A ranar Litinin Mambobin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta ASUU, sun yi barazanar daukar mataki mai tsauri da gwamnatin tarayya kan abin da suka bayyana a matsayin aiwatar da yarjejeniyar watan Disamban 2025 cikin kuskure da son kai.
Kungiyar ta kuma lissafo batutuwan albashin watanni uku da rabi da aka rike, bashin karin girma a aiki, gibin albashi da ya samo asali daga amfani da tsarin IPPIS, kudaden cirewa na bangare na uku da ba a biya ba, da bashin karin albashi na kaso 25 zuwa 35 cikin dari a matsayin wasu daga cikin matsalolin da ke haddasa korafi.
Hakan na kunshe ne a cikin sakamakon taron Kwamitin Zartarwa na Kasa (NEC) na kungiyar wanda aka gudanar a Jami’ar Modibbo Adama da ke Yola.
Da yake karanta sanarwar taron ga manema labarai a Abuja ranar Litinin, Farfesa Christopher Piwuna ya ce: “Kara takaicin da ke karuwa sakamakon abin da ya yi kama da rashin nuna damuwar gwamnati kan walwalar malaman jami’o’in Nijeriya na haifar da fushin da ka iya rikidewa zuwa wani sabon rikicin yajin aiki idan ba a magance matsalolin ba.”
Ya kara da cewa: “Kungiyar na kira ga duk masu kishin kasa na gaskiya, ‘yan Nijeriya masu kyakkyawar manufa da masu son ci gaban kasar nan da su matsa wa gwamnatocin jihohi da ta tarayya lamba domin cikakken aiwatar da sabuwar yarjejeniya tare da warware sauran matsalolin da suka rage domin amfanin iyaye, dalibai da kasa baki daya.
“Kofofin kungiyarmu a bude suke domin ci gaba da aiki tare da gwamnati wajen cimma dukkan bukatunmu. A lokaci guda, NEC ta bayar da umarnin kiran wani taron gaggawa na NEC cikin makwanni masu zuwa domin sake duba halin da ake ciki tare da daukar matakin da ya dace idan ya zama dole,” in ji shi.















Discussion about this post