ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

by Yusuf Shuaibu
3 weeks ago
Adawa

Jam’iyyun siyasa a Nijeriya sun shiga rudani a yayin da wa’adin mika jerin sunayen mambobin jam’iyyun ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ya kare.

Wa’adin ranar karshe ga jam’iyyun siyasa don mika rajistar mambobinsu ga hukumar zabe ta kare da tsakar daren ranar 10 ga watan Mayu.

Jam’iyyar APC da jam’iyyar ADC da jam’iyyar NDC na iya fafatawa da ‘yan takarar shugaban kasa iri daya da na zaben 2023, amma a jam’iyyu daban-daban.

ADVERTISEMENT

A zaben shugaban kasa na 2023, ya kasance fafatawa ne tsakanin mutane uku, inda shugaba Bola Tinubu ya kasance dan takarar APC, tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar a matsayin dan takarar jam’iyyar PDP da kuma tsohon gwamnan Jihar Anambra, Mista Peter Obi a matsayin dan takarar jam’iyyar LP.

Bayan shekaru hudu, PDP da LP na daga cikin manyan jam’iyyun adawa guda uku a 2023, duka sun shiga cikin rikice-rikicen wanda ya janyo har sai da manyan mutane a cikinsu sun tilasta musu barin jam’iyyun. Atiku ya koma ADC yayin da Obi ya koma NDC.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

Obi ya bayyana a bainar jama’a cewa dole ne ya kasance a kan takardar zabe a shekarar 2027, kuma ya kara nuna aniyyarsa ta yin wa’adi guda idan an zabe shi a matsayin shugaban Nijeriya, tare da yanke shawarar NDC na kai mukamin shugaban kasa a yankin kudu, fitowarsa a matsayin dan takarar shugaban kasa na NDC ya kusan tabbata. A karkashin wannan tsarin, NDC ta ce za a juya tikitin zuwa arewa a shekarar 2031, kuma tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Kwankwaso, wanda ake tsammanin zai zama mataimakin Obi, ya amince da hakan.

‘Yan takara guda uku sun nuna sha’awar takara a zaben shugaban kasa a karkashin jam’iyyar ADC kuma su ne Atiku, tsohon ministan sufuri, Chibuike Amaechi da Mohamed Hayatu-Deen kuma jam’iyyar ba ta fayyace ko za ta bi tsarin karba-karba wajen raba tikitinta ba.

Ga PDP, yiwuwar tsohuwar jam’iyyar gwamnati wadda rikici mai tsawo na shugabanci ya raba ta gida biyu wajen fitar da dan takarar shugaban kasa, ya bayyana a matsayin abin shakka yayin da wa’adin da jam’iyyun ke da shi don mika jerin mambobinsu ga hukumar zabe ya wuce a ranar 10 ga Mayu.

PDP ta rabu kashi biyu. Daya na karkashin kulawar ministan Babban Birnin Tarayya Abuja kuma tsohon Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, yayin da daya bangaren ke karkashin kulawar Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde. Dukkanin bangarorin biyu suna cikin dogon rikici kan wanda ke wakiltar sahihin shugabancin kasa na jam’iyyar.

A cikin hukuncin kotun koli na baya-bayan nan, hukuncin ya nuna cewa kotu ta tabbatar da dakatar da abokin Wike, Sam Anyanwu a matsayin sakataren jam’iyyar na kasa, amma har yanzu shafin yanar gizo na hukumar INEC na nuna cewa, Abdul Rahman Mohamed a matsayin shugaban jam’iyyar da Anyanwu a matsayin sakataren jam’iyyar PDP. Dukkanin wadannan mutane suna cikin bangaren Wike, kuma ci gaba da kasancewarsu a shafin INEC na nuni da cewa hukumar zabe ba ta aiwatar da wani umarnin kotu da zai iya canza shugabancin da aka amince da shi a jam’iyyar ba.

Matakin INEC na ci gaba da sanya abokan Wike a matsayin shugaban jam’iyyar da sakatare, yana da bambanci da gaggawar cire sunan tsohon shugaban majalisar dattawa, Dabid Mark da tsohon ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola a matsayin shugaban da sakataren jam’iyyar ADC.

Lokacin da kotun koli ta yanke hukunci cewa shugabancin ADC ya kamata ya koma yadda yake a baya, INEC ta dauki mataki cikin sauri ta fassara hukuncin a matsayin cewa an dawo da Mark da Aregbesola. Duka shugabannin an dawo da sunayansu daga shafin yanar gizon INEC.

Wata majiya daga PDP ya shaida cewa INEC ba ta yi wani canji a shugabancin jam’iyyar duk da hukuncin kotun koli, wanda ana fassara shi a matsayin cewa hukumar na jiran karin bayani.

Siyasa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Siyasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Yanzu-yanzu: ‘Yan Majalisar Wakilai 17 Sun Fice Daga ADC Zuwa NDC
Tambarin Dimokuradiyya

Kwararan Sauye-sauyen Da Obi Da Kwankwaso Suka Jawo A Siyasar Nijeriya Gabanin Cikar Wa’adin INEC

May 9, 2026
Next Post
Masanin Angola: Manufar Soke Harajin Kwastam Za Ta Bude Sabon Babi Na Raya Dangantakar Sin Da Afirka

An Samu Karuwar Hada-hadar Jiragen Ruwa A Zangon Farko Na 2026 —Shugaban NPA

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.