Alƙalin babban kotun tarayya da ke Jihar Legas, Mai Shari’a Ambrose Lewis-Allagoa ya bayyana cewa tilasta gudanar da allurar rigakafi ba tare da yardar kai ba, ya saɓa wa kundin tsarin mulkin Nijeriya. Alali Lewis-Allagoa ya bayyana hakan ne a yayin da yake yanke hukunci a ƙarar tabbatar da haƙƙoƙi ɗan ƙasa da ƙungiyar ‘Eƙuity International Initiatiɓe’ ta shigar da gwamnatin Jihar Legas.
Yayin da aka amince cewa manufofin lafiyar jama’a suna da muhimmanci, kotu ta yi jawabi cewa dole ne a aiwatar da su cikin iyakokin doka da kuma girmama haƙƙi da ƴancin mutum.
Alƙalin ya kuma tabbatar da cewa haƙƙoƙi kamar daidaiton jiki da ƴancin ƙin karɓar jiyya suna ci gaba da samun kariya ƙarƙashin dokar Nijeriya.
- Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
- An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
- 2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
- Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
- Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Baya ga gwamnatin jiha, sauran waɗanda ake ƙara sun haɗa da hukumar lafiya matakin Farko ta Jihar Legas da kwamishinan shari’a na jihar da kwamishinan ƴansandan jihar.
Ƙungiyar ‘Eƙuity International Initiatiɓe’ ta nemi kotu ta ayyana hana tilasta yin allurorin rigakafi da jihar take bayar da umarni a kai, wanda ta zargi ana tilasta wa mutane allurar rigakafi ba tare da izininsu ba, wanda hakan ke keta haƙƙinsu na ƴan ƙasa.
A cikin hujjojinta, mai shigar da ƙara ta bayyana cewa umarnin sun keta haƙƙoƙin ƴan ƙasa a ƙarƙashin kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999, ciki har da haƙƙoƙin rayuwa da daraja Ɗan’adam da ƴancin gudanar da rayuwa da na addini.
Haka nan ta kawo tanade-tanaden dokar ƙasa da ƙasa ta Afirka kan haƙƙoƙin Ɗan’adam da ya bai wa mutum ƴancin gudanar da rayuwa.
Kazalika, masu amsa ƙara sun ƙalubalantar ikon kotu da matsayin mai shigar da ƙara, da ingancin ƙarar.
Kotun ta ƙara bayyana cewa mai ƙara yana da isasshen hujjoji na doka don ɗaukar mataki a madadin mazauna jihar da abin ya shafa. Tana bayyana ƙarar a matsayin ingantacciyar hanyar shari’ar na muradin jama’a wadda aka sadaukar don kare haƙƙoƙin al’umma.
Alƙali Lewis-Allagoa ya ƙara ba da umarni wanda ke hana masu amsa ƙara, ko da da kansu, wakilansu, masu hulɗa da su, ma’aikata, ko wasu mutane da ke ɗaukar umarni daga gare su, aiwatar da shirin yin allurar rigakafi ga jama’a a makarantun Jihar Legas da sauran wurare.















Discussion about this post