• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Shakka Babu Tinubu Ne Zai Lashe Zaben Shugaban Kasa A 2027 – APC

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
8 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
APC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar APC mai mulki ta gargadi jam’iyyun adawa a Nijeriya ka da su yi zumudin kan kayen da aka yi wa Kamala Harris, a zaben shugaban kasar Amurka, inda ta ce ko shakka babu Shugaba Bola Tinubu zai sake lashe zaben shugaban kasa a shekarar 2027.

 

A ranar Laraba ne aka sanar da tsohon shugaban kasar Amurka, Donald Trump a matsayin wanda ya lashe zaben Amurka, bayan da ya doke Harris a wani gagarumin siyasa da ya jefa fargaba a duniya.

  • Mizanin Hajoji Da Hidimomi Da Masana’antun Kasar Sin Ke Samarwa Ya Karu Da Kaso 5.3 Bisa Dari A Watan Oktoba
  • Kudirin Sake Fasalin Haraji Ya Raba Kan ‘Yan Majalisar Arewa

Dan kasuwan mai shekaru 78 a duniya ya zama shugaban kasa na 47, kuma shi ne mutum mafi tsufa da ya taba lashe zaben Amurka.

 

Labarai Masu Nasaba

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

Da yake mayar da martani, sakataren yada labarai na jam’iyyar LP, Obiora Ifo, ya bayyana zaben Amurka da aka sa ido a duk duniya a matsayin gwajin dimokuradiyya na gaskiya.

 

Yayin da yake bayyana cewa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) tana da darrusa masu yawa da za ta koya daga zaben Amurka, Ifoh ya ce, abin sha’awa ne ganin yadda Amurkawa masu kada kuri’a suka yi biris da jam’iyya mai mulki, wanda har yanzu shi ne tasiri a zaben Afirka, musamman a Nijeriya.

 

Shi ma da yake mayar da martini kan zaben Amurkan, mai magana da yawun jam’iyyar NNPP, Ladipo Johnson, ya ce duk da cewa tsarin zaben Amurka yana da sarkakkiya kuma ya yi nisa, yana mamakin yaushe ne Nijeriya za ta kawo karshen shugabanni masu tsatsauran ra’ayi da ke amfani da karfin mulki da jami’an tsaro wajen mulkin kama karya wanda ‘yan adawa kan iya kayar da jam’iyya mai mulki kai tsaye.

 

Sai dai daraktan yada labarai na jam’iyyar APC na kasa, Bala Ibrahim ya gargadi ‘yan adawa da ka da su bari sakamakon zaben Amurka ya yaudare su, yana mai cewa tsarin zabe a tsakanin kasashen biyu ya sha bamban.

 

Bala, wanda ya bayyana haka a zantarsa da manema labarai, ya bayyana cewa ba a ko da yaushe karfin mulki ke tasiri ba, lokacin da jama’a suka yi magana da murya daya kamar yadda aka shaida nasarar da tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya samu kan shugaba mai ci, Goodluck Jonathan a 2015.

 

Mai magana da yawun jam’iyyar APC ya bayyana yakinin cewa a lokacin da ‘yan Nijeriya za su fara karbar tukuicin gyare-gyaren tattalin arzikin da shugaban kasa ya yi, za su yaba masa tare da bukatar ya ci gaba da wa’adi na biyu.

 

Ya ce, “Yadda wannan gwamnatin ta APC ke aiki tukuru, ta kawo sabbin gyare-gyare da sauye-sauye da ke da daci, za mu ci riba sosai a nan gaba.

 

“Muna sa ran fara ganin amfanin wadannan sauye-sauye kafin lokacin zabe. Wato a kusa da 2026 da 2027. A lokacin ne mutane za su fara yaba wa jam’iyya da shugaban kasa.

 

“Ba zai yi wuya wani ya fito daga waje ba, musamman wani bare da ya gaza a baya, ko wani baren da ya kasa sawo kan rikicin cikin gidansa kuma ya yi tunanin kayar da mai mulki. Zai yi wahala sosai. Jam’iyyar APC da shugaban kasa suna da masaniya kan wannan zagon kasa da ‘yan adawa ke shirya musu.

 

“Amma ba wai a ce jam’iyya da shugaban kasa suna barci ba. A’a, suna yin dabarun da za a samu sakamako nan gaba. Don haka, idan muka kai gabar, za mu ga wanda ya fi karfin ketare ta. Kuma ina tabbatar muku da cewa, APC ne za ta lashe zaben shugaban kasa a 2027 a Nijeriya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Babban Taron Harshen Sinanci Na Duniya

Next Post

Tashar Chancay: Sabon Mafari Ne Ga “Tsohuwar Hanyar Inca A Sabon Zamani”

Related

Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

20 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Tambarin Dimokuradiyya

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

21 hours ago
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

22 hours ago
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

3 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

3 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

4 weeks ago
Next Post
Tashar Chancay: Sabon Mafari Ne Ga “Tsohuwar Hanyar Inca A Sabon Zamani”

Tashar Chancay: Sabon Mafari Ne Ga “Tsohuwar Hanyar Inca A Sabon Zamani"

LABARAI MASU NASABA

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

July 5, 2025
Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.