Jam’iyyun siyasa a Nijeriya sun shiga rudani a yayin da wa’adin mika jerin sunayen mambobin jam’iyyun ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ya kare.
Wa’adin ranar karshe ga jam’iyyun siyasa don mika rajistar mambobinsu ga hukumar zabe ta kare da tsakar daren ranar 10 ga watan Mayu.
Jam’iyyar APC da jam’iyyar ADC da jam’iyyar NDC na iya fafatawa da ‘yan takarar shugaban kasa iri daya da na zaben 2023, amma a jam’iyyu daban-daban.
A zaben shugaban kasa na 2023, ya kasance fafatawa ne tsakanin mutane uku, inda shugaba Bola Tinubu ya kasance dan takarar APC, tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar a matsayin dan takarar jam’iyyar PDP da kuma tsohon gwamnan Jihar Anambra, Mista Peter Obi a matsayin dan takarar jam’iyyar LP.
Bayan shekaru hudu, PDP da LP na daga cikin manyan jam’iyyun adawa guda uku a 2023, duka sun shiga cikin rikice-rikicen wanda ya janyo har sai da manyan mutane a cikinsu sun tilasta musu barin jam’iyyun. Atiku ya koma ADC yayin da Obi ya koma NDC.
Obi ya bayyana a bainar jama’a cewa dole ne ya kasance a kan takardar zabe a shekarar 2027, kuma ya kara nuna aniyyarsa ta yin wa’adi guda idan an zabe shi a matsayin shugaban Nijeriya, tare da yanke shawarar NDC na kai mukamin shugaban kasa a yankin kudu, fitowarsa a matsayin dan takarar shugaban kasa na NDC ya kusan tabbata. A karkashin wannan tsarin, NDC ta ce za a juya tikitin zuwa arewa a shekarar 2031, kuma tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Kwankwaso, wanda ake tsammanin zai zama mataimakin Obi, ya amince da hakan.
‘Yan takara guda uku sun nuna sha’awar takara a zaben shugaban kasa a karkashin jam’iyyar ADC kuma su ne Atiku, tsohon ministan sufuri, Chibuike Amaechi da Mohamed Hayatu-Deen kuma jam’iyyar ba ta fayyace ko za ta bi tsarin karba-karba wajen raba tikitinta ba.
Ga PDP, yiwuwar tsohuwar jam’iyyar gwamnati wadda rikici mai tsawo na shugabanci ya raba ta gida biyu wajen fitar da dan takarar shugaban kasa, ya bayyana a matsayin abin shakka yayin da wa’adin da jam’iyyun ke da shi don mika jerin mambobinsu ga hukumar zabe ya wuce a ranar 10 ga Mayu.
PDP ta rabu kashi biyu. Daya na karkashin kulawar ministan Babban Birnin Tarayya Abuja kuma tsohon Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, yayin da daya bangaren ke karkashin kulawar Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde. Dukkanin bangarorin biyu suna cikin dogon rikici kan wanda ke wakiltar sahihin shugabancin kasa na jam’iyyar.
A cikin hukuncin kotun koli na baya-bayan nan, hukuncin ya nuna cewa kotu ta tabbatar da dakatar da abokin Wike, Sam Anyanwu a matsayin sakataren jam’iyyar na kasa, amma har yanzu shafin yanar gizo na hukumar INEC na nuna cewa, Abdul Rahman Mohamed a matsayin shugaban jam’iyyar da Anyanwu a matsayin sakataren jam’iyyar PDP. Dukkanin wadannan mutane suna cikin bangaren Wike, kuma ci gaba da kasancewarsu a shafin INEC na nuni da cewa hukumar zabe ba ta aiwatar da wani umarnin kotu da zai iya canza shugabancin da aka amince da shi a jam’iyyar ba.
Matakin INEC na ci gaba da sanya abokan Wike a matsayin shugaban jam’iyyar da sakatare, yana da bambanci da gaggawar cire sunan tsohon shugaban majalisar dattawa, Dabid Mark da tsohon ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola a matsayin shugaban da sakataren jam’iyyar ADC.
Lokacin da kotun koli ta yanke hukunci cewa shugabancin ADC ya kamata ya koma yadda yake a baya, INEC ta dauki mataki cikin sauri ta fassara hukuncin a matsayin cewa an dawo da Mark da Aregbesola. Duka shugabannin an dawo da sunayansu daga shafin yanar gizon INEC.
Wata majiya daga PDP ya shaida cewa INEC ba ta yi wani canji a shugabancin jam’iyyar duk da hukuncin kotun koli, wanda ana fassara shi a matsayin cewa hukumar na jiran karin bayani.















Discussion about this post