ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasuwar Musayar ‘Yan Kwallo: Yadda ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Canza Kungiyoyi

by Abba Ibrahim Wada
4 months ago
Nijeriya

‘Yan wasa da dama daga Nijeriya, sun samu sauyin kungiyoyin da suke taka leda, yayin da aka bude kasuwar saye da sayar da ‘yan wasa ta nahiyar Turai.

A watan Janairu, yayin da wasu suka canza kungiya a matsayin aro, wasu kuma sun canza ne a matsayin dindindin.

  • Shugabancin Ƙungiyar Kasuwar Singa (SIMDA) Ya Karyata Rahoton Tashin Sabuwar Gobara A Kasuwar
  • Arewa Maso Gabashin Jigawa: Abokan Babandede Sun Dauki Harama

Leadership Hausa, ta zakulo muku cikakken jerin sauye-sauyen kungiyoyin da ‘yan wasan suka samu.

ADVERTISEMENT

ADEMOLA LOOKMAN

Atalanta zuwa Atletico Madrid (Yuro Miliyan 35)

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Daya daga cikin manyan canje-canjen da aka samu shi ne, sauya shekar dan wasan Atalanta, kuma tsohon gwarzon dan kwallon kafar nahiyar Afirika.

Ademola Lookman, wanda ya koma kungiyar kwallon kafa ta Atletico Madrid ta kasar Sifaniya, a kan kudi Yuro miliyan 35.

Lookman ya taka rawar gani a gasar cin kofin kasashen nahiyar Afirika da aka kammala a Kasar Morocco, bayan ya zura kwallaye 3, kuma ya taimaka wajen zura 4, hakan ya kara habaka martabarsa a fagen kwallon kafa a duniya, wanda ya jawo Atletico Madrid ta biya Yuro miliyan 35, domin daukar dan wasa mai shekaru 28, Lookman ya zama dan wasa na biyu daga Nijeriya da zai buga wa Rojiblancos din wasa a tarihi.

FRANK ONYEKA

Brentford zuwa Cobentry City (Aro)

Wani sauyin sheka da ya bayar da mamaki shi ne, na Frank Onyeka, wanda kungiyar Brentford ta bayar da shi aro ga Cobentry City da ke buga gasar Championship ta Kasar Ingila, amma Onyeka yana da damar taka muhimmiyar rawa a kokarin da Cobentry City ke yi, wajen ganin sun samu gurbi a gasar Premier League a karon farko cikin shekaru 25.

BICTOR MOSES (Fc Kaysar)

Bayan shafe wata bakwai ba tare da kungiya ba, Moses dan shekara 35,

ya sanya hannu a wani kwantiragi da kungiyar kwallon kafa ta FC Kaysar ta kasar Kazakhstan, tsohon dan wasan na Chelsea, ya sanya hannu kan yarjejeniyar shekara daya, inda ake fatan zai taimaka wajen mayar da kungiyar da ke fama da kalubale zuwa matakin nasara.

WILLIAM TROOST-EKONG

Al-Kholood zuwa Al-Ahli

Tsohon kyaftin din Super Eagles, ya samu canjin kungiya babu zato babu tsammani a watan Janairu, Ekong ya bar tsohuwar kungiyarsa ta Al-Khoolod ta Kasar Saudiyya, inda ya koma kungiyar Al-Ahli ta kasar Katar, inda nan take ya lashe gasar cin kofin UAE (Katar Super Cup), bayan samun nasara a kan Al Jazira.

JOE ARIBO (Aro)

Dan wasan tsakiya mai shekara 27, ya sha fama da rashin buga wasanni a Southampton, a wannan kakar ta bana, hakan ya sa ya zabi komawa Leicester City a matsayin aro, inda ake ganin wannan canjin da ya samu zai zamar masa wata hanya da zai nuna wa duniya irin bajinyar da yake da ita a fagen taka leda.

