ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Sake Ci Gaba Da Shari’ar ‘Yan Bindiga Biyar Masu Alaka Da Bello Turji

by Leadership Hausa
9 months ago

Babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta amince da bukatar gwamnatin tarayya na sake bude tuhumar ta’addanci kan wasu mutane biyar da ake zargi da alaka da fitaccen shugaban ‘yan ta’adda, Bello Turji.

Mai shari’a Emeka Nwite, a cikin hukuncin da ya yanke a ranar Litinin, ya amince da bukatar da babban mai shari’a na kasa (AGF) ya gabatar na neman a sake shigar da kara mai lamba FHC/ABJ/CR/633/2024, a jerin dalilan kotun.

  • Sheikh Al-Sudais Ya Gargadi Masu Ibadah Kan Kiyaye Darajar Masallatan Harami
  • Mutane 5 Sun Rasu, 35 Sun Jikkata A Harin Bam A Masallaci A Borno

An dai ci gaba da shari’ar ne, a ranar 8 ga watan Yulin 2025, bayan lauyan da ke kare wanda ake tuhuma ya nemi a kori karar, saboda zargin rashin gurfanar da shi a gaban kotu.

ADVERTISEMENT

Mai gabatar da kara, ta bakin lauyan AGF, Dabid Kaswe, ya bayar da hujjar cewa; masu gabatar da kara ba su kare dage zaman da aka yi ba, sannan kuma a shirye suke tsaf, domin gabatar da shaidu.

Laifukan ta’addanci 11 da aka shigar a farko a ranar 16 ga watan Disamba, 2024, ya shafi mutane takwas da ake tuhuma da suka hada da Musa Muhammed Kamarawa, Abubakar Hashimu (wanda aka fi sani da Dakta), Bashir Abdullahi, Samuel Chinedu da Lucky Chukwuma, wadanda a halin yanzu suke tsare. Sai dai, Bello Turji da Aminu Muhammad da Sani Lawal suna nan a matsayin manyan jagororinsu.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Ana zargin wadanda ake zargin da bayar da tallafin kayan aiki ga kungiyoyin ‘yan ta’adda da Turji ke jagoranta da sauran ‘yan fashi da suka hada da samar da haramtattun kwayoyi, abinci, kayan soja da na ‘yansanda, kayayyakin gine-gine, har ma da samar da wata motar yaki da ake amfani da ita wajen ayyukan ta’addanci.

A yayin shari’ar, Kaswe ya ci gaba da cewa; rashin halartar masu gabatar da kara a ranar 8 ga watan Yuli, ya faru ne sakamakon wani aiki a hukumance; ba da gangan ba, yana mai jaddada muhimmancin sake shigar da karar, domin tabbatar da adalci, tsaron kasa da kare lafiyar jama’a.

Lauyan wadanda ake kara na 1 da na 2, Lukman bai yi adawa da bukatar ba, sai dai ya bukaci a biya shi Naira miliyan 10 a kan masu gabatar da kara, saboda tsawaita tsare wadanda ake tuhuma a lokacin shari’ar.

A hukuncin da ya yanke, Mai shari’a Nwite ya bayyana cewa; bukatar da gwamnatin tarayya ta gabatar, ta dace kuma ta amince da shi, inda ta ba da umarnin a ci gaba da shari’ar ba tare da biyan wasu kudade ba.

An dage ci gaba da sauraren karar har zuwa ranar 21 ga watan Janairun 2026.

Shari’ar dai, ta bayyana kokarin da hukumomin Nijeriya ke ci gaba da yi na gurfanar da ta’addanci a sassan duniya da kuma karfafa daukar nauyin tallafin kayan aiki ga haramtattun kungiyoyi.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Binciken CGTN: 80% Na Matasan Duniya Sun Yi Kiran Maida Hankali Kan Karin Kasafin Kudin Tsaron Kasar Japan

Binciken CGTN: 80% Na Matasan Duniya Sun Yi Kiran Maida Hankali Kan Karin Kasafin Kudin Tsaron Kasar Japan

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.