A kalla kananan yara 469 suka mutu sanadiyar rashin ko karancin abinci mai gina jiki tsakanin watannin Janairu da Yuli na, 2025, a Jihar Kano, yayin da kashi 51.9 na yaran da basu samu girma ba kamar yadda ya dace.
Kamar yadda Farfesa Rukayya Aliyu Yusuf ta sashen labarai da harkokin da suka shafe su,ta Jami’ar Bayero ta Kano (BUK), ta bayyana a wata kasidar da ta gabatar mai taken,: “Gane dalilan da suka sa ake samun sauyin halaye: Hanyar da za’a inganta lamarin daya shafi abinda ya shafi abincin yara a Kano”, a wani horo na wayar da kan mahalarta.
- Gwamnatin Tarayya Ta Biya ‘Yan Wasan Super Eagles Haƙƙoƙinsu
- Kasar Sin Ta Ce Wajibi Ne A Kare Halastattun Muradunta A Venezuela
Shugabar ta ce kashi 40 na kananan yaran da basu kai shekara 5 ba, basu girma kamar yadda ya dace, kusan kashi 51.9 ne a Kano , kamar yadda rahoton UNICEF na 2025 ya bayyana.
Da take nuna rashin jin dadinta kan lamarin,Malamar ta ce, “Shi lamarin rashin abinci mai inganci hakan yana faruwa ne saboda fatara, rashin abinci, rashin abinci mai inganci da tsafta.”
Masaniyar kimiyyar abinci, Amina Ado Yahaya, ta ce Kano ita ce ke da yawan yaran da basu kai shekara 5 biyar ba, da kashi 42.6, wani yanayin da yake bukatar tallafi na gida kamar lambun gida da za’a rika shuka ganyayen da za su taimaka wajen samun abinci mai inganci.
Ta bayyana cewa rashin sinadarin Bitamin A yana sa kananan yara rika makancewa, ga kuma yiyuwar kamuwa da cutar bakon dauro da kuma gudawa.















Discussion about this post