Shugabar Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta Jihar Kaduna (KASTLEA), Carla Abdulmalik, ta bayyana jin daɗinta kan matakin da Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya ɗauka na samar da na’urorin zamani domin daƙile yawaitar afkuwar haɗurra a manyan hanyoyin jihar.
Carla ta ce gwamnan ya samar da kyamarori na zamani da za su riƙa sa ido kan zirga-zirgar ababen hawa, domin gano direbobin da ke karya dokokin hanya da kuma taimakawa wajen tabbatar da bin ƙa’idojin tuƙi a faɗin Jihar Kaduna.
- KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano
- Gwamnan Kano Ya Yi Allah-wadai Da Kisan Uwa Da ‘Ya’yanta 6, Ya Umarci A Kamo Masu Laifin
Shugabar ta bayyana haka ne a zantawarta da manema labarai, tana mai cewa baya ga kyamarorin, gwamnatin jihar ta kuma samar wa jami’an KASTLEA kayan aikin zamani da za su taimaka musu wajen gano takardun ababen hawa na boge, tare da inganta tsarin isar da saƙonni da bayanai ga jami’an hukumar a duk inda suke, domin sauƙaƙa aikinsu da kuma ƙara inganci.
Ta bayyana cewa wannan doka na da matuƙar muhimmanci wajen rage cunkoso, haɗurra, da kuma tabbatar da sauƙin zirga-zirga a cikin birnin, tare da jan hankalin direbobi da kamfanonin sufuri da su bai wa hukumar haɗin kai domin cimma burin da aka sanya a gaba.
A cewarta, waɗannan matakai na daga cikin ƙoƙarin da gwamnatin Uba Sani ke yi na inganta harkar sufuri da kare rayukan al’ummar Jihar Kaduna.















Discussion about this post