ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kafafen Sadarwa Na Zamani Wuri Ne Na Bunƙasa Tattalin Arziƙi — Ubale Kiru

by Idris Umar
4 weeks ago
Sadarwa

A ranar Asabar ta makon jiya ne ƙungiyar Sayarwa Market Place ta shiya wa matasa masu gudanar da harkokin kasuwaninsu ta kafafen sadarwa na zamani (Shoshiyal Mediya) taron ƙara wa juna ilimi. Editanmu Bello Hamza ya tattauna da Dakta Muhammad Ubale Kiru (Manajan Sadarwa na Kamfanin SINNTS) wanda yana ɗaya daga cikin masanan da suka gabatar da bayanai a yayin taron, inda ya yi ƙarin haske a kan wata sabwar manhaja da za ta taimaka wajen bunƙasa tattalin arziƙin al’ummar mu. Ga dai yadda hirar ta kasance.

Wani bayani zaka yi mana a kan manhajar SINNTS?

Manhajar ta samu asali ne sakamakon giɓin da aka samu kuma muke kallo a sauran kafofin soshial mediya msamman yadda suka karkata ga sauran al’ummar wasu ɓangare na duniya sai muka ga ya dace mu ƙirƙiro wani abun da ta dace da yanayi da al’adunmu a matsayinmu na ƴan Afirka, wanda zai tafi a kan irin tsarin rayuwarmu ya kuma tafi a kan yadda muke so muga ya yi maganin abin da suka fi damun mu a matsayin mu na baƙaƙen fata kamar talauci, kuma sauran mahajojin da ake dasu ba a waklitarmu ƴan Afrika. A kan haka muka ƙirƙiro da SINNT domin ta aƙalla ta yi mana maganin wasu daga cikin waɗannan matsalolin.

ADVERTISEMENT

A kan haka ita SINNTS ta samar da cewa, mutum miliyan 1 na farko da suka fara hawa (suka yi rajista) za su zama masu hannu jari a kamfanin kai tsaye, duka abin da kamfani yake samu da su za a raba a ƙarshen shekara, ba irin yadda muka saba gani na a yanzu kamfanonin su kaɗai ke amfana da duk abin da akasa mu daga abin da aka samu a mahajonjin da ake ake amfani da su. Haka kuma ta hanyar amfani da manhajar mutum zai kai ga samun ribar miliyan ɗaya ba tare da ya ankara ba. Wanda hakan zai canza rayuwar matasan mu.

Ta yaya matasa za su mayar da kafafen sadarwa na Soshiyal Mediya wurin samun arziƙi ba nishaɗi kaɗai ba?

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

A wannan yankin ne kawai matasa suka mayar da kafafen sadarwa wuri ne kawai na kallo da nishaɗi amma a wasu sassan yana zama wuri ne na bunƙasa tattalin arziƙi. Misali a shekarar da ta gabata an ƙiyarsata cews, kamfanin Facebook ya samu ribar aƙalla Dala biliyan Dubu. An kuma ƙiyarsa cewa, matashi na iya samun aƙalla daga Dala 50 zuwa sama a kowacce wata ta hanyar amfani da Facebook, amma matasan mu na Afrika basa amfana da wannan tsarin, a kan haka muka fito da tsarin SINNTS domin matasa masu fasaha za su amfana ta hanyar samun kuɗaɗe a kan dukkan abin da suka ɗora a manhajar.

Mene ne sharhinka a kan matasa masu amfani da kafafen sadarwa wajen cin zarafin mutane?

Lallai yadda wasu matasan ke amfani da kafafen sadarwa wajen yaɗa kalaman ɓatanci a cikin al’umma abin takaici ne. Za mu tabbatar da mun tsaftace wannan mahajar ta mu daga masu irin wannan halin. Ya kumata su gane cewa, wannan ba abin kirki ba ne domin addini ma ya haramta cin zarafin mutum ta kowacce hanya. Haka kuma doka ta haramta hakan, akwai kuma tanade tanade na dokokin Nijeriya da zai iya kaiwa ga an ɗaure duk wanda aka kama da irin wannan halin.

Ta yaya mutum zai samu hawa tare da amfani da wannan mahajar ta SINNTS?

Abu ne mai sauƙi, tana nan a google playstore da sauran wuraren sauke manhajoji, daga nan ne zaka bi matakan da za su biyo baya domin zama cikakken mai amfani manhajar SINNTS.

Mun gode ƙwarai da gaske

Nima na gode sosai

Sadarwa
Idris Umar
+ postsBio
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    Sanata Shehu Sani Ya Nemi Gwamnonin Arewa Su Tallafa Wa Bikin Al’adu Na ABU Zariya
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    Yadda Dakta A’isha Mustapha Ta Zama Shugabar Ƙungiyar Likitocin Jihar Kaduna
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    Kungiyar Daliban Jami’ar ABU Ta Gudanar Gasar Girke-girken Abincin Gargajiya A Bude Bikin Al’adu Na Bana
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Sadarwa

NSCDC Ta Tura Jami'ai 10,210 Da Za Su Sanya Ido A Zaɓen Gwamnan Jihar Osun

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.