ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotun Ta Haramta Tilasta Allurar Rigakafi Ga Al’umma

by Yusuf Shuaibu
3 months ago
Allurar

Alƙalin babban kotun tarayya da ke Jihar Legas, Mai Shari’a Ambrose Lewis-Allagoa ya bayyana cewa tilasta gudanar da allurar rigakafi ba tare da yardar kai ba, ya saɓa wa kundin tsarin mulkin Nijeriya. Alali Lewis-Allagoa ya bayyana hakan ne a yayin da yake yanke hukunci a ƙarar tabbatar da haƙƙoƙi ɗan ƙasa da ƙungiyar ‘Eƙuity International Initiatiɓe’ ta shigar da gwamnatin Jihar Legas.

Yayin da aka amince cewa manufofin lafiyar jama’a suna da muhimmanci, kotu ta yi jawabi cewa dole ne a aiwatar da su cikin iyakokin doka da kuma girmama haƙƙi da ƴancin mutum. 

Alƙalin ya kuma tabbatar da cewa haƙƙoƙi kamar daidaiton jiki da ƴancin ƙin karɓar jiyya suna ci gaba da samun kariya ƙarƙashin dokar Nijeriya. 

ADVERTISEMENT
  • ’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A Jihar Benuwai
  • Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara
  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma
  • Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI
  • Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Baya ga gwamnatin jiha, sauran waɗanda ake ƙara sun haɗa da hukumar lafiya matakin Farko ta Jihar Legas da kwamishinan shari’a na jihar da kwamishinan ƴansandan jihar.

Ƙungiyar ‘Eƙuity International Initiatiɓe’ ta nemi kotu ta ayyana hana tilasta yin allurorin rigakafi da jihar take bayar da umarni a kai, wanda ta zargi ana tilasta wa mutane allurar rigakafi ba tare da izininsu ba, wanda hakan ke keta haƙƙinsu na ƴan ƙasa.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A Jihar Benuwai

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

A cikin hujjojinta, mai shigar da ƙara ta bayyana cewa umarnin sun keta haƙƙoƙin ƴan ƙasa a ƙarƙashin kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999, ciki har da haƙƙoƙin rayuwa da daraja Ɗan’adam da ƴancin gudanar da rayuwa da na addini.

Haka nan ta kawo tanade-tanaden dokar ƙasa da ƙasa ta Afirka kan haƙƙoƙin Ɗan’adam da ya bai wa mutum ƴancin gudanar da rayuwa.

Kazalika, masu amsa ƙara sun ƙalubalantar ikon kotu da matsayin mai shigar da ƙara, da ingancin ƙarar.

Kotun ta ƙara bayyana cewa mai ƙara yana da isasshen hujjoji na doka don ɗaukar mataki a madadin mazauna jihar da abin ya shafa. Tana bayyana ƙarar a matsayin ingantacciyar hanyar shari’ar na muradin jama’a wadda aka sadaukar don kare haƙƙoƙin al’umma.

Alƙali Lewis-Allagoa ya ƙara ba da umarni wanda ke hana masu amsa ƙara, ko da da kansu, wakilansu, masu hulɗa da su, ma’aikata, ko wasu mutane da ke ɗaukar umarni daga gare su, aiwatar da shirin yin allurar rigakafi ga jama’a a makarantun Jihar Legas da sauran wurare.

Allurar
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

MASU ALAKA

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A  Jihar Benuwai
Labarai

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A Jihar Benuwai

July 9, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Next Post
PDP Ta Bankaɗo Shirin Tsige Gwamna Makinde Na Jihar Oyo

PDP Ta Bankaɗo Shirin Tsige Gwamna Makinde Na Jihar Oyo

LABARAI MASU NASABA

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A  Jihar Benuwai

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A Jihar Benuwai

July 9, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.