ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasuwar Musayar ‘Yan Kwallo: Yadda ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Canza Kungiyoyi

by Abba Ibrahim Wada
4 months ago
Nijeriya

‘Yan wasa da dama daga Nijeriya, sun samu sauyin kungiyoyin da suke taka leda, yayin da aka bude kasuwar saye da sayar da ‘yan wasa ta nahiyar Turai.

A watan Janairu, yayin da wasu suka canza kungiya a matsayin aro, wasu kuma sun canza ne a matsayin dindindin.

  • Shugabancin Ƙungiyar Kasuwar Singa (SIMDA) Ya Karyata Rahoton Tashin Sabuwar Gobara A Kasuwar
  • Arewa Maso Gabashin Jigawa: Abokan Babandede Sun Dauki Harama

Leadership Hausa, ta zakulo muku cikakken jerin sauye-sauyen kungiyoyin da ‘yan wasan suka samu.

ADVERTISEMENT

ADEMOLA LOOKMAN

Atalanta zuwa Atletico Madrid (Yuro Miliyan 35)

LABARAI MASU NASABA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Daya daga cikin manyan canje-canjen da aka samu shi ne, sauya shekar dan wasan Atalanta, kuma tsohon gwarzon dan kwallon kafar nahiyar Afirika.

Ademola Lookman, wanda ya koma kungiyar kwallon kafa ta Atletico Madrid ta kasar Sifaniya, a kan kudi Yuro miliyan 35.

Lookman ya taka rawar gani a gasar cin kofin kasashen nahiyar Afirika da aka kammala a Kasar Morocco, bayan ya zura kwallaye 3, kuma ya taimaka wajen zura 4, hakan ya kara habaka martabarsa a fagen kwallon kafa a duniya, wanda ya jawo Atletico Madrid ta biya Yuro miliyan 35, domin daukar dan wasa mai shekaru 28, Lookman ya zama dan wasa na biyu daga Nijeriya da zai buga wa Rojiblancos din wasa a tarihi.

FRANK ONYEKA

Brentford zuwa Cobentry City (Aro)

Wani sauyin sheka da ya bayar da mamaki shi ne, na Frank Onyeka, wanda kungiyar Brentford ta bayar da shi aro ga Cobentry City da ke buga gasar Championship ta Kasar Ingila, amma Onyeka yana da damar taka muhimmiyar rawa a kokarin da Cobentry City ke yi, wajen ganin sun samu gurbi a gasar Premier League a karon farko cikin shekaru 25.

BICTOR MOSES (Fc Kaysar)

Bayan shafe wata bakwai ba tare da kungiya ba, Moses dan shekara 35,

ya sanya hannu a wani kwantiragi da kungiyar kwallon kafa ta FC Kaysar ta kasar Kazakhstan, tsohon dan wasan na Chelsea, ya sanya hannu kan yarjejeniyar shekara daya, inda ake fatan zai taimaka wajen mayar da kungiyar da ke fama da kalubale zuwa matakin nasara.

WILLIAM TROOST-EKONG

Al-Kholood zuwa Al-Ahli

Tsohon kyaftin din Super Eagles, ya samu canjin kungiya babu zato babu tsammani a watan Janairu, Ekong ya bar tsohuwar kungiyarsa ta Al-Khoolod ta Kasar Saudiyya, inda ya koma kungiyar Al-Ahli ta kasar Katar, inda nan take ya lashe gasar cin kofin UAE (Katar Super Cup), bayan samun nasara a kan Al Jazira.

JOE ARIBO (Aro)

Dan wasan tsakiya mai shekara 27, ya sha fama da rashin buga wasanni a Southampton, a wannan kakar ta bana, hakan ya sa ya zabi komawa Leicester City a matsayin aro, inda ake ganin wannan canjin da ya samu zai zamar masa wata hanya da zai nuna wa duniya irin bajinyar da yake da ita a fagen taka leda.

SADIK UMAR

Real Sociedad zuwa Balencia (Yuro miliyan 5)

Sadik ya kawo karshen wahalar da ya sha a Real Sociedad na rashin samun lokutan wasanni, bayan komawa Balencia a zaman dindindin na kungiyar da a baya ya zauna zaman aro, yanzu dan wasan yana da sabuwar dama ta farfado da kwarewarsa da kuma sake samun tagomashi a bangaren wasannin gida.

