ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyoyin Sa-ido Na Kasa-da-kasa Sun Yaba Da Zaben Ghana

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Ghana

Ƙungiyoyin sun yaba wa Ghana da ‘yan kasar bisa gudanar da zaben Shugaban kasa da na Majalisun dokoki cikin lumana.

Kungiyoyin da suka fito daga Tarayyar Afirka (AU), Kungiyar Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afrika (ECOWAS), da kungiyar Commonwealth a wani taron manema labarai na hadin gwiwa, sun yaba wa hukumar zabe (EC), jami’an zabe, jam’iyyun siyasa, ‘yansanda, da kafofin yada labarai kan rawar da suka taka wajen tabbatar da nasarar gudanar da zaben a Ghana.

  • ‘Yan Nijeriya Za Su Kayar Da APC A 2027 Kamar Yadda Aka Yi Wa NPP A Ghana – PDP
  • Motoci Kirar Kamfanin Kasar Sin Na Samun Karin Karbuwa A Kasar Ghana

Da take jawabi a taron manema labaran a Accra babban birnin Ghana, Sahle-Work Zewde, tsohuwar Shugabar kasar Habasha kuma Shugabar tawagar sa ido kan zabe a Tarayyar Afirka (AUEOM) ta ce, an gudanar da zaben cikin lumana da kara tabbatar da dimokuradiyyar kasar. Ta ce, ‘Tawagar masu sa ido a zabukan kasashen tarayyar Afirka (AUEOM) ta yaba wa al’ummar Ghana bisa jajircewar da suka yi na tabbatar da tsarin dimokuradiyya, wanda hakan ke nuni da yadda aka gudanar da babban zaben kasar a ranar 7 ga watan Disamban 2024 cikin lumana. Gaba daya tsarin zaben ya bi ka’idodin yankin kasa da kasa, da kara karfafa kimar dimokradiyyar Ghana.

ADVERTISEMENT

Alhaji Mohammed Namadi Sambo, tsohon mataimakin Shugaban Nijeriya kuma jagoran tawagar sa ido a kungiyar ECOWAS, ya ce masu kada kuri’a sun yi zabe cikin yanayi mai kyau, ba tare da tsangwama ko takurawa ba. Ta kuma taya al’ummar kasar Ghana murna. ‘Tawagar masu sa ido kan zabe ta Ecowas na taya al’ummar Ghana murna, tare da yi musu fatan ci gaba da samun zaman lafiya, daukaka, da ci gaba.”

Kungiyar sa ido ta ECOWAS ta jinjinawa Shugaban Ghana mai barin gado, Nana Akufo-Addo bisa yadda ya jagoranci kasar na shekaru 8, daya daga cikin mambar kungiyar.

LABARAI MASU NASABA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

Kungiyar sa ido ta Commonwealth a karkashin jagorancin tsohon Shugaban kasar Botswana, Dokta Mokgweetsi Masisi ta ce, sun lura an bai wa nakasassu da tsoffi fifiko kuma an ba wa masu fama da matsalar gani da ido hakkinsu a wasu rumfunan zabe. Sai dai kuma sun lura da kalubale a wasu rumfunan zabe don wurin kada kuri’a ya yi wa masu amfani da keken guragu nisa.

Ya kara da cewa, ‘Rahoton su na karshe mai dauke da muhimman shawarwari za su mika shi ga babban sakatare kuma a raba shi zuwa ga gwamnatin Jamhuriyyar Ghana da sauran masu ruwa da tsaki da sauran jama’a.

A gefen taron, tsohon mataimakin Shugaban Nijeriya, kuma jagoran tawagar kungiyar ECOWAS ya yaba wa hukumomi da al’ummar Ghana bisa yadda aka gudanar da zaben kan tsari, a hira ta musamman da Muryar Amurka.

Tsohon shugaban kasa, John Dramani Mahama, na babbar jam’iyar adawa ta NDC, wanda ya lashe zaben Ghanan da kashi 56.55 cikin 100 na kuri’un da aka kada, ya yi jawabin amincewa da nasararsa bayan da hukumar zabe ta ayyana shi, a matsayin wanda ya lashe zaben kasar a hukumance.

Ghana
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya
Kasashen Ketare

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

June 23, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Kasashen Ketare

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

June 22, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran
Kasashen Ketare

Iran Ta Ce Shirinta Na Makamai Masu Linzami Ba Ya Cikin Tattaunawa Da Amurka

June 18, 2026
Next Post
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Muhimmiyar Makalar Xi Mai Taken “Zurfafa Aiwatar Da Juyin Juya Halin Jam’iyyar Kwaminis Ta Sin”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Muhimmiyar Makalar Xi Mai Taken “Zurfafa Aiwatar Da Juyin Juya Halin Jam'iyyar Kwaminis Ta Sin”

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.