Bikin Al’adu na ɗaliban Jami’ar Ahmadu Bello (ABU), Zariya, na shekarar 2026 ya ƙara ɗaukar armashi, yayin da ɗalibai daga jihohi daban-daban suka fafata a gasar girki.Wakilan jihohi daban-daban sun taru domin nuna ƙwarewarsu wajen shirya abincin gargajiya da ke bayyana tarihi, al’adu da kuma asalin al’ummominsu.
Gasar ya tantance mahalarta ne bisa ɗanɗano da ƙamshin abincinsu, ƙwarewar girki, yadda aka gabatar da abincin, da kuma al’adun da kowanne abinci ke wakilta.Irin waɗannan gasa na taimakawa wajen ƙarfafa zumunci, haɗin kai da fahimtar juna tsakanin ɗalibai daga sassa daban-daban na ƙasar nan.Taron ya samu halartar ɗalibai da baƙi daga kabilu daban-daban, inda aka samu damar nuna da kuma yaba wa ɗimbin al’adun gargajiya da Najeriya ke da su.
An gudanar da gasar ne a babban filin taro na Mamman Kontagora da ke cikin harabar jami’ar. A ƙarshen gasar, alkalan gasar sun bayyana Jihar Nasarawa a matsayin wadda ta yi nasara.Jihar da ta yi nasara ta samu yabo da taya murna daga ɗalibai da sauran mahalarta taron.
Gasar girkin ya kasance wani ɓangare na shirye-shiryen Makon Al’adu (Cultural Week) na bana, wanda ƙungiyar ɗaliban Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya, ta shirya. Ana sa ran shirin zai gudana na tsawon kwanaki uku.














