ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasuwar Musayar ‘Yan Kwallo: Yadda ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Canza Kungiyoyi

by Abba Ibrahim Wada
5 months ago
Nijeriya

‘Yan wasa da dama daga Nijeriya, sun samu sauyin kungiyoyin da suke taka leda, yayin da aka bude kasuwar saye da sayar da ‘yan wasa ta nahiyar Turai.

A watan Janairu, yayin da wasu suka canza kungiya a matsayin aro, wasu kuma sun canza ne a matsayin dindindin.

  • Shugabancin Ƙungiyar Kasuwar Singa (SIMDA) Ya Karyata Rahoton Tashin Sabuwar Gobara A Kasuwar
  • Arewa Maso Gabashin Jigawa: Abokan Babandede Sun Dauki Harama

Leadership Hausa, ta zakulo muku cikakken jerin sauye-sauyen kungiyoyin da ‘yan wasan suka samu.

ADVERTISEMENT

ADEMOLA LOOKMAN

Atalanta zuwa Atletico Madrid (Yuro Miliyan 35)

LABARAI MASU NASABA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

Daya daga cikin manyan canje-canjen da aka samu shi ne, sauya shekar dan wasan Atalanta, kuma tsohon gwarzon dan kwallon kafar nahiyar Afirika.

Ademola Lookman, wanda ya koma kungiyar kwallon kafa ta Atletico Madrid ta kasar Sifaniya, a kan kudi Yuro miliyan 35.

Lookman ya taka rawar gani a gasar cin kofin kasashen nahiyar Afirika da aka kammala a Kasar Morocco, bayan ya zura kwallaye 3, kuma ya taimaka wajen zura 4, hakan ya kara habaka martabarsa a fagen kwallon kafa a duniya, wanda ya jawo Atletico Madrid ta biya Yuro miliyan 35, domin daukar dan wasa mai shekaru 28, Lookman ya zama dan wasa na biyu daga Nijeriya da zai buga wa Rojiblancos din wasa a tarihi.

FRANK ONYEKA

Brentford zuwa Cobentry City (Aro)

Wani sauyin sheka da ya bayar da mamaki shi ne, na Frank Onyeka, wanda kungiyar Brentford ta bayar da shi aro ga Cobentry City da ke buga gasar Championship ta Kasar Ingila, amma Onyeka yana da damar taka muhimmiyar rawa a kokarin da Cobentry City ke yi, wajen ganin sun samu gurbi a gasar Premier League a karon farko cikin shekaru 25.

BICTOR MOSES (Fc Kaysar)

Bayan shafe wata bakwai ba tare da kungiya ba, Moses dan shekara 35,

ya sanya hannu a wani kwantiragi da kungiyar kwallon kafa ta FC Kaysar ta kasar Kazakhstan, tsohon dan wasan na Chelsea, ya sanya hannu kan yarjejeniyar shekara daya, inda ake fatan zai taimaka wajen mayar da kungiyar da ke fama da kalubale zuwa matakin nasara.

WILLIAM TROOST-EKONG

Al-Kholood zuwa Al-Ahli

Tsohon kyaftin din Super Eagles, ya samu canjin kungiya babu zato babu tsammani a watan Janairu, Ekong ya bar tsohuwar kungiyarsa ta Al-Khoolod ta Kasar Saudiyya, inda ya koma kungiyar Al-Ahli ta kasar Katar, inda nan take ya lashe gasar cin kofin UAE (Katar Super Cup), bayan samun nasara a kan Al Jazira.

JOE ARIBO (Aro)

Dan wasan tsakiya mai shekara 27, ya sha fama da rashin buga wasanni a Southampton, a wannan kakar ta bana, hakan ya sa ya zabi komawa Leicester City a matsayin aro, inda ake ganin wannan canjin da ya samu zai zamar masa wata hanya da zai nuna wa duniya irin bajinyar da yake da ita a fagen taka leda.

SADIK UMAR

Real Sociedad zuwa Balencia (Yuro miliyan 5)

Sadik ya kawo karshen wahalar da ya sha a Real Sociedad na rashin samun lokutan wasanni, bayan komawa Balencia a zaman dindindin na kungiyar da a baya ya zauna zaman aro, yanzu dan wasan yana da sabuwar dama ta farfado da kwarewarsa da kuma sake samun tagomashi a bangaren wasannin gida.

