• English
  • Business News
Thursday, July 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kare Mafi Alkawari A Duniya Ya Cika Shekara 100

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
Kare Mafi Alkawari A Duniya Ya Cika Shekara 100
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Taken fim din da aka yi bisa dogaro da labarin karen shi ne: ” Zan jira ka komai tsawon lokaci.”

Labari ne na Hachiko, wani kare da ya kwashe shekaru yana jiran dawowar maigidansa.

  • Kiwon Lafiya: Yadda Dabi’un Ko-in-kula Ke Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke (II)

Karen mai launin fari, wanda aka haifa shekaru 100 da suka gabata, an yi fina-finai da rubuce-rubuce don bayar da labarinsa wanda ya kunshi al`adun al`ummar Chaina, a shekara ta 1987, an yi wani fim sannan a shekara ta 2009 jarumi Richard Gere ya fito a jigon wani fim da ya yi fice mai dauke da labarin Hachiko.

Akwai wasu labarun na karnukan da suka yi abubuwan al`ajabi da sadaukarwa ga iyayen gidansu, kamar karen nan mai suna Greyfriars Bobby to amma babu karen da labarinsa ya shahara a duniya kamar Hachiko.

An girke mutum-mutumin Hachinko na tagulla a kofar tashar Shibuya da ke Tokyo, inda karen ya yi zaman jiran Ubangidansa na tsawon lokaci.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Bai TaÉ“a Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista

Har Yanzu A Cikin PDP Nake, Ba Zan Koma APC Ko ADC Ba – Gwamnan Zamfara

An fara kafa mutum-mutumin a shekara ta 1934 kafin a canja shi bayan yakin duniya na biyu, ana koyar da dalibai a Japan labarin Chuken Hachiko ko Hachiko Karen Alkawari a matsayin misalin amana da sadaukarwa.
Farfesa Christine Yano ta Jami’ar Hawaii ta ce Hachiko yana wakiltar “amintaccen dan Kasar Japan” la`akari da irin rikon amanarsa da cika alkawari da kuma biyayya ga Ubangidansa.

Labarin Hachiko
An haifi Hachiko a watan Nuwamba shekara ta 1923 a birnin Odate da ke Lardin Akita, a asalin gidan Akitas.

Kare ne mai girman jiki dan Kasar Japan, Akita daya ne daga cikin nau`in tsoffin karnukan da suka yi fice. Wadanda Gwamnatin Japan ta zabe su a matsayin alamar kasar a shekara ta 1931, an taba horar da su don farautar dabbobin daji.
“Karnukan Akita suna da natsuwa da amana da hankali da jarumtaka da kuma biyayya ga iyayen gidansu,” in ji Eietsu Sakuraba, marubucin gejerun labarai don yara a harshen Turanci.

Ya kuma bayyana cewar Karnukan su na da dabi`ar taurin kai da kuma taka-tsan-tsan da duk wanda ba Ubangidansu ba.
A shekarar da aka haifi Hachiko, Hidesaburo Ueno, wani mashahurin Farfesa a fannin noma kuma mai son karnuka ya nemi wani dalibi ya samo masa dan kwikwiyon Akita.
Bayan doguwar tafiya a jirgin kasa, dan kwikwiyon ya isa gidan Ueno a gundumar Shibuya ranar 15 ga watan Janairun shekara ta 1924, da farko an yi tsammanin karen ya mutu.

Marubucin tarihin Hachiko Farfesa Mayumi Itoh, ya bayyana cewar Ueno da matarsa, Ya ce sun yi jinyar karen har zuwa lokacin da ya murmure a tsawon watanni shida.
Ueno ya rada masa suna Hachi, ma`ana takwas ke nan a harshen Japan, ko kuma lakabi ne na girmamawa da daliban Ueno suka rada masa.

Dogon Jira
Ueno ya na shiga jirgin kasa sau da dama a mako kuma yana tafiya ne da karnuka 3 da suka hada da Hachiko, haka karnukan suke zaman jiransa har ya dawo da maraice.
A ranar 21 ga watan Mayu shekara ta 1925 a lokacin Ueno yana da shekaru 53 da haihuwa sai ya mutu sakamako ciwo a lakarsa, a lokacin Hachiko yana da watanni goma sha shida tare da su.

Farfesa Itoh ya bayyana cewar yayin da jama`a suke zaman alhinin mutuwar mamacin, sai Hachi ya jiyo kamshin Ubangidansa Dakta Ueno daga cikin gida don haka sai ya kutsa cikin gidan ya shiga karkashin makarar da aka sanya Ueno ya ki fitowa.

Hachiko ya rayu da iyalai daban-daban bayan mutuwar Ubangidansa a wajen gundumar Shibuya amma daga karshe a shekara ta 1928 ya koma gurin Kikusaburo Kobayashi mai kula da furannin ubangidansa.
Ganin ya koma inda Ubangidansa ya rayu, sai Hachiko ya koma sintiri zuwa tashar jiragen kasa kullum komai ruwa komai zafin rana.
Ya shahara a kasar bayan Jaridar Asahi Shimbun ta fitar da wani labarinsa a watan Oktoban shekara ta 1932.

