ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kuncin Rayuwa: Jam’iyyun Adawa Da Kungiyar Kwadago Sun Caccaki Tinubu

by Yusuf Shuaibu
4 months ago

Jam’iyyar ADC ta caccaki gwamntin Shugaban kasa, Bola Tinubu kan kuncin rayuwa a Nijeriya tare da musanta cewa, jam’iyyar APC ta gudanar da sauye-sauyen tattalin arziki na Tinubu, da suka kawo saukin rayuwa.

Sai dai kuma APC ta mayar da martini kan wannan lamari, ta zargi jam’iyyar adawa ta ADC da yaudarar ‘yan Nijeriya ta hanyar zargin Shugaba Tinubu kan kashi 63 na talauci a kasar kamar yadda bincike ya nuna a makon da ya gabata.

  • Ana Neman Hankada Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Mummunan Rami In Ji Wakilin Kasar Sin
  • Rawar Da Sashen Ayyukan Hidimomi Da Biyan Bukatu Ke Kara Takawa A Kasar Sin 

Binciken masu ruwa da tsaki da aka shirya tattaunawa a Abuja, ya nuna cewa yawan talauci a kasa nan ya tashi sosai daga matsakaicin kaso kusan 49.8 cikin dari zuwa kusan 63 cikin dari bayan cire tallafin mai kafin ya dan ragu kadan bayan gabatar da matakai masu tsauri.

ADVERTISEMENT

Da yake magana kan lamarin, sakataren yada labarai na jam’iyyar ADC na kasa, Malam Bolaji Abdullahi, ya jaddada cewa bayanan sun nuna cewa matakin talauci a Nijeriya ya haura zuwa kashi 63 cikin dari, daga kusan kashi 50 cikin dari kafin a cire tallafin mai.

Abdullahi ya tabbatar da cewa rahoton da ya nuna cewa kashi 93 cikin dari na ‘yan Nijeriya suna ganin kasar na tafiya a mummunan hanya ba batutuwan jam’iyyar adawa ba ne kan lamarin.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Ya ce rahotannin sun nuna karara cewa manufofin gwamnatin APC kan tattalin arziki ba sa tafiya kan ceto rayukan ‘yan Nijeriya karkashin mulkin Tinubu.

Mai magana da yawun ADC ya ce maimakon mayar da hankali kan magance talauci da kuncin rayuwa da ya dabaibaye ‘yan Nijeriya a karkashin wannan gwamnati, jam’iyyar mai mulki ta ci gaba da farmakan jam’iyyun adawa tare da yin watsi da ceto rayukan miliyoyin ‘yan kasa.

Ya kara da cewa ba za a iya watsi da gaskiya ta hanyar bayanan jarida ba, yana jaddada cewa rahoton ‘yanci da ya haifar da muhawara yana nuna cewa yawan talauci a Nijeriya ya kai kashi 63 cikin dari, daga kusan kashi 50 kafin a cire tallafin man fetur.

“Wannan na nufin cewa wasu karin miliyoyin ‘yan Nijeriya za a kara tilasta musu shiga cikin talauci a wannana lokacin da aka gabatar da manufofin tattalin arziki da gwamnatin APC ta gaza aiwatarwa.”

ADC ta kara da cewa yayin da APC ke ikirarin cewa ‘yan Nijeriya suna goyon bayan sauye-sauyen da gwamnati Tinubu ta aiwatar a kasar nan, amma kuma bayanan sun nuna akasin haka.

Mai magana da yawun jam’iyyar adawa ya ce binciken masu zaman kansu sun nuna cewa kashi 93 cikin dari na ‘yan Nijeriya suna ganin cewa kasar na tafiya a mummunan shugabanci.

“Kashi tamanin da takwas cikin dari suna bayyana tattalin arzikin kasa a matsayin mara kyau, yayin da kashi 74 cikin dari ke suna rayuwa cikin kangin talauci. Wadannan ba maganganu ne na ‘yan adawa ba. Ra’ayoyin ‘yan Nijeriya ne da kansu ciki har da ‘yan APC.”

ADC ta ce yayin da APC ke dagewa kan cewa wahalar da ‘yan Nijeriya ke sha ta kasance ta wucin gadi ne, said ai kuma alkaluma suna ba da wani labari daban.

“Binciken baya-bayan nan ya nuna cewa kashi 82 cikin dari na ‘yan Nijeriya bas a samun isasshen abinci a kalla sau daya a cikin shekarar da ta gabata, kashi 82 cikin dari na fama da rashin kula da lafiya, kashi 79 cikin dari sun daina amfani da man girki, kashi 74 cikin dari na fama da rashin tsaftar ruwa, kuma kashi 95 cikin dari na fama da rashin samun kudade a wani lokaci cikin shekarar. Wadannan alkaluma ba su nuna rashin jin dadi na dan lokaci ba, amma suna nuna talauci da kuncin rayuwa mai tsanani,” in ji ADC.

A yayin da take mayar da martani kan ikirarin APC game da matakan tattalin arziki, ADC ta ce ‘yan Nijeriya na rayuwa kuncin tattalin arziki, inda farashin man fetur ya karu kusan kashi 500 cikin dari, daga kusan naira 255 a kowanne lita a watan Mayu 2023 lokacin da Tinubu ya hau mulki, zuwa kusan naira 1,500 a kowanne lita a yau a wurare da dama na wannan kasa.

“Wannan yana kara tsadar sufuri kuma yana kara farashi kayayyaki abinci fiye da abin da miliyoyin gidaje za su iya saya.”

ADC ya kara sukar da’awar APC kan kudin da ake kashewa kan tallafin mai, wanda ya kamata ya kai kusan naira tiriliyan 6.4 a asusun ajiya a bara kadai, sai yanzu ne ake karkatar da shi zuwa wasu sassa masu muhimmanci kamar kiwon lafiya da ci gaban al’umma.

Jam’iyyar adawa ta ce a rubuce yake cewa naira miliyan 36 kawai, kusan kashi 0.02 cikin dari na manyan ayyuka a cikin kasafin kudin, don ainihin ayyukan jari a shekarar 2025 ga dukkan sashen kula da lafiya na tarayya na Najeriya.

“Saboda haka, ‘yan Nijeriya suna bukatar amsar wadanan tambayoyi masu sauki. Idan an tanadi kudaden tallafin mai tare da rarraba su zuwa muhimman sassan, to a ina dukkan kudin ke tafiya? Me ya sa aka kasa biyan ‘yan kwangiloli na cikin gida? Me ya sa jami’o’i har yanzu ba su da kayan aiki masu kyau?”

Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Zargin Cin Hanci: Babu Wani Shirin Tsige El-Rufai – Kakakin Majalisar Dokokin Kaduna

Bayan Kwana 30, Har Yanzu ICPC Na Ci Gaba Rike El-Rufai

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.