TEREM MOFFI

OGC Nice zuwa Fc Porto

Dangantaka ta yi tsami tsakanin Terem Moffi da magoya bayan Nice a

kwanakin baya, inda har ta kai ga magoya bayan kungiyar sun jefi dan

was an, bayan wata rashin nasara da suka yi, hakan ya sa tsohon dan wasan tawagar Super Eagles din ya zabi komawa Fc Porto a matsayin aro, dan wasan zai yi kokarin ganin zaman aron ya rikide zuwa zaman dindindin.

RAFIU DUROSINMI

Biktoria Plzen zuwa Pisa (Yuro miliyan 9)

Dan wasan gaban mai shekara 23, ya kammala komawa kungiyar Pisa da ke buga gasar Serie A ta Kasar Italiya ba tare da wata matsala ba a farkon watan Janairu, Durosinmi ya samu nasarar jefa kwallo 1, kuma ya taimaka aka jefa kwallaye 3, tun bayan komawarsa Pisa.

TOCHUKWU NNADI

Zulte Waregem zuwa Marseille (Yuro miliyan 6)

Dan wasan tsakiya mai shekara 22, yana cikin tawagar Nijeriya ta AFCON na 2025 da aka kamala, a cikin tawagar ‘yan wasan na tsakiya, ya ci gaba da samun ci gaba cikin sauri a harkar kwallon kafa, ana kallonsa a matsayin wanda zai iya maye gurbin Wilfred Ndidi, komawar Nnadi zuwa babbar kungiyar Ligue 1 ta Marseille, alama ce ta samun babban ci gaba.

SALIM FAGO LAWAL

NK Istra zuwa Biktoria Plzen  (Yuro miliyan 2)

Shigar Salim Fago cikin tawagar Super Eagles ta Nijeriya, ta bai wa

kungiyarsa ta Istra mamaki, kwallaye 7 da ya ci, kuma ya taimaka wajen

jefa 2, wadanda suka taimaka wa Istra zuwa matsayi na 3 a teburin gasar kasar.

Croatia, komawarsa zuwa Bictoria Plezn, zai zama wani mataki babba a

rayuwarsa ta kwallon kafa, yayin da kuma zai sake samun gayyata daga

tawagar kasa.

LEONARD NGENGE

Remo Stars zuwa Leeds United

Dan wasan mai shekara 18, ya samu ci gaba mai girma daga gasar kwallon kafa ta Nijeriya zuwa daya daga cikin manyan kungiyoyin kwallon kafa a Ingila, duk da cewa; a halin yanzu ya shiga makarantar horar da ‘yan was an Leeds United, wannan wata alama ce da ke nuna kyakkyawar makoma ga dan wasan.

CHIBUIKE NWAIWU

Wolfsberger zuwa Trabzonspor (Yuro miliyan 5)

Dan wasan tsakiya mai shekara 22, ya sauya sheka zuwa kungiyar kwallon kafa ta Trapzanspor ta kasar Turkiyya, inda ya buga wasanni uku zuwa yanzu a gasar, tun bayan komawarsa a watan Janairu, tsohon dan wasan na Enyimba ya bayyana a shirye ya ke wajen ganin ya samu wuri a kungiyar.

Sauran su ne:

UCHENNA OGUNDU

Alanyaspor zuwa Augsburg (Yuro miliyan 4)

SULEMAN SANI

Trencin zuwa RB Leipzig  (Yuro miliyan 5)

EHIJE UKAKI

Sheffield United zuwa Atromitos (Aro)

EJIKE OPARA

Nobi Pazar zuwa Biktoria Guimaraes

Nijeriya
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Jiya Aka Fara Gasar Cin Kofin Duniya
  • Abba Ibrahim Wada
    Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya
  • Abba Ibrahim Wada
    Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

MASU ALAKA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé
Wasanni

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?
Wasanni

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Next Post
Kasashe 10 Da Kudadensu Suka Fi Daraja A Duniya

Kasashe 10 Da Kudadensu Suka Fi Daraja A Duniya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.