ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kuskure Goma (10) Da Matan Aure Ke Yi A Gidan Miji

by Bilkisu Tijjani
1 month ago
aure

Na (9) dana (10) su ne mafi muni

1. Tattauna sirrin matsalolin gidan miji da abokai da dangi:

A kowane gidan aure ana samun matsaloli, sai dai masu hankali acikin matan aure ke boyewa su bar komai a wurin Allah. Daukan sirrinki da mijinki ki sanar da wasu yana kawo babbar matsala a rayuwar aure.

ADVERTISEMENT

2. Yawan tattauna matsalolin miji da kushe kokarinsa a gaban ‘ya’yansa:

Wannan yana sa yara su raina kokarin da mahaifinsu ke yi acikin gida

LABARAI MASU NASABA

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa

3. Cusawa yara kiyayyar amaryar mahaifinsu (kishiya):

Wata rana za ki iya mutuwa ki bar yara a hannun kishiya ko rashin lafiya mai tsanani. To idan kin cusa musu kiyayyar, wannan zai iya haifar matsala babba a tsakaninsu.

4. Kiyayyar yaran kishiya da neman ganin bayansu:

Shin ko kin san cewa Allah zai iya daukaka ‘ya’yan kishiryarki su zamo manyan mutane masu daraja wata rana?

Sannan kuma su zama sune masu daukan nauyinki, to idan Allah ya kaiki wannan lokacin da wanne ido za ki kallesu.

5. Gasar haihuwar yara domin samun kaso mafi girma acikin gadon dukiyar miji:

Shin ko kin san cewa mijinki zai iya talaucewa kamin mutuwarsa? Ko kuma keki da yaran ku rigashi mutuwa.

6. Tunanin cewa miji zai mutu ya barki da yara a cikin wahala:

Waye ya sanar da ke cewa miji ke fara mutuwa ya bar matarsa? Mata sun fi yawan mutuwa su bar mazajensu sanadiyyar (haihuwa, hawan jini, ciwon sikari, tashin gobara a gida, kunar ruwan zafi, da sauransu.

Idan ki ka je assibiti, zaki samu mafi yawan masu jinya a (Dakin karban agaji na gaggawa na mata, da ICU) mata ne da kananan yara, kalilan ne maza acikinsu.

7. Kyauta acikin dukiyar miji ba tare da saninsa ba:

Dukiyar miji amana ce a gareki, dole ki sanar dashi duk abunda za ki aikata acikin dukiyarsa.

Ko bako zai shigo gida (mace ko namiji) dole ki sanarda miji domin neman yardarsa da amincewarsa.

8. Fifita bukatun naki dangi sama da dangin miji:

‘Yan uwa da dangin miji su ne sukafi kusanci dashi sama da dangin matarsa, kar ki tilasta mijinki yiwa danginki dawainiyar da baya yiwa nashi dangi.

9. Rashin godiya da hango ni’imar gidan wasu:

Dawainiyar gidan aure tana da yawa sosai, sai jarumi acikin maza ke iya daukar nauyin matarsa da yara na tsawo shekaru 10, 20, 30, ko 40

Abinci, sutura, sabulai, magani, ruwan sha, kudin lantarki, kudin gas, kudin makarantar yara, kudin tafiya mataranta da kai yara makaranta.

Wallahi duk matar dake raina kokarin mijinta, ba zatayi karshe mai kyau ba.

10. Sabawa miji da goyon bayan yara zuwaga barna:

Duk abunda yara ke aikatawa acikin gida, mahaifiyarsu ta san komai.

Wasu mata za su goyi bayan yara zuwaga barna saboda son zuciya irin nasu.

Idan miji ya hana yara fita, sai bayan mijin yaje aiki ko kasuwa sai mahaifiyarsu ta basu izinin fita.

Idan miji ya hana yara zuwa biki, mahaifiyarsu ta basu izini.

Idan miji ya hana yara fita babu hijabi, sai mahaifiyarsu ta basu damar fita da gyale.

Idan miji ya hana yara fita yawon banza, ko mu’amala da abokan banza, sai mahaifiyarsu ta basu izini.

Idan wani abu ya faru marar kyau, sai mahaifiyarsu tace kaddara ce kowa da irin tasa.

Matan aure
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa

MASU ALAKA

Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)
Uwargida Sarautar Mata

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 21, 2026
Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa
Uwargida Sarautar Mata

Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa

May 30, 2026
Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki
Uwargida Sarautar Mata

Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki

May 24, 2026
Next Post
Matan aure

Aure Ba Sana’a:Imani Ko Ganganci?

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.