ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kuncin Rayuwa: Jam’iyyun Adawa Da Kungiyar Kwadago Sun Caccaki Tinubu

by Yusuf Shuaibu
3 months ago

Jam’iyyar ADC ta caccaki gwamntin Shugaban kasa, Bola Tinubu kan kuncin rayuwa a Nijeriya tare da musanta cewa, jam’iyyar APC ta gudanar da sauye-sauyen tattalin arziki na Tinubu, da suka kawo saukin rayuwa.

Sai dai kuma APC ta mayar da martini kan wannan lamari, ta zargi jam’iyyar adawa ta ADC da yaudarar ‘yan Nijeriya ta hanyar zargin Shugaba Tinubu kan kashi 63 na talauci a kasar kamar yadda bincike ya nuna a makon da ya gabata.

  • Ana Neman Hankada Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Mummunan Rami In Ji Wakilin Kasar Sin
  • Rawar Da Sashen Ayyukan Hidimomi Da Biyan Bukatu Ke Kara Takawa A Kasar Sin 

Binciken masu ruwa da tsaki da aka shirya tattaunawa a Abuja, ya nuna cewa yawan talauci a kasa nan ya tashi sosai daga matsakaicin kaso kusan 49.8 cikin dari zuwa kusan 63 cikin dari bayan cire tallafin mai kafin ya dan ragu kadan bayan gabatar da matakai masu tsauri.

ADVERTISEMENT

Da yake magana kan lamarin, sakataren yada labarai na jam’iyyar ADC na kasa, Malam Bolaji Abdullahi, ya jaddada cewa bayanan sun nuna cewa matakin talauci a Nijeriya ya haura zuwa kashi 63 cikin dari, daga kusan kashi 50 cikin dari kafin a cire tallafin mai.

Abdullahi ya tabbatar da cewa rahoton da ya nuna cewa kashi 93 cikin dari na ‘yan Nijeriya suna ganin kasar na tafiya a mummunan hanya ba batutuwan jam’iyyar adawa ba ne kan lamarin.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Ya ce rahotannin sun nuna karara cewa manufofin gwamnatin APC kan tattalin arziki ba sa tafiya kan ceto rayukan ‘yan Nijeriya karkashin mulkin Tinubu.

Mai magana da yawun ADC ya ce maimakon mayar da hankali kan magance talauci da kuncin rayuwa da ya dabaibaye ‘yan Nijeriya a karkashin wannan gwamnati, jam’iyyar mai mulki ta ci gaba da farmakan jam’iyyun adawa tare da yin watsi da ceto rayukan miliyoyin ‘yan kasa.

Ya kara da cewa ba za a iya watsi da gaskiya ta hanyar bayanan jarida ba, yana jaddada cewa rahoton ‘yanci da ya haifar da muhawara yana nuna cewa yawan talauci a Nijeriya ya kai kashi 63 cikin dari, daga kusan kashi 50 kafin a cire tallafin man fetur.

“Wannan na nufin cewa wasu karin miliyoyin ‘yan Nijeriya za a kara tilasta musu shiga cikin talauci a wannana lokacin da aka gabatar da manufofin tattalin arziki da gwamnatin APC ta gaza aiwatarwa.”

ADC ta kara da cewa yayin da APC ke ikirarin cewa ‘yan Nijeriya suna goyon bayan sauye-sauyen da gwamnati Tinubu ta aiwatar a kasar nan, amma kuma bayanan sun nuna akasin haka.

Mai magana da yawun jam’iyyar adawa ya ce binciken masu zaman kansu sun nuna cewa kashi 93 cikin dari na ‘yan Nijeriya suna ganin cewa kasar na tafiya a mummunan shugabanci.

“Kashi tamanin da takwas cikin dari suna bayyana tattalin arzikin kasa a matsayin mara kyau, yayin da kashi 74 cikin dari ke suna rayuwa cikin kangin talauci. Wadannan ba maganganu ne na ‘yan adawa ba. Ra’ayoyin ‘yan Nijeriya ne da kansu ciki har da ‘yan APC.”

ADC ta ce yayin da APC ke dagewa kan cewa wahalar da ‘yan Nijeriya ke sha ta kasance ta wucin gadi ne, said ai kuma alkaluma suna ba da wani labari daban.

“Binciken baya-bayan nan ya nuna cewa kashi 82 cikin dari na ‘yan Nijeriya bas a samun isasshen abinci a kalla sau daya a cikin shekarar da ta gabata, kashi 82 cikin dari na fama da rashin kula da lafiya, kashi 79 cikin dari sun daina amfani da man girki, kashi 74 cikin dari na fama da rashin tsaftar ruwa, kuma kashi 95 cikin dari na fama da rashin samun kudade a wani lokaci cikin shekarar. Wadannan alkaluma ba su nuna rashin jin dadi na dan lokaci ba, amma suna nuna talauci da kuncin rayuwa mai tsanani,” in ji ADC.

A yayin da take mayar da martani kan ikirarin APC game da matakan tattalin arziki, ADC ta ce ‘yan Nijeriya na rayuwa kuncin tattalin arziki, inda farashin man fetur ya karu kusan kashi 500 cikin dari, daga kusan naira 255 a kowanne lita a watan Mayu 2023 lokacin da Tinubu ya hau mulki, zuwa kusan naira 1,500 a kowanne lita a yau a wurare da dama na wannan kasa.

“Wannan yana kara tsadar sufuri kuma yana kara farashi kayayyaki abinci fiye da abin da miliyoyin gidaje za su iya saya.”

ADC ya kara sukar da’awar APC kan kudin da ake kashewa kan tallafin mai, wanda ya kamata ya kai kusan naira tiriliyan 6.4 a asusun ajiya a bara kadai, sai yanzu ne ake karkatar da shi zuwa wasu sassa masu muhimmanci kamar kiwon lafiya da ci gaban al’umma.

Jam’iyyar adawa ta ce a rubuce yake cewa naira miliyan 36 kawai, kusan kashi 0.02 cikin dari na manyan ayyuka a cikin kasafin kudin, don ainihin ayyukan jari a shekarar 2025 ga dukkan sashen kula da lafiya na tarayya na Najeriya.

“Saboda haka, ‘yan Nijeriya suna bukatar amsar wadanan tambayoyi masu sauki. Idan an tanadi kudaden tallafin mai tare da rarraba su zuwa muhimman sassan, to a ina dukkan kudin ke tafiya? Me ya sa aka kasa biyan ‘yan kwangiloli na cikin gida? Me ya sa jami’o’i har yanzu ba su da kayan aiki masu kyau?”

Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Zargin Cin Hanci: Babu Wani Shirin Tsige El-Rufai – Kakakin Majalisar Dokokin Kaduna

Bayan Kwana 30, Har Yanzu ICPC Na Ci Gaba Rike El-Rufai

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.