ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotun Ta Haramta Tilasta Allurar Rigakafi Ga Al’umma

by Yusuf Shuaibu
2 months ago
Allurar

Alƙalin babban kotun tarayya da ke Jihar Legas, Mai Shari’a Ambrose Lewis-Allagoa ya bayyana cewa tilasta gudanar da allurar rigakafi ba tare da yardar kai ba, ya saɓa wa kundin tsarin mulkin Nijeriya. Alali Lewis-Allagoa ya bayyana hakan ne a yayin da yake yanke hukunci a ƙarar tabbatar da haƙƙoƙi ɗan ƙasa da ƙungiyar ‘Eƙuity International Initiatiɓe’ ta shigar da gwamnatin Jihar Legas.

Yayin da aka amince cewa manufofin lafiyar jama’a suna da muhimmanci, kotu ta yi jawabi cewa dole ne a aiwatar da su cikin iyakokin doka da kuma girmama haƙƙi da ƴancin mutum. 

Alƙalin ya kuma tabbatar da cewa haƙƙoƙi kamar daidaiton jiki da ƴancin ƙin karɓar jiyya suna ci gaba da samun kariya ƙarƙashin dokar Nijeriya. 

ADVERTISEMENT
  • Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
  • An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • 2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Baya ga gwamnatin jiha, sauran waɗanda ake ƙara sun haɗa da hukumar lafiya matakin Farko ta Jihar Legas da kwamishinan shari’a na jihar da kwamishinan ƴansandan jihar.

Ƙungiyar ‘Eƙuity International Initiatiɓe’ ta nemi kotu ta ayyana hana tilasta yin allurorin rigakafi da jihar take bayar da umarni a kai, wanda ta zargi ana tilasta wa mutane allurar rigakafi ba tare da izininsu ba, wanda hakan ke keta haƙƙinsu na ƴan ƙasa.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

A cikin hujjojinta, mai shigar da ƙara ta bayyana cewa umarnin sun keta haƙƙoƙin ƴan ƙasa a ƙarƙashin kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999, ciki har da haƙƙoƙin rayuwa da daraja Ɗan’adam da ƴancin gudanar da rayuwa da na addini.

Haka nan ta kawo tanade-tanaden dokar ƙasa da ƙasa ta Afirka kan haƙƙoƙin Ɗan’adam da ya bai wa mutum ƴancin gudanar da rayuwa.

Kazalika, masu amsa ƙara sun ƙalubalantar ikon kotu da matsayin mai shigar da ƙara, da ingancin ƙarar.

Kotun ta ƙara bayyana cewa mai ƙara yana da isasshen hujjoji na doka don ɗaukar mataki a madadin mazauna jihar da abin ya shafa. Tana bayyana ƙarar a matsayin ingantacciyar hanyar shari’ar na muradin jama’a wadda aka sadaukar don kare haƙƙoƙin al’umma.

Alƙali Lewis-Allagoa ya ƙara ba da umarni wanda ke hana masu amsa ƙara, ko da da kansu, wakilansu, masu hulɗa da su, ma’aikata, ko wasu mutane da ke ɗaukar umarni daga gare su, aiwatar da shirin yin allurar rigakafi ga jama’a a makarantun Jihar Legas da sauran wurare.

Allurar
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
PDP Ta Bankaɗo Shirin Tsige Gwamna Makinde Na Jihar Oyo

PDP Ta Bankaɗo Shirin Tsige Gwamna Makinde Na Jihar Oyo

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.