Tashar Jiragen kasan ta samu gudummawar abincin Hachiko na kowacce rana, yayin da baki suke zuwa don ganinsa, an rubuta kasidu da dama game da shi.

A shekara ta 1934 an kaddamar da gidauniyar kera mutum-mutuminsa, wacce ta samu halartar mutane akalla dubu uku.
Hachiko ya mutu a ranar 8 ga watan Maris shekara ta 1935, labarin da Jaridu da dama suka buga, shugabannin Addinin Buddha sun yi masa da addu`o`i yayin da dubban mutane suka ziyarci mutum-mutuminsa.

Tunawa da Hachiko
Kowace shekara a ranar 8 ga watan Afrilu, ana gudanar da taron tunawa da Hachiko a tashar Shibuya, a lokaci ana yi wa mutum-mutuminsa ado da gyale da hular Santa da kuma kuma takunkumin rufe fuska.
Shin ko za a ci gaba da bikin tunawa da kare mafi rikon alkawari a duniya shekaru dari daga yanzu? Farfesa Yano ta ce labarin “jarumtar Hachiko” ba ya da lokacin karewa.
Shi ma Mista Sakuraba yana da kyakkyawan fatan labarin Hachiko zai dore har abada. Mun ciro daga BBC HAUSA


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kiwon Lafiya: Yadda Dabi’un Ko-in-kula Ke Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke (II)

Next Post

Diphtheria: Kano Ce Kan Gaba A Yawan Masu Dauke Da Cutar Mashaƙo A Nijeriya

Related

Tinubu Bai TaÉ“a Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Bai TaÉ“a Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista

51 minutes ago
Har Yanzu A Cikin PDP Nake, Ba Zan Koma APC Ko ADC Ba – Gwamnan Zamfara
Manyan Labarai

Har Yanzu A Cikin PDP Nake, Ba Zan Koma APC Ko ADC Ba – Gwamnan Zamfara

9 hours ago
EFCC Ta Kama Ƴan Ƙasashen Waje 146 Kan Laifukan Zambar Kuɗaɗe
Labarai

EFCC Ta Kama Ƴan Ƙasashen Waje 146 Kan Laifukan Zambar Kuɗaɗe

10 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 13 A Neja
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 13 A Neja

11 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina

13 hours ago
Na Biya Bashin Garatutin Naira Biliyan 13.6 Da ’Yan Fanshon Zamfara Ke Bi Tun 2011 – Gwamna Lawal
Labarai

Na Biya Bashin Garatutin Naira Biliyan 13.6 Da ’Yan Fanshon Zamfara Ke Bi Tun 2011 – Gwamna Lawal

13 hours ago
Next Post
Hajji 2023: Alhazan Nijeriya 6 Sun Rasu, 30 Na Da Tabin Hankali A Saudiyya

Diphtheria: Kano Ce Kan Gaba A Yawan Masu Dauke Da Cutar Mashaƙo A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Bai TaÉ“a Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista

Tinubu Bai TaÉ“a Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista

July 10, 2025
UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba

UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba

July 9, 2025
Har Yanzu A Cikin PDP Nake, Ba Zan Koma APC Ko ADC Ba – Gwamnan Zamfara

Har Yanzu A Cikin PDP Nake, Ba Zan Koma APC Ko ADC Ba – Gwamnan Zamfara

July 9, 2025
An Fara Taron Nishan Karo Na 11 Game Da Wayewar Kai A Duniya

An Fara Taron Nishan Karo Na 11 Game Da Wayewar Kai A Duniya

July 9, 2025
EFCC Ta Kama Ƴan Ƙasashen Waje 146 Kan Laifukan Zambar Kuɗaɗe

EFCC Ta Kama Ƴan Ƙasashen Waje 146 Kan Laifukan Zambar Kuɗaɗe

July 9, 2025
An Yi Hasashen Karuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Tiriliyan 35 Tsakanin 2021 Zuwa 2025

An Yi Hasashen Karuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Tiriliyan 35 Tsakanin 2021 Zuwa 2025

July 9, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 13 A Neja

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 13 A Neja

July 9, 2025
Ma’anar Sabon Tsarin Hadin Kan Mambobin Brics a Sabon Zamani Ga Dunkulewar Kasashe Masu Tasowa

Ma’anar Sabon Tsarin Hadin Kan Mambobin Brics a Sabon Zamani Ga Dunkulewar Kasashe Masu Tasowa

July 9, 2025
Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique

Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique

July 9, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Kara Kamfanoni 8 Na Yankin Taiwan Cikin Jerin Wadanda Aka Takaita Sayar Musu Kayayyaki

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Kara Kamfanoni 8 Na Yankin Taiwan Cikin Jerin Wadanda Aka Takaita Sayar Musu Kayayyaki

July 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.