ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Sake Ci Gaba Da Shari’ar ‘Yan Bindiga Biyar Masu Alaka Da Bello Turji

by Leadership Hausa
5 months ago

Babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta amince da bukatar gwamnatin tarayya na sake bude tuhumar ta’addanci kan wasu mutane biyar da ake zargi da alaka da fitaccen shugaban ‘yan ta’adda, Bello Turji.

Mai shari’a Emeka Nwite, a cikin hukuncin da ya yanke a ranar Litinin, ya amince da bukatar da babban mai shari’a na kasa (AGF) ya gabatar na neman a sake shigar da kara mai lamba FHC/ABJ/CR/633/2024, a jerin dalilan kotun.

  • Sheikh Al-Sudais Ya Gargadi Masu Ibadah Kan Kiyaye Darajar Masallatan Harami
  • Mutane 5 Sun Rasu, 35 Sun Jikkata A Harin Bam A Masallaci A Borno

An dai ci gaba da shari’ar ne, a ranar 8 ga watan Yulin 2025, bayan lauyan da ke kare wanda ake tuhuma ya nemi a kori karar, saboda zargin rashin gurfanar da shi a gaban kotu.

ADVERTISEMENT

Mai gabatar da kara, ta bakin lauyan AGF, Dabid Kaswe, ya bayar da hujjar cewa; masu gabatar da kara ba su kare dage zaman da aka yi ba, sannan kuma a shirye suke tsaf, domin gabatar da shaidu.

Laifukan ta’addanci 11 da aka shigar a farko a ranar 16 ga watan Disamba, 2024, ya shafi mutane takwas da ake tuhuma da suka hada da Musa Muhammed Kamarawa, Abubakar Hashimu (wanda aka fi sani da Dakta), Bashir Abdullahi, Samuel Chinedu da Lucky Chukwuma, wadanda a halin yanzu suke tsare. Sai dai, Bello Turji da Aminu Muhammad da Sani Lawal suna nan a matsayin manyan jagororinsu.

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Ana zargin wadanda ake zargin da bayar da tallafin kayan aiki ga kungiyoyin ‘yan ta’adda da Turji ke jagoranta da sauran ‘yan fashi da suka hada da samar da haramtattun kwayoyi, abinci, kayan soja da na ‘yansanda, kayayyakin gine-gine, har ma da samar da wata motar yaki da ake amfani da ita wajen ayyukan ta’addanci.

A yayin shari’ar, Kaswe ya ci gaba da cewa; rashin halartar masu gabatar da kara a ranar 8 ga watan Yuli, ya faru ne sakamakon wani aiki a hukumance; ba da gangan ba, yana mai jaddada muhimmancin sake shigar da karar, domin tabbatar da adalci, tsaron kasa da kare lafiyar jama’a.

Lauyan wadanda ake kara na 1 da na 2, Lukman bai yi adawa da bukatar ba, sai dai ya bukaci a biya shi Naira miliyan 10 a kan masu gabatar da kara, saboda tsawaita tsare wadanda ake tuhuma a lokacin shari’ar.

A hukuncin da ya yanke, Mai shari’a Nwite ya bayyana cewa; bukatar da gwamnatin tarayya ta gabatar, ta dace kuma ta amince da shi, inda ta ba da umarnin a ci gaba da shari’ar ba tare da biyan wasu kudade ba.

An dage ci gaba da sauraren karar har zuwa ranar 21 ga watan Janairun 2026.

Shari’ar dai, ta bayyana kokarin da hukumomin Nijeriya ke ci gaba da yi na gurfanar da ta’addanci a sassan duniya da kuma karfafa daukar nauyin tallafin kayan aiki ga haramtattun kungiyoyi.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Binciken CGTN: 80% Na Matasan Duniya Sun Yi Kiran Maida Hankali Kan Karin Kasafin Kudin Tsaron Kasar Japan

Binciken CGTN: 80% Na Matasan Duniya Sun Yi Kiran Maida Hankali Kan Karin Kasafin Kudin Tsaron Kasar Japan

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.