Kotun Ƙoli ta tabbatar da hukuncin kisa da aka yanke wa Maryam Sanda kan kashe mijinta, Bilyaminu Bello, a rikicin cikin gida da ya faru shekaru takwas da suka gabata. A 2020 ne babbar kotu a FCT ta yanke mata hukuncin kisa ta hanyar rataya, duk da cewa daga baya Shugaba Bola Tinubu ya rage hukuncin zuwa shekaru 12 a kurkuku bisa tausayawa.
A hukuncin da yawansu ya fi rinjaye, alkalai huɗu cikin biyar na kotun sun tabbatar da hukuncin da Kotun Ɗaukaka ƙara ta yanke, wadda ita ma ta tsaya kan hukuncin kisa da kotun farko ta ɗora mata. Kotun ta ce an gabatar da hujjoji masu ƙarfi da suka gamsar da ita cewa Maryam ta aikata laifin ne tana sane.
Mai shari’a Moore Adumein, wanda ya jagoranci yanke hukuncin, ya bayyana cewa masu gabatar da ƙara sun tabbatar da laifin ne kamar yadda doka ta tanada. Ya ce kotu ta yi daidai da ta tabbatar da hukuncin da aka fara yanke mata, domin babu hujjar da ta ƙaryata sahihancin shari’ar farko.
Alƙalin ya kuma bayyana cewa kuskure ne ɓangaren zartarwa ya yi rangwame ga hukuncin kisa yayin da har yanzu ake gaban shari’a a kotun ɗaukaka ƙara. Don haka, kotun ta kori ɗaukaka ƙarar Maryam Sanda gaba ɗaya tare da tabbatar da hukuncin kisa da kotunan ƙasa suka yanke mata.














