ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Kasashen Afirka Bisa Hadin Gwiwar Raya Ayyukan Gona Na Zamani

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
Sin

An sake samun girbi mai armashi a kasar Sin! Alkaluman da hukumar kididdiga ta kasar Sin ta samar a kwanan nan sun nuna cewa, a shekarar 2025 da ta gabata, yawan hatsin da aka girbe a kasar ya kai tan miliyan 714 da dubu 880, wanda ya karu da kaso 1.2% bisa shekarar da ta gabace ta. Shekaru biyu a jere ke nan kasar Sin ta kai ga girbe hatsi sama da ton miliyan 700.

Hakan ya faru ne sakamakon yadda kasar Sin take matukar dora muhimmanci a kan raya noma da karkara da kuma manoma, wanda kuma ya samu shaida daga “kundinta mai lamba ta farko” da ta kan bayar a farkon kowace shekara. Kasancewarsa kundin gwamnati da ya shafi manufofinta, kundin ya yi ta nuna alkiblar da za a bi wajen raya abubuwan da suka shafi noma da karkara da kuma manoma. A jiya Talata, kasar Sin ta fitar da  “kundinta mai lamba ta farko” na shekarar 2026, inda ta bayyana tsare-tsaren bunkasa zamanantar da noma da yankunan karkara da kuma inganta raya karkara a dukkan fannoni. Tun daga shekarun 1980 zuwa yanzu, shekaru sama da 40 a jere ke nan, kundin mai lamba ta farko da kasar Sin ta bayar yake daukar jigon da ya shafi noma da karkara da kuma manoma, matakin da ya shaida muhimmancin ayyukan raya noma da karkara da kuma manoma ga kasar Sin.

Amma me ya sa kasar Sin ke dora matukar muhimmanci a kan raya noma da karkara da kuma manoma? Amsa ita ce sabo da kasar Sin kasa ce da ke da al’umma biliyan 1.4, kuma daga cikinsu kaso 1/3 manoma ne. Don haka, batun noma da karkara da kuma manoma, ba kawai yana shafar samar da isasshen abinci ga ‘yan kasar ba ne, hatta ma yana da alaka da zamanantarwar kasar baki daya.

ADVERTISEMENT

Noma tushen arzki, abin hakan yake. A nahiyar Afirka, musamman kasashen da ke kudu da hamadar Sahara, ayyukan noma kan dauki sama da kaso 30% daga cikin jimillar karfin tattalin arziki ta GDP, yayin da sama da kaso 70% na al’ummomin da suke da ayyukan yi suna gudanar da sana’o’i ne da suka shafi noma. Don haka ma, batun raya noma da karkara da kuma manoma su ma suna taka muhimmiyar rawa wurin daidaita matsalolin da kasashen suke fuskanta ta fannonin abinci da saukaka fatara da ma zamanantar da kansu.

Kasancewarta kasa mai tasowa mafi girma a duniya, kullum kasar Sin na kallon kanta da kasashen Afirka a matsayin al’ummu mai makoma ta bai-daya, abin da ya sa take kokarin bayyana dabarunta da ma damammakinta ga kasashen Afirka a lokacin da take bunkasa kanta ta fannonin noma da karkara da ma manoma. A gun taron kolin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka da ya gudana a shekarar 2024 a birnin Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sanar da wasu matakai 10 na hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka wajen zamanantar da kansu, ciki har da matakin da ya shafi bunkasa ayyukan noma, wato za a samar da gudummawar hatsi na kimanin kudin Sin yuan biliyan daya ga kasashen Afirka cikin gaggawa, da kafa yankunan nune-nunen fasahohin noma da tura masanan ayyukan noma 500 zuwa kasashen Afirka da kafa kawancen kirkire-kirkiren fasahohin noma a tsakanin Sin da kasashen Afirka da dai sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

In mun ba da misali da Nijeriya, cibiyar nune-nunen fasahohin noma da kasar Sin ta gina a kasar ta hada hannu da cibiyar nazarin fasahar noma ta kasar Sin da sauran cibiyoyin nazari wajen ayyukan inganta ire-iren shinkafa da rogo da gyada da sauran amfanin gona, kuma sabon nau’in shinkafar da ta kirkiro na iya samar da karin shinkafa na sama da kaso 20%, wanda har ya amfanar da manoma sama da dubu 200. A sa’i daya kuma, kamfanonin kasar Sin suna kokarin shiga ayyukan ban ruwa a kasar, wadanda har suka gina manyan tsarukan ban ruwa a jihohin Kano da Gombe da kuma Jigawa, wadanda suka shafi gonaki masu fadin eka dubu 22. Ban da haka, ta hanyar shirya kwasa-kwasai iri iri, kasar Sin ta taimaka wajen horar da dimbin kwararrun ayyukan gona ga Nijeriya.

Bana ta kasance shekarar da kasar Sin za ta fara aiwatar da shirinta na raya tattalin arziki da zaman al’umma na shekaru biyar biyar karo na 15, haka kuma wani sabon mafari ne a kokarinta na zamanantar da kanta. Kasancewarsu kawayen juna, kasar Sin za ta rika bayar da cin gajiyar nasarorinta ga aminanta na Afirka wajen zamanantar da ayyukan noma, don su cimma burinsu na zamanantar da kansu. (Lubabatu Lei)

 

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri
  • Sulaiman
    Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK
  • Sulaiman
    Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA
  • Sulaiman
    Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

MASU ALAKA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Next Post
Mutum 3 Sun Rasu, 15 Sun Jikkata A Wani Hadarin Mota A Hanyar Kano

Mutane 597 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Cikin Wata 1 — FRSC

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

July 18, 2026
Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

July 18, 2026
Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

July 18, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.