ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyoyin Sa-ido Na Kasa-da-kasa Sun Yaba Da Zaben Ghana

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Ghana

Ƙungiyoyin sun yaba wa Ghana da ‘yan kasar bisa gudanar da zaben Shugaban kasa da na Majalisun dokoki cikin lumana.

Kungiyoyin da suka fito daga Tarayyar Afirka (AU), Kungiyar Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afrika (ECOWAS), da kungiyar Commonwealth a wani taron manema labarai na hadin gwiwa, sun yaba wa hukumar zabe (EC), jami’an zabe, jam’iyyun siyasa, ‘yansanda, da kafofin yada labarai kan rawar da suka taka wajen tabbatar da nasarar gudanar da zaben a Ghana.

  • ‘Yan Nijeriya Za Su Kayar Da APC A 2027 Kamar Yadda Aka Yi Wa NPP A Ghana – PDP
  • Motoci Kirar Kamfanin Kasar Sin Na Samun Karin Karbuwa A Kasar Ghana

Da take jawabi a taron manema labaran a Accra babban birnin Ghana, Sahle-Work Zewde, tsohuwar Shugabar kasar Habasha kuma Shugabar tawagar sa ido kan zabe a Tarayyar Afirka (AUEOM) ta ce, an gudanar da zaben cikin lumana da kara tabbatar da dimokuradiyyar kasar. Ta ce, ‘Tawagar masu sa ido a zabukan kasashen tarayyar Afirka (AUEOM) ta yaba wa al’ummar Ghana bisa jajircewar da suka yi na tabbatar da tsarin dimokuradiyya, wanda hakan ke nuni da yadda aka gudanar da babban zaben kasar a ranar 7 ga watan Disamban 2024 cikin lumana. Gaba daya tsarin zaben ya bi ka’idodin yankin kasa da kasa, da kara karfafa kimar dimokradiyyar Ghana.

ADVERTISEMENT

Alhaji Mohammed Namadi Sambo, tsohon mataimakin Shugaban Nijeriya kuma jagoran tawagar sa ido a kungiyar ECOWAS, ya ce masu kada kuri’a sun yi zabe cikin yanayi mai kyau, ba tare da tsangwama ko takurawa ba. Ta kuma taya al’ummar kasar Ghana murna. ‘Tawagar masu sa ido kan zabe ta Ecowas na taya al’ummar Ghana murna, tare da yi musu fatan ci gaba da samun zaman lafiya, daukaka, da ci gaba.”

Kungiyar sa ido ta ECOWAS ta jinjinawa Shugaban Ghana mai barin gado, Nana Akufo-Addo bisa yadda ya jagoranci kasar na shekaru 8, daya daga cikin mambar kungiyar.

LABARAI MASU NASABA

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola

Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

Kungiyar sa ido ta Commonwealth a karkashin jagorancin tsohon Shugaban kasar Botswana, Dokta Mokgweetsi Masisi ta ce, sun lura an bai wa nakasassu da tsoffi fifiko kuma an ba wa masu fama da matsalar gani da ido hakkinsu a wasu rumfunan zabe. Sai dai kuma sun lura da kalubale a wasu rumfunan zabe don wurin kada kuri’a ya yi wa masu amfani da keken guragu nisa.

Ya kara da cewa, ‘Rahoton su na karshe mai dauke da muhimman shawarwari za su mika shi ga babban sakatare kuma a raba shi zuwa ga gwamnatin Jamhuriyyar Ghana da sauran masu ruwa da tsaki da sauran jama’a.

A gefen taron, tsohon mataimakin Shugaban Nijeriya, kuma jagoran tawagar kungiyar ECOWAS ya yaba wa hukumomi da al’ummar Ghana bisa yadda aka gudanar da zaben kan tsari, a hira ta musamman da Muryar Amurka.

Tsohon shugaban kasa, John Dramani Mahama, na babbar jam’iyar adawa ta NDC, wanda ya lashe zaben Ghanan da kashi 56.55 cikin 100 na kuri’un da aka kada, ya yi jawabin amincewa da nasararsa bayan da hukumar zabe ta ayyana shi, a matsayin wanda ya lashe zaben kasar a hukumance.

Ghana
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
Kasashen Ketare

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola

May 30, 2026
Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
Kasashen Ketare

Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

May 30, 2026
Iran Ta Zargi Amurka Da Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Da Ke Tsakaninsu
Kasashen Ketare

Iran Ta Zargi Amurka Da Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Da Ke Tsakaninsu

May 30, 2026
Next Post
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Muhimmiyar Makalar Xi Mai Taken “Zurfafa Aiwatar Da Juyin Juya Halin Jam’iyyar Kwaminis Ta Sin”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Muhimmiyar Makalar Xi Mai Taken “Zurfafa Aiwatar Da Juyin Juya Halin Jam'iyyar Kwaminis Ta Sin”

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.