ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kuncin Rayuwa: Jam’iyyun Adawa Da Kungiyar Kwadago Sun Caccaki Tinubu

by Yusuf Shuaibu
3 months ago

Jam’iyyar ADC ta caccaki gwamntin Shugaban kasa, Bola Tinubu kan kuncin rayuwa a Nijeriya tare da musanta cewa, jam’iyyar APC ta gudanar da sauye-sauyen tattalin arziki na Tinubu, da suka kawo saukin rayuwa.

Sai dai kuma APC ta mayar da martini kan wannan lamari, ta zargi jam’iyyar adawa ta ADC da yaudarar ‘yan Nijeriya ta hanyar zargin Shugaba Tinubu kan kashi 63 na talauci a kasar kamar yadda bincike ya nuna a makon da ya gabata.

  • Ana Neman Hankada Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Mummunan Rami In Ji Wakilin Kasar Sin
  • Rawar Da Sashen Ayyukan Hidimomi Da Biyan Bukatu Ke Kara Takawa A Kasar Sin 

Binciken masu ruwa da tsaki da aka shirya tattaunawa a Abuja, ya nuna cewa yawan talauci a kasa nan ya tashi sosai daga matsakaicin kaso kusan 49.8 cikin dari zuwa kusan 63 cikin dari bayan cire tallafin mai kafin ya dan ragu kadan bayan gabatar da matakai masu tsauri.

ADVERTISEMENT

Da yake magana kan lamarin, sakataren yada labarai na jam’iyyar ADC na kasa, Malam Bolaji Abdullahi, ya jaddada cewa bayanan sun nuna cewa matakin talauci a Nijeriya ya haura zuwa kashi 63 cikin dari, daga kusan kashi 50 cikin dari kafin a cire tallafin mai.

Abdullahi ya tabbatar da cewa rahoton da ya nuna cewa kashi 93 cikin dari na ‘yan Nijeriya suna ganin kasar na tafiya a mummunan hanya ba batutuwan jam’iyyar adawa ba ne kan lamarin.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Ya ce rahotannin sun nuna karara cewa manufofin gwamnatin APC kan tattalin arziki ba sa tafiya kan ceto rayukan ‘yan Nijeriya karkashin mulkin Tinubu.

Mai magana da yawun ADC ya ce maimakon mayar da hankali kan magance talauci da kuncin rayuwa da ya dabaibaye ‘yan Nijeriya a karkashin wannan gwamnati, jam’iyyar mai mulki ta ci gaba da farmakan jam’iyyun adawa tare da yin watsi da ceto rayukan miliyoyin ‘yan kasa.

Ya kara da cewa ba za a iya watsi da gaskiya ta hanyar bayanan jarida ba, yana jaddada cewa rahoton ‘yanci da ya haifar da muhawara yana nuna cewa yawan talauci a Nijeriya ya kai kashi 63 cikin dari, daga kusan kashi 50 kafin a cire tallafin man fetur.

“Wannan na nufin cewa wasu karin miliyoyin ‘yan Nijeriya za a kara tilasta musu shiga cikin talauci a wannana lokacin da aka gabatar da manufofin tattalin arziki da gwamnatin APC ta gaza aiwatarwa.”

ADC ta kara da cewa yayin da APC ke ikirarin cewa ‘yan Nijeriya suna goyon bayan sauye-sauyen da gwamnati Tinubu ta aiwatar a kasar nan, amma kuma bayanan sun nuna akasin haka.

Mai magana da yawun jam’iyyar adawa ya ce binciken masu zaman kansu sun nuna cewa kashi 93 cikin dari na ‘yan Nijeriya suna ganin cewa kasar na tafiya a mummunan shugabanci.

“Kashi tamanin da takwas cikin dari suna bayyana tattalin arzikin kasa a matsayin mara kyau, yayin da kashi 74 cikin dari ke suna rayuwa cikin kangin talauci. Wadannan ba maganganu ne na ‘yan adawa ba. Ra’ayoyin ‘yan Nijeriya ne da kansu ciki har da ‘yan APC.”

ADC ta ce yayin da APC ke dagewa kan cewa wahalar da ‘yan Nijeriya ke sha ta kasance ta wucin gadi ne, said ai kuma alkaluma suna ba da wani labari daban.

“Binciken baya-bayan nan ya nuna cewa kashi 82 cikin dari na ‘yan Nijeriya bas a samun isasshen abinci a kalla sau daya a cikin shekarar da ta gabata, kashi 82 cikin dari na fama da rashin kula da lafiya, kashi 79 cikin dari sun daina amfani da man girki, kashi 74 cikin dari na fama da rashin tsaftar ruwa, kuma kashi 95 cikin dari na fama da rashin samun kudade a wani lokaci cikin shekarar. Wadannan alkaluma ba su nuna rashin jin dadi na dan lokaci ba, amma suna nuna talauci da kuncin rayuwa mai tsanani,” in ji ADC.

A yayin da take mayar da martani kan ikirarin APC game da matakan tattalin arziki, ADC ta ce ‘yan Nijeriya na rayuwa kuncin tattalin arziki, inda farashin man fetur ya karu kusan kashi 500 cikin dari, daga kusan naira 255 a kowanne lita a watan Mayu 2023 lokacin da Tinubu ya hau mulki, zuwa kusan naira 1,500 a kowanne lita a yau a wurare da dama na wannan kasa.

“Wannan yana kara tsadar sufuri kuma yana kara farashi kayayyaki abinci fiye da abin da miliyoyin gidaje za su iya saya.”

ADC ya kara sukar da’awar APC kan kudin da ake kashewa kan tallafin mai, wanda ya kamata ya kai kusan naira tiriliyan 6.4 a asusun ajiya a bara kadai, sai yanzu ne ake karkatar da shi zuwa wasu sassa masu muhimmanci kamar kiwon lafiya da ci gaban al’umma.

Jam’iyyar adawa ta ce a rubuce yake cewa naira miliyan 36 kawai, kusan kashi 0.02 cikin dari na manyan ayyuka a cikin kasafin kudin, don ainihin ayyukan jari a shekarar 2025 ga dukkan sashen kula da lafiya na tarayya na Najeriya.

“Saboda haka, ‘yan Nijeriya suna bukatar amsar wadanan tambayoyi masu sauki. Idan an tanadi kudaden tallafin mai tare da rarraba su zuwa muhimman sassan, to a ina dukkan kudin ke tafiya? Me ya sa aka kasa biyan ‘yan kwangiloli na cikin gida? Me ya sa jami’o’i har yanzu ba su da kayan aiki masu kyau?”

Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Zargin Cin Hanci: Babu Wani Shirin Tsige El-Rufai – Kakakin Majalisar Dokokin Kaduna

Bayan Kwana 30, Har Yanzu ICPC Na Ci Gaba Rike El-Rufai

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.