Kamfanin Simintin Dangote, reshen Obajana, ya ƙara faɗaɗa ayyukan tallafinsa ga al’umma ta hanyar raba kayayyakin karatu ga ɗalibai a Lakwaja, babban birnin Jihar Kogi.
Babban Manajan Sashen Harkokin Jin Daɗin Al’umma na Dangote Cement, reshen Obajana, Ademola Adeyemi, ya bayyana cewa wannan wani ɓangare ne na shirye-shiryen alhakin zamantakewa na kamfanin (CSR).
A cewarsa, wannan tallafin ilimi da aka kai Lokoja ya biyo bayan irin wannan rabon kayayyakin karatu da kamfanin ya yi wa ɗaliban makarantun gwamnati a al’ummomin Oyo, Iwaa, Obajana da Apata. Haka kuma, kamfanin ya ƙaddamar da wani asibiti na miliyoyin naira a Obajana, wanda ya ƙara wa jerin ayyukan ci gaban al’umma da suka haɗa da asibitocin da aka gina a al’ummomin Iwaa da Oyo.
Ya ce tsawon shekaru, kamfanin ya zuba biliyoyin Naira wajen aiwatar da shirye-shiryen ci gaban al’ummomin da ke karɓar baƙuncinsa, ciki har da shirye-shiryen ƙarfafa tattalin arziki, gina hanyoyi da samar da ruwan sha mai tsafta. Ya kuma jaddada cewa kamfanin zai ci gaba da faɗaɗa irin waɗannan ayyuka.
Adeyemi ya ƙara da cewa shirye-shiryen kula da alhakin zamantakewa na kamfanin suna tafiya da manufofin gwamnati na ci gaba, kuma ana aiwatar da su ne ta hanyar haɗin gwiwa mai ɗorewa da amfani ga ɓangarorin biyu.
A cikin wata sanarwa da kamfanin ya fitar kuma aka raba wa manema labarai a Lokwaja, an bayyana cewa kayayyakin karatun da aka raba sun haɗa da jakunkunan makaranta, littattafan rubutu, kayan rubutu, kwalaben ruwa da sauran muhimman kayan koyo domin inganta karatun ɗalibai da kuma shirya su domin shiga sabon zangon karatu.
Sanarwar ta ce wannan tallafin ya biyo bayan binciken tantance buƙatun da Kamfanin Simintin Dangote ya gudanar, inda aka gano cewa ɗalibai da dama suna zuwa makaranta ba tare da jakunkunan makaranta ba, yayin da wasu kuma ke ɗaukar littattafansu a hannu. Haka kuma an gano cewa ɗalibai da dama ba su da muhimman kayan koyo kamar littattafan rubutu, alƙaluma, fensir da sauran kayan karatu na yau da kullum.
Da yake jawabi, Babban Malamin Makarantar UBE LGEA School, St. Luke Model II, Adankolo, a Ƙaramar Hukumar Lakwaja, Abubakar Sanni, ya nuna matuƙar godiyarsa ga mahukuntan Kamfanin Simintin Dangote bisa wannan tallafi.
Ya kuma gode wa Shugaban Rukunin Kamfanonin Dangote, Aliko Dangote, saboda faɗaɗa shirin tallafin ilimi na kamfanin har zuwa makarantun da ke babban birnin jihar, ba tare da taƙaita shi ga al’ummomin da kamfanin ke gudanar da ayyukansa kaɗai ba.
Waɗanda suka amfana da tallafin, shugabannin makarantu, iyaye da sauran masu ruwa da tsaki a al’umma sun bayyana godiyarsu ga Kamfanin Simintin Dangote bisa wannan taimako da ya zo a kan lokaci, tare da yi wa kamfanin addu’ar samun ci gaba da nasara a ƙoƙarinsa na inganta rayuwar al’umma da tallafa wa ci gaba mai ɗorewa.














