ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Sake Ci Gaba Da Shari’ar ‘Yan Bindiga Biyar Masu Alaka Da Bello Turji

by Leadership Hausa
7 months ago

Babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta amince da bukatar gwamnatin tarayya na sake bude tuhumar ta’addanci kan wasu mutane biyar da ake zargi da alaka da fitaccen shugaban ‘yan ta’adda, Bello Turji.

Mai shari’a Emeka Nwite, a cikin hukuncin da ya yanke a ranar Litinin, ya amince da bukatar da babban mai shari’a na kasa (AGF) ya gabatar na neman a sake shigar da kara mai lamba FHC/ABJ/CR/633/2024, a jerin dalilan kotun.

  • Sheikh Al-Sudais Ya Gargadi Masu Ibadah Kan Kiyaye Darajar Masallatan Harami
  • Mutane 5 Sun Rasu, 35 Sun Jikkata A Harin Bam A Masallaci A Borno

An dai ci gaba da shari’ar ne, a ranar 8 ga watan Yulin 2025, bayan lauyan da ke kare wanda ake tuhuma ya nemi a kori karar, saboda zargin rashin gurfanar da shi a gaban kotu.

ADVERTISEMENT

Mai gabatar da kara, ta bakin lauyan AGF, Dabid Kaswe, ya bayar da hujjar cewa; masu gabatar da kara ba su kare dage zaman da aka yi ba, sannan kuma a shirye suke tsaf, domin gabatar da shaidu.

Laifukan ta’addanci 11 da aka shigar a farko a ranar 16 ga watan Disamba, 2024, ya shafi mutane takwas da ake tuhuma da suka hada da Musa Muhammed Kamarawa, Abubakar Hashimu (wanda aka fi sani da Dakta), Bashir Abdullahi, Samuel Chinedu da Lucky Chukwuma, wadanda a halin yanzu suke tsare. Sai dai, Bello Turji da Aminu Muhammad da Sani Lawal suna nan a matsayin manyan jagororinsu.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Ana zargin wadanda ake zargin da bayar da tallafin kayan aiki ga kungiyoyin ‘yan ta’adda da Turji ke jagoranta da sauran ‘yan fashi da suka hada da samar da haramtattun kwayoyi, abinci, kayan soja da na ‘yansanda, kayayyakin gine-gine, har ma da samar da wata motar yaki da ake amfani da ita wajen ayyukan ta’addanci.

A yayin shari’ar, Kaswe ya ci gaba da cewa; rashin halartar masu gabatar da kara a ranar 8 ga watan Yuli, ya faru ne sakamakon wani aiki a hukumance; ba da gangan ba, yana mai jaddada muhimmancin sake shigar da karar, domin tabbatar da adalci, tsaron kasa da kare lafiyar jama’a.

Lauyan wadanda ake kara na 1 da na 2, Lukman bai yi adawa da bukatar ba, sai dai ya bukaci a biya shi Naira miliyan 10 a kan masu gabatar da kara, saboda tsawaita tsare wadanda ake tuhuma a lokacin shari’ar.

A hukuncin da ya yanke, Mai shari’a Nwite ya bayyana cewa; bukatar da gwamnatin tarayya ta gabatar, ta dace kuma ta amince da shi, inda ta ba da umarnin a ci gaba da shari’ar ba tare da biyan wasu kudade ba.

An dage ci gaba da sauraren karar har zuwa ranar 21 ga watan Janairun 2026.

Shari’ar dai, ta bayyana kokarin da hukumomin Nijeriya ke ci gaba da yi na gurfanar da ta’addanci a sassan duniya da kuma karfafa daukar nauyin tallafin kayan aiki ga haramtattun kungiyoyi.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Binciken CGTN: 80% Na Matasan Duniya Sun Yi Kiran Maida Hankali Kan Karin Kasafin Kudin Tsaron Kasar Japan

Binciken CGTN: 80% Na Matasan Duniya Sun Yi Kiran Maida Hankali Kan Karin Kasafin Kudin Tsaron Kasar Japan

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.