ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Kasashen Afirka Bisa Hadin Gwiwar Raya Ayyukan Gona Na Zamani

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
Sin

An sake samun girbi mai armashi a kasar Sin! Alkaluman da hukumar kididdiga ta kasar Sin ta samar a kwanan nan sun nuna cewa, a shekarar 2025 da ta gabata, yawan hatsin da aka girbe a kasar ya kai tan miliyan 714 da dubu 880, wanda ya karu da kaso 1.2% bisa shekarar da ta gabace ta. Shekaru biyu a jere ke nan kasar Sin ta kai ga girbe hatsi sama da ton miliyan 700.

Hakan ya faru ne sakamakon yadda kasar Sin take matukar dora muhimmanci a kan raya noma da karkara da kuma manoma, wanda kuma ya samu shaida daga “kundinta mai lamba ta farko” da ta kan bayar a farkon kowace shekara. Kasancewarsa kundin gwamnati da ya shafi manufofinta, kundin ya yi ta nuna alkiblar da za a bi wajen raya abubuwan da suka shafi noma da karkara da kuma manoma. A jiya Talata, kasar Sin ta fitar da  “kundinta mai lamba ta farko” na shekarar 2026, inda ta bayyana tsare-tsaren bunkasa zamanantar da noma da yankunan karkara da kuma inganta raya karkara a dukkan fannoni. Tun daga shekarun 1980 zuwa yanzu, shekaru sama da 40 a jere ke nan, kundin mai lamba ta farko da kasar Sin ta bayar yake daukar jigon da ya shafi noma da karkara da kuma manoma, matakin da ya shaida muhimmancin ayyukan raya noma da karkara da kuma manoma ga kasar Sin.

Amma me ya sa kasar Sin ke dora matukar muhimmanci a kan raya noma da karkara da kuma manoma? Amsa ita ce sabo da kasar Sin kasa ce da ke da al’umma biliyan 1.4, kuma daga cikinsu kaso 1/3 manoma ne. Don haka, batun noma da karkara da kuma manoma, ba kawai yana shafar samar da isasshen abinci ga ‘yan kasar ba ne, hatta ma yana da alaka da zamanantarwar kasar baki daya.

ADVERTISEMENT

Noma tushen arzki, abin hakan yake. A nahiyar Afirka, musamman kasashen da ke kudu da hamadar Sahara, ayyukan noma kan dauki sama da kaso 30% daga cikin jimillar karfin tattalin arziki ta GDP, yayin da sama da kaso 70% na al’ummomin da suke da ayyukan yi suna gudanar da sana’o’i ne da suka shafi noma. Don haka ma, batun raya noma da karkara da kuma manoma su ma suna taka muhimmiyar rawa wurin daidaita matsalolin da kasashen suke fuskanta ta fannonin abinci da saukaka fatara da ma zamanantar da kansu.

Kasancewarta kasa mai tasowa mafi girma a duniya, kullum kasar Sin na kallon kanta da kasashen Afirka a matsayin al’ummu mai makoma ta bai-daya, abin da ya sa take kokarin bayyana dabarunta da ma damammakinta ga kasashen Afirka a lokacin da take bunkasa kanta ta fannonin noma da karkara da ma manoma. A gun taron kolin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka da ya gudana a shekarar 2024 a birnin Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sanar da wasu matakai 10 na hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka wajen zamanantar da kansu, ciki har da matakin da ya shafi bunkasa ayyukan noma, wato za a samar da gudummawar hatsi na kimanin kudin Sin yuan biliyan daya ga kasashen Afirka cikin gaggawa, da kafa yankunan nune-nunen fasahohin noma da tura masanan ayyukan noma 500 zuwa kasashen Afirka da kafa kawancen kirkire-kirkiren fasahohin noma a tsakanin Sin da kasashen Afirka da dai sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

In mun ba da misali da Nijeriya, cibiyar nune-nunen fasahohin noma da kasar Sin ta gina a kasar ta hada hannu da cibiyar nazarin fasahar noma ta kasar Sin da sauran cibiyoyin nazari wajen ayyukan inganta ire-iren shinkafa da rogo da gyada da sauran amfanin gona, kuma sabon nau’in shinkafar da ta kirkiro na iya samar da karin shinkafa na sama da kaso 20%, wanda har ya amfanar da manoma sama da dubu 200. A sa’i daya kuma, kamfanonin kasar Sin suna kokarin shiga ayyukan ban ruwa a kasar, wadanda har suka gina manyan tsarukan ban ruwa a jihohin Kano da Gombe da kuma Jigawa, wadanda suka shafi gonaki masu fadin eka dubu 22. Ban da haka, ta hanyar shirya kwasa-kwasai iri iri, kasar Sin ta taimaka wajen horar da dimbin kwararrun ayyukan gona ga Nijeriya.

Bana ta kasance shekarar da kasar Sin za ta fara aiwatar da shirinta na raya tattalin arziki da zaman al’umma na shekaru biyar biyar karo na 15, haka kuma wani sabon mafari ne a kokarinta na zamanantar da kanta. Kasancewarsu kawayen juna, kasar Sin za ta rika bayar da cin gajiyar nasarorinta ga aminanta na Afirka wajen zamanantar da ayyukan noma, don su cimma burinsu na zamanantar da kansu. (Lubabatu Lei)

 

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa
  • Sulaiman
    Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass
  • Sulaiman
    Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Mutum 3 Sun Rasu, 15 Sun Jikkata A Wani Hadarin Mota A Hanyar Kano

Mutane 597 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Cikin Wata 1 — FRSC

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

An Kama Uwa Da Abokiyar Burminta Kan Kisan Jariri A Jihar Yobe

June 27, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Manoma 2,930 Buhun Taki 11,720 A Abuja

June 27, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Jam’iyyun Adawa Na Cikin Tsoron Soke Rajistarsu – Baba-Ahmed

Jam’iyyun Adawa Na Cikin Tsoron Soke Rajistarsu – Baba-Ahmed

June 27, 2026
Sin

Ku Gaggauta Fara Yin Shuka A Kakar Bana: Saƙon Hukumar NiMet Ga Manoma

June 27, 2026
Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji

Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji

June 27, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

Bidiyo: Turji Ya Yi Iƙirarin Ɗaukar Alhakin Kashe Wasu Sojoji

June 27, 2026
Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

June 26, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A  Titin Bypass

Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass

June 26, 2026
Disu

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.