Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarnin tura bataliyar Sojoji zuwa Ƙaramar Hukumar Kaiama a Jihar Kwara, biyo bayan kisan gillar da ’yan Boko Haram suka yi wa jama’a da dama a ƙauyen Worro.
A cikin wata sanarwa da kakakin shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya fitar, Tinubu ya ce sabuwar rundunar za ta jagoranci aikin soji mai taken Operation Savannah Shield, domin daƙile hare-haren ’yan ta’adda tare da kare al’ummomin da ba su da kariya.
- ’Yan Bindiga Sun Kashe Mutane, Sun Ƙone Gidaje A Ƙauyukan Kwara
- Xi Da Takwaransa Na Aljeriya Sun Taya Juna Murna Kan Nasarar Harba Tauraron Dan Adam Na Aljeriya
Shugaban ƙasar ya yi Allah-wadai da harin, yana mai bayyana ’yan bindigar a matsayin marasa imani da tausayi, musamman ganin yadda suka kai hari kan fararen hula. Ya kuma nuna ɓacin ransa kan yadda aka kashe mutanen da suka ƙi karɓar aƙidar tsattsauran ra’ayi.
Tinubu ya yi kira ga haɗin gwuiwar hukumomin tarayya da na jiha domin tallafa wa waɗanda abin ya shafa, tare da tabbatar da cewa waɗanda suka aikata laifin ba za su tsira ba. Ya kuma miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan mamatan da al’ummar Jihar Kwara baki ɗaya, yana roƙon Allah Ya jiƙan waɗanda suka rasu.















Discussion about this post