SADIK UMAR

Real Sociedad zuwa Balencia (Yuro miliyan 5)

Sadik ya kawo karshen wahalar da ya sha a Real Sociedad na rashin samun lokutan wasanni, bayan komawa Balencia a zaman dindindin na kungiyar da a baya ya zauna zaman aro, yanzu dan wasan yana da sabuwar dama ta farfado da kwarewarsa da kuma sake samun tagomashi a bangaren wasannin gida.

TEREM MOFFI

OGC Nice zuwa Fc Porto

Dangantaka ta yi tsami tsakanin Terem Moffi da magoya bayan Nice a

kwanakin baya, inda har ta kai ga magoya bayan kungiyar sun jefi dan

was an, bayan wata rashin nasara da suka yi, hakan ya sa tsohon dan wasan tawagar Super Eagles din ya zabi komawa Fc Porto a matsayin aro, dan wasan zai yi kokarin ganin zaman aron ya rikide zuwa zaman dindindin.

RAFIU DUROSINMI

Biktoria Plzen zuwa Pisa (Yuro miliyan 9)

Dan wasan gaban mai shekara 23, ya kammala komawa kungiyar Pisa da ke buga gasar Serie A ta Kasar Italiya ba tare da wata matsala ba a farkon watan Janairu, Durosinmi ya samu nasarar jefa kwallo 1, kuma ya taimaka aka jefa kwallaye 3, tun bayan komawarsa Pisa.

TOCHUKWU NNADI

Zulte Waregem zuwa Marseille (Yuro miliyan 6)

Dan wasan tsakiya mai shekara 22, yana cikin tawagar Nijeriya ta AFCON na 2025 da aka kamala, a cikin tawagar ‘yan wasan na tsakiya, ya ci gaba da samun ci gaba cikin sauri a harkar kwallon kafa, ana kallonsa a matsayin wanda zai iya maye gurbin Wilfred Ndidi, komawar Nnadi zuwa babbar kungiyar Ligue 1 ta Marseille, alama ce ta samun babban ci gaba.

SALIM FAGO LAWAL

NK Istra zuwa Biktoria Plzen  (Yuro miliyan 2)

Shigar Salim Fago cikin tawagar Super Eagles ta Nijeriya, ta bai wa

kungiyarsa ta Istra mamaki, kwallaye 7 da ya ci, kuma ya taimaka wajen

jefa 2, wadanda suka taimaka wa Istra zuwa matsayi na 3 a teburin gasar kasar.

Croatia, komawarsa zuwa Bictoria Plezn, zai zama wani mataki babba a

rayuwarsa ta kwallon kafa, yayin da kuma zai sake samun gayyata daga

tawagar kasa.

LEONARD NGENGE

Remo Stars zuwa Leeds United

Dan wasan mai shekara 18, ya samu ci gaba mai girma daga gasar kwallon kafa ta Nijeriya zuwa daya daga cikin manyan kungiyoyin kwallon kafa a Ingila, duk da cewa; a halin yanzu ya shiga makarantar horar da ‘yan was an Leeds United, wannan wata alama ce da ke nuna kyakkyawar makoma ga dan wasan.

CHIBUIKE NWAIWU

Wolfsberger zuwa Trabzonspor (Yuro miliyan 5)

Dan wasan tsakiya mai shekara 22, ya sauya sheka zuwa kungiyar kwallon kafa ta Trapzanspor ta kasar Turkiyya, inda ya buga wasanni uku zuwa yanzu a gasar, tun bayan komawarsa a watan Janairu, tsohon dan wasan na Enyimba ya bayyana a shirye ya ke wajen ganin ya samu wuri a kungiyar.

Sauran su ne:

UCHENNA OGUNDU

Alanyaspor zuwa Augsburg (Yuro miliyan 4)

SULEMAN SANI

Trencin zuwa RB Leipzig  (Yuro miliyan 5)

EHIJE UKAKI

Sheffield United zuwa Atromitos (Aro)

EJIKE OPARA

Nobi Pazar zuwa Biktoria Guimaraes

Nijeriya
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Next Post
Kasashe 10 Da Kudadensu Suka Fi Daraja A Duniya

Kasashe 10 Da Kudadensu Suka Fi Daraja A Duniya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.