ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotun Ta Haramta Tilasta Allurar Rigakafi Ga Al’umma

by Yusuf Shuaibu
2 months ago
Allurar

Alƙalin babban kotun tarayya da ke Jihar Legas, Mai Shari’a Ambrose Lewis-Allagoa ya bayyana cewa tilasta gudanar da allurar rigakafi ba tare da yardar kai ba, ya saɓa wa kundin tsarin mulkin Nijeriya. Alali Lewis-Allagoa ya bayyana hakan ne a yayin da yake yanke hukunci a ƙarar tabbatar da haƙƙoƙi ɗan ƙasa da ƙungiyar ‘Eƙuity International Initiatiɓe’ ta shigar da gwamnatin Jihar Legas.

Yayin da aka amince cewa manufofin lafiyar jama’a suna da muhimmanci, kotu ta yi jawabi cewa dole ne a aiwatar da su cikin iyakokin doka da kuma girmama haƙƙi da ƴancin mutum. 

Alƙalin ya kuma tabbatar da cewa haƙƙoƙi kamar daidaiton jiki da ƴancin ƙin karɓar jiyya suna ci gaba da samun kariya ƙarƙashin dokar Nijeriya. 

ADVERTISEMENT
  • Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
  • Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
  • Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

Baya ga gwamnatin jiha, sauran waɗanda ake ƙara sun haɗa da hukumar lafiya matakin Farko ta Jihar Legas da kwamishinan shari’a na jihar da kwamishinan ƴansandan jihar.

Ƙungiyar ‘Eƙuity International Initiatiɓe’ ta nemi kotu ta ayyana hana tilasta yin allurorin rigakafi da jihar take bayar da umarni a kai, wanda ta zargi ana tilasta wa mutane allurar rigakafi ba tare da izininsu ba, wanda hakan ke keta haƙƙinsu na ƴan ƙasa.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

A cikin hujjojinta, mai shigar da ƙara ta bayyana cewa umarnin sun keta haƙƙoƙin ƴan ƙasa a ƙarƙashin kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999, ciki har da haƙƙoƙin rayuwa da daraja Ɗan’adam da ƴancin gudanar da rayuwa da na addini.

Haka nan ta kawo tanade-tanaden dokar ƙasa da ƙasa ta Afirka kan haƙƙoƙin Ɗan’adam da ya bai wa mutum ƴancin gudanar da rayuwa.

Kazalika, masu amsa ƙara sun ƙalubalantar ikon kotu da matsayin mai shigar da ƙara, da ingancin ƙarar.

Kotun ta ƙara bayyana cewa mai ƙara yana da isasshen hujjoji na doka don ɗaukar mataki a madadin mazauna jihar da abin ya shafa. Tana bayyana ƙarar a matsayin ingantacciyar hanyar shari’ar na muradin jama’a wadda aka sadaukar don kare haƙƙoƙin al’umma.

Alƙali Lewis-Allagoa ya ƙara ba da umarni wanda ke hana masu amsa ƙara, ko da da kansu, wakilansu, masu hulɗa da su, ma’aikata, ko wasu mutane da ke ɗaukar umarni daga gare su, aiwatar da shirin yin allurar rigakafi ga jama’a a makarantun Jihar Legas da sauran wurare.

Allurar
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
PDP Ta Bankaɗo Shirin Tsige Gwamna Makinde Na Jihar Oyo

PDP Ta Bankaɗo Shirin Tsige Gwamna Makinde Na Jihar Oyo

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.