ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Ku Sha Kuruminku, Nan Gaba Kadan A Nijeriya Za A Samu Tikitin Kirista Da Kirista” —In Ji Matar Tinubu

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Tinubu

Matar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Sanata Oluremi Tinubu a ranar Laraba ta ce, tikitin Musulmi da Musulmi ya bude wani sabon salo kuma sabon babi a siyasar kasar nan a 2023.

Da take buga misali da tikitin Shugaban kasa na musulmai biyu a jam’iyyar APC da yadda hakan ke cigaba da janyo cece-kuce, matar na Tinubu ta yi fatan cewa nan gaba kuma wata rana sai an samu tikitin Kirista da Kirista biyu a kasar nan.

  • 2023: Kotu Ta Yi Watsi Da Karar Da Aka Shigar Kan Kalubalantar Takarar Tinubu

Kan hakan ne ta ce ga masu daga jijiyar wuya kan hakan da su sha kuruminsu yanzu an bude babi ne don kuwa wata rana za a samu tikitin Kirista biyu.

ADVERTISEMENT

Ta yi wannan harsashen ne a yayin gangamin kamfen din APC na Mata a shiyyar Kudu Maso Yamma da ya gudana a Mobolaji Johnson Arena a Legas.

“Dangane da tikitin musulmai biyu, wannan ya bude wani sabon fage a siyasar kasar nan, kuma nan gaba za a sake samun wani makamancinsa. Wani lokaci a nan gaba za mu samu tikitin Kirista da Kirista.”

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

Ta mika godiyarta ga uwar gidan shugaban kasa Muhammadu Buhari, Aisha Buhari wacce aka tura wa katin gayyata amma ba ta samu halartar ba.

“Muna mika muku godiya bisa fitowa da kuka yi kuka halarci wannan taron. Zuwa na nan kamar zuwa gida ziyara ne. A shekaru 23 da suka wuce, Allah ya albarkaci mijina ya zama gwamna, na ba shi goyon baya dari bisa dari a matsayina ta matar gwamna.”

Matar Tinubu din wacce ta misalta gangamin a matsayin ziyara zuwa gida “Ina kuma godiya ga al’ummar Legas ta tsakiya bisa turani Majalisar Dattawa domin na wakilcesu. Ni ne mace ta farko da ta zama Sanata har sau uku. Wannan babbar damace a gareni. Tun 2007 da mijina ya bar gwamna, na cigaba da aiki wa jama’anmu masu albarka.”

Matar gwamnan Jihar Legas, Dakta Ibijoke Sanwo-Olu, ta ce, Nijeriya na bukatar wani jajirtacce irin Tinubu wanda zai iya tafiyar da harkokin kasar nan a nan gaba.

Ta ce, Gwamnatin Tinubu za ta baiwa Mata damarmaki masu yawa.

Tinubu
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Tinubu
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
2023: Matsin Lamba Ba Za Ta Sa Na Janye Takarata Ba – A.A Zaura

2023: Matsin Lamba Ba Za Ta Sa Na Janye Takarata Ba - A.A Zaura

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.