TEREM MOFFI

OGC Nice zuwa Fc Porto

Dangantaka ta yi tsami tsakanin Terem Moffi da magoya bayan Nice a

kwanakin baya, inda har ta kai ga magoya bayan kungiyar sun jefi dan

was an, bayan wata rashin nasara da suka yi, hakan ya sa tsohon dan wasan tawagar Super Eagles din ya zabi komawa Fc Porto a matsayin aro, dan wasan zai yi kokarin ganin zaman aron ya rikide zuwa zaman dindindin.

RAFIU DUROSINMI

Biktoria Plzen zuwa Pisa (Yuro miliyan 9)

Dan wasan gaban mai shekara 23, ya kammala komawa kungiyar Pisa da ke buga gasar Serie A ta Kasar Italiya ba tare da wata matsala ba a farkon watan Janairu, Durosinmi ya samu nasarar jefa kwallo 1, kuma ya taimaka aka jefa kwallaye 3, tun bayan komawarsa Pisa.

TOCHUKWU NNADI

Zulte Waregem zuwa Marseille (Yuro miliyan 6)

Dan wasan tsakiya mai shekara 22, yana cikin tawagar Nijeriya ta AFCON na 2025 da aka kamala, a cikin tawagar ‘yan wasan na tsakiya, ya ci gaba da samun ci gaba cikin sauri a harkar kwallon kafa, ana kallonsa a matsayin wanda zai iya maye gurbin Wilfred Ndidi, komawar Nnadi zuwa babbar kungiyar Ligue 1 ta Marseille, alama ce ta samun babban ci gaba.

SALIM FAGO LAWAL

NK Istra zuwa Biktoria Plzen  (Yuro miliyan 2)

Shigar Salim Fago cikin tawagar Super Eagles ta Nijeriya, ta bai wa

kungiyarsa ta Istra mamaki, kwallaye 7 da ya ci, kuma ya taimaka wajen

jefa 2, wadanda suka taimaka wa Istra zuwa matsayi na 3 a teburin gasar kasar.

Croatia, komawarsa zuwa Bictoria Plezn, zai zama wani mataki babba a

rayuwarsa ta kwallon kafa, yayin da kuma zai sake samun gayyata daga

tawagar kasa.

LEONARD NGENGE

Remo Stars zuwa Leeds United

Dan wasan mai shekara 18, ya samu ci gaba mai girma daga gasar kwallon kafa ta Nijeriya zuwa daya daga cikin manyan kungiyoyin kwallon kafa a Ingila, duk da cewa; a halin yanzu ya shiga makarantar horar da ‘yan was an Leeds United, wannan wata alama ce da ke nuna kyakkyawar makoma ga dan wasan.

CHIBUIKE NWAIWU

Wolfsberger zuwa Trabzonspor (Yuro miliyan 5)

Dan wasan tsakiya mai shekara 22, ya sauya sheka zuwa kungiyar kwallon kafa ta Trapzanspor ta kasar Turkiyya, inda ya buga wasanni uku zuwa yanzu a gasar, tun bayan komawarsa a watan Janairu, tsohon dan wasan na Enyimba ya bayyana a shirye ya ke wajen ganin ya samu wuri a kungiyar.

Sauran su ne:

UCHENNA OGUNDU

Alanyaspor zuwa Augsburg (Yuro miliyan 4)

SULEMAN SANI

Trencin zuwa RB Leipzig  (Yuro miliyan 5)

EHIJE UKAKI

Sheffield United zuwa Atromitos (Aro)

EJIKE OPARA

Nobi Pazar zuwa Biktoria Guimaraes

Nijeriya
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City
  • Abba Ibrahim Wada
    LeBron James Zai Bar Los Angeles Lakers 
  • Abba Ibrahim Wada
    An Raba Jadawalin Gasar Premier Ta Ingila Ta Kakar Wasan 2026/2027
  • Abba Ibrahim Wada
    Daga 1930 Zuwa 2026: Yadda Aka Buga Wasa Na Dubu Ɗaya A Gasar Kofin Duniya

MASU ALAKA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA
Wasanni

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa
Wasanni

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City
Wasanni

Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

July 5, 2026
Next Post
Kasashe 10 Da Kudadensu Suka Fi Daraja A Duniya

Kasashe 10 Da Kudadensu Suka Fi Daraja A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Kwankwaso Ya Yi Ta’aziyyar ’Ya’yan Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi da Suka Rasu a Hatsarin Mota

July 6, 2026
An Kaddamar Da Atisayen Hadin Gwiwa Mai Taken “Hadin Gwiwar Ayyuka Kan Teku-2026” Tsakanin Sin Da Rasha

An Kaddamar Da Atisayen Hadin Gwiwa Mai Taken “Hadin Gwiwar Ayyuka Kan Teku-2026” Tsakanin Sin Da Rasha

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.