ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Kasashen Afirka Bisa Hadin Gwiwar Raya Ayyukan Gona Na Zamani

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
Sin

An sake samun girbi mai armashi a kasar Sin! Alkaluman da hukumar kididdiga ta kasar Sin ta samar a kwanan nan sun nuna cewa, a shekarar 2025 da ta gabata, yawan hatsin da aka girbe a kasar ya kai tan miliyan 714 da dubu 880, wanda ya karu da kaso 1.2% bisa shekarar da ta gabace ta. Shekaru biyu a jere ke nan kasar Sin ta kai ga girbe hatsi sama da ton miliyan 700.

Hakan ya faru ne sakamakon yadda kasar Sin take matukar dora muhimmanci a kan raya noma da karkara da kuma manoma, wanda kuma ya samu shaida daga “kundinta mai lamba ta farko” da ta kan bayar a farkon kowace shekara. Kasancewarsa kundin gwamnati da ya shafi manufofinta, kundin ya yi ta nuna alkiblar da za a bi wajen raya abubuwan da suka shafi noma da karkara da kuma manoma. A jiya Talata, kasar Sin ta fitar da  “kundinta mai lamba ta farko” na shekarar 2026, inda ta bayyana tsare-tsaren bunkasa zamanantar da noma da yankunan karkara da kuma inganta raya karkara a dukkan fannoni. Tun daga shekarun 1980 zuwa yanzu, shekaru sama da 40 a jere ke nan, kundin mai lamba ta farko da kasar Sin ta bayar yake daukar jigon da ya shafi noma da karkara da kuma manoma, matakin da ya shaida muhimmancin ayyukan raya noma da karkara da kuma manoma ga kasar Sin.

Amma me ya sa kasar Sin ke dora matukar muhimmanci a kan raya noma da karkara da kuma manoma? Amsa ita ce sabo da kasar Sin kasa ce da ke da al’umma biliyan 1.4, kuma daga cikinsu kaso 1/3 manoma ne. Don haka, batun noma da karkara da kuma manoma, ba kawai yana shafar samar da isasshen abinci ga ‘yan kasar ba ne, hatta ma yana da alaka da zamanantarwar kasar baki daya.

ADVERTISEMENT

Noma tushen arzki, abin hakan yake. A nahiyar Afirka, musamman kasashen da ke kudu da hamadar Sahara, ayyukan noma kan dauki sama da kaso 30% daga cikin jimillar karfin tattalin arziki ta GDP, yayin da sama da kaso 70% na al’ummomin da suke da ayyukan yi suna gudanar da sana’o’i ne da suka shafi noma. Don haka ma, batun raya noma da karkara da kuma manoma su ma suna taka muhimmiyar rawa wurin daidaita matsalolin da kasashen suke fuskanta ta fannonin abinci da saukaka fatara da ma zamanantar da kansu.

Kasancewarta kasa mai tasowa mafi girma a duniya, kullum kasar Sin na kallon kanta da kasashen Afirka a matsayin al’ummu mai makoma ta bai-daya, abin da ya sa take kokarin bayyana dabarunta da ma damammakinta ga kasashen Afirka a lokacin da take bunkasa kanta ta fannonin noma da karkara da ma manoma. A gun taron kolin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka da ya gudana a shekarar 2024 a birnin Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sanar da wasu matakai 10 na hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka wajen zamanantar da kansu, ciki har da matakin da ya shafi bunkasa ayyukan noma, wato za a samar da gudummawar hatsi na kimanin kudin Sin yuan biliyan daya ga kasashen Afirka cikin gaggawa, da kafa yankunan nune-nunen fasahohin noma da tura masanan ayyukan noma 500 zuwa kasashen Afirka da kafa kawancen kirkire-kirkiren fasahohin noma a tsakanin Sin da kasashen Afirka da dai sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

In mun ba da misali da Nijeriya, cibiyar nune-nunen fasahohin noma da kasar Sin ta gina a kasar ta hada hannu da cibiyar nazarin fasahar noma ta kasar Sin da sauran cibiyoyin nazari wajen ayyukan inganta ire-iren shinkafa da rogo da gyada da sauran amfanin gona, kuma sabon nau’in shinkafar da ta kirkiro na iya samar da karin shinkafa na sama da kaso 20%, wanda har ya amfanar da manoma sama da dubu 200. A sa’i daya kuma, kamfanonin kasar Sin suna kokarin shiga ayyukan ban ruwa a kasar, wadanda har suka gina manyan tsarukan ban ruwa a jihohin Kano da Gombe da kuma Jigawa, wadanda suka shafi gonaki masu fadin eka dubu 22. Ban da haka, ta hanyar shirya kwasa-kwasai iri iri, kasar Sin ta taimaka wajen horar da dimbin kwararrun ayyukan gona ga Nijeriya.

Bana ta kasance shekarar da kasar Sin za ta fara aiwatar da shirinta na raya tattalin arziki da zaman al’umma na shekaru biyar biyar karo na 15, haka kuma wani sabon mafari ne a kokarinta na zamanantar da kanta. Kasancewarsu kawayen juna, kasar Sin za ta rika bayar da cin gajiyar nasarorinta ga aminanta na Afirka wajen zamanantar da ayyukan noma, don su cimma burinsu na zamanantar da kansu. (Lubabatu Lei)

 

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Mutum 3 Sun Rasu, 15 Sun Jikkata A Wani Hadarin Mota A Hanyar Kano

Mutane 597 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Cikin Wata 1 — FRSC

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.