tsari Daga Sharrin Shaidan
Dausayin Musulunci

Falalar Neman Tsari Daga Sharrin Shaidan

June 12, 2026
Bukatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
Dausayin Musulunci

Bukatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

June 5, 2026
Next Post
2023: “Atiku Zai Lashe Zabensa A Zagayen Farko”, Martanin PDP Ga INEC

“Zamu Kare Kanmu Daga Barazanar Kawo Mana Farmaki A Jihar Ribas” —Magoya Bayan Atiku

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.