ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Shakka Babu Tinubu Ne Zai Lashe Zaben Shugaban Kasa A 2027 – APC

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
2 years ago
APC

Jam’iyyar APC mai mulki ta gargadi jam’iyyun adawa a Nijeriya ka da su yi zumudin kan kayen da aka yi wa Kamala Harris, a zaben shugaban kasar Amurka, inda ta ce ko shakka babu Shugaba Bola Tinubu zai sake lashe zaben shugaban kasa a shekarar 2027.

 

A ranar Laraba ne aka sanar da tsohon shugaban kasar Amurka, Donald Trump a matsayin wanda ya lashe zaben Amurka, bayan da ya doke Harris a wani gagarumin siyasa da ya jefa fargaba a duniya.

ADVERTISEMENT
  • Mizanin Hajoji Da Hidimomi Da Masana’antun Kasar Sin Ke Samarwa Ya Karu Da Kaso 5.3 Bisa Dari A Watan Oktoba
  • Kudirin Sake Fasalin Haraji Ya Raba Kan ‘Yan Majalisar Arewa

Dan kasuwan mai shekaru 78 a duniya ya zama shugaban kasa na 47, kuma shi ne mutum mafi tsufa da ya taba lashe zaben Amurka.

 

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

Da yake mayar da martani, sakataren yada labarai na jam’iyyar LP, Obiora Ifo, ya bayyana zaben Amurka da aka sa ido a duk duniya a matsayin gwajin dimokuradiyya na gaskiya.

 

Yayin da yake bayyana cewa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) tana da darrusa masu yawa da za ta koya daga zaben Amurka, Ifoh ya ce, abin sha’awa ne ganin yadda Amurkawa masu kada kuri’a suka yi biris da jam’iyya mai mulki, wanda har yanzu shi ne tasiri a zaben Afirka, musamman a Nijeriya.

 

Shi ma da yake mayar da martini kan zaben Amurkan, mai magana da yawun jam’iyyar NNPP, Ladipo Johnson, ya ce duk da cewa tsarin zaben Amurka yana da sarkakkiya kuma ya yi nisa, yana mamakin yaushe ne Nijeriya za ta kawo karshen shugabanni masu tsatsauran ra’ayi da ke amfani da karfin mulki da jami’an tsaro wajen mulkin kama karya wanda ‘yan adawa kan iya kayar da jam’iyya mai mulki kai tsaye.

 

Sai dai daraktan yada labarai na jam’iyyar APC na kasa, Bala Ibrahim ya gargadi ‘yan adawa da ka da su bari sakamakon zaben Amurka ya yaudare su, yana mai cewa tsarin zabe a tsakanin kasashen biyu ya sha bamban.

 

Bala, wanda ya bayyana haka a zantarsa da manema labarai, ya bayyana cewa ba a ko da yaushe karfin mulki ke tasiri ba, lokacin da jama’a suka yi magana da murya daya kamar yadda aka shaida nasarar da tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya samu kan shugaba mai ci, Goodluck Jonathan a 2015.

 

Mai magana da yawun jam’iyyar APC ya bayyana yakinin cewa a lokacin da ‘yan Nijeriya za su fara karbar tukuicin gyare-gyaren tattalin arzikin da shugaban kasa ya yi, za su yaba masa tare da bukatar ya ci gaba da wa’adi na biyu.

 

Ya ce, “Yadda wannan gwamnatin ta APC ke aiki tukuru, ta kawo sabbin gyare-gyare da sauye-sauye da ke da daci, za mu ci riba sosai a nan gaba.

 

“Muna sa ran fara ganin amfanin wadannan sauye-sauye kafin lokacin zabe. Wato a kusa da 2026 da 2027. A lokacin ne mutane za su fara yaba wa jam’iyya da shugaban kasa.

 

“Ba zai yi wuya wani ya fito daga waje ba, musamman wani bare da ya gaza a baya, ko wani baren da ya kasa sawo kan rikicin cikin gidansa kuma ya yi tunanin kayar da mai mulki. Zai yi wahala sosai. Jam’iyyar APC da shugaban kasa suna da masaniya kan wannan zagon kasa da ‘yan adawa ke shirya musu.

 

“Amma ba wai a ce jam’iyya da shugaban kasa suna barci ba. A’a, suna yin dabarun da za a samu sakamako nan gaba. Don haka, idan muka kai gabar, za mu ga wanda ya fi karfin ketare ta. Kuma ina tabbatar muku da cewa, APC ne za ta lashe zaben shugaban kasa a 2027 a Nijeriya.”

APC
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa
APC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Tashar Chancay: Sabon Mafari Ne Ga “Tsohuwar Hanyar Inca A Sabon Zamani”

Tashar Chancay: Sabon Mafari Ne Ga “Tsohuwar Hanyar Inca A Sabon Zamani"

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.