ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Shakka Babu Tinubu Ne Zai Lashe Zaben Shugaban Kasa A 2027 – APC

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
2 years ago
APC

Jam’iyyar APC mai mulki ta gargadi jam’iyyun adawa a Nijeriya ka da su yi zumudin kan kayen da aka yi wa Kamala Harris, a zaben shugaban kasar Amurka, inda ta ce ko shakka babu Shugaba Bola Tinubu zai sake lashe zaben shugaban kasa a shekarar 2027.

 

A ranar Laraba ne aka sanar da tsohon shugaban kasar Amurka, Donald Trump a matsayin wanda ya lashe zaben Amurka, bayan da ya doke Harris a wani gagarumin siyasa da ya jefa fargaba a duniya.

ADVERTISEMENT
  • Mizanin Hajoji Da Hidimomi Da Masana’antun Kasar Sin Ke Samarwa Ya Karu Da Kaso 5.3 Bisa Dari A Watan Oktoba
  • Kudirin Sake Fasalin Haraji Ya Raba Kan ‘Yan Majalisar Arewa

Dan kasuwan mai shekaru 78 a duniya ya zama shugaban kasa na 47, kuma shi ne mutum mafi tsufa da ya taba lashe zaben Amurka.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Da yake mayar da martani, sakataren yada labarai na jam’iyyar LP, Obiora Ifo, ya bayyana zaben Amurka da aka sa ido a duk duniya a matsayin gwajin dimokuradiyya na gaskiya.

 

Yayin da yake bayyana cewa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) tana da darrusa masu yawa da za ta koya daga zaben Amurka, Ifoh ya ce, abin sha’awa ne ganin yadda Amurkawa masu kada kuri’a suka yi biris da jam’iyya mai mulki, wanda har yanzu shi ne tasiri a zaben Afirka, musamman a Nijeriya.

 

Shi ma da yake mayar da martini kan zaben Amurkan, mai magana da yawun jam’iyyar NNPP, Ladipo Johnson, ya ce duk da cewa tsarin zaben Amurka yana da sarkakkiya kuma ya yi nisa, yana mamakin yaushe ne Nijeriya za ta kawo karshen shugabanni masu tsatsauran ra’ayi da ke amfani da karfin mulki da jami’an tsaro wajen mulkin kama karya wanda ‘yan adawa kan iya kayar da jam’iyya mai mulki kai tsaye.

 

Sai dai daraktan yada labarai na jam’iyyar APC na kasa, Bala Ibrahim ya gargadi ‘yan adawa da ka da su bari sakamakon zaben Amurka ya yaudare su, yana mai cewa tsarin zabe a tsakanin kasashen biyu ya sha bamban.

 

Bala, wanda ya bayyana haka a zantarsa da manema labarai, ya bayyana cewa ba a ko da yaushe karfin mulki ke tasiri ba, lokacin da jama’a suka yi magana da murya daya kamar yadda aka shaida nasarar da tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya samu kan shugaba mai ci, Goodluck Jonathan a 2015.

 

Mai magana da yawun jam’iyyar APC ya bayyana yakinin cewa a lokacin da ‘yan Nijeriya za su fara karbar tukuicin gyare-gyaren tattalin arzikin da shugaban kasa ya yi, za su yaba masa tare da bukatar ya ci gaba da wa’adi na biyu.

 

Ya ce, “Yadda wannan gwamnatin ta APC ke aiki tukuru, ta kawo sabbin gyare-gyare da sauye-sauye da ke da daci, za mu ci riba sosai a nan gaba.

 

“Muna sa ran fara ganin amfanin wadannan sauye-sauye kafin lokacin zabe. Wato a kusa da 2026 da 2027. A lokacin ne mutane za su fara yaba wa jam’iyya da shugaban kasa.

 

“Ba zai yi wuya wani ya fito daga waje ba, musamman wani bare da ya gaza a baya, ko wani baren da ya kasa sawo kan rikicin cikin gidansa kuma ya yi tunanin kayar da mai mulki. Zai yi wahala sosai. Jam’iyyar APC da shugaban kasa suna da masaniya kan wannan zagon kasa da ‘yan adawa ke shirya musu.

 

“Amma ba wai a ce jam’iyya da shugaban kasa suna barci ba. A’a, suna yin dabarun da za a samu sakamako nan gaba. Don haka, idan muka kai gabar, za mu ga wanda ya fi karfin ketare ta. Kuma ina tabbatar muku da cewa, APC ne za ta lashe zaben shugaban kasa a 2027 a Nijeriya.”

APC
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
APC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Tashar Chancay: Sabon Mafari Ne Ga “Tsohuwar Hanyar Inca A Sabon Zamani”

Tashar Chancay: Sabon Mafari Ne Ga “Tsohuwar Hanyar Inca A Sabon Zamani"

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.