Wata Babbar Kotun Tarayya da ke Jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin Mai shari’a S.M Shuaibu, ta yanke wa jarumar Kannywood, Saadatu Mohammed Inuwa (wadda aka fi sani da Samha) hukuncin ɗaurin watanni shida bisa laifin wulaƙanta takardar Naira.
Kotun ta ce ta wulaƙanta takardar Naira ₦1,000 da jarumar ta yi a shekarar 2022 ta hanyar goge hanci da ita, ya saɓa wa dokar Babban Bankin Nijeriya (CBN).
- Karfafa Tsarin Kimiyyar Fintech A Nijeriya
- Sin Da Amurka Na Ci Gaba Da Musayar Bayanan Sirri Kan Yaki Da Miyagun Kwayoyi
An gurfanar da ita kan laifi guda ɗaya, kuma ta amsa laifinta a kotu.
Bayan mai gabatar da ƙara ya yi bayani, ta roƙi kotu ta tausaya mata, inda ta bayyana cewa wannan ne karon farko da ta aikata irin wannan laifi kuma ta yi nadama.
Daga nan ne Mai shari’a ya yanke mata hukuncin ɗaurin watanni shida, tare da zaɓin biyan tarar Naira 200,000 maimakon zaman gidan yari.















Discussion about this post