ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyamar Baki: Majalisa Ta Bukaci Tinubu Ya Janye Lasisin Kamfanonin Afrika Ta Kudu

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
4 weeks ago
majalisar kasa

Sanata mai wakiltar Edo North, Adams Oshiomhole, ya bukaci Gwamnatin Tarayya ta dauki matakan tattalin arziki masu tsauri kan kamfanonin Afirka ta Kudu da ke aiki a Nijeriya, sakamakon sabbin hare-haren kiyayya (denophobia) da ake kai wa ‘yan Nijeriya a South Africa.

Yayin da yake gabatar da batun a zaman majalisar dattawa a ranar Talata, Oshiomhole ya bukaci a wuce matakin korafi na diflomasiyya kawai, a rungumi manufar mayar da martani daidai da abin da aka yi (reciprocity).

Ya ba da shawarar musamman a janye lasisin MTN Nigeria, yana mai cewa ‘yan kasuwar Nijeriya za su iya cike gibin da hakan zai haifar.

ADVERTISEMENT

“Ba na son wannan Majalisa ta rika zubar da hawaye… Idan ka buge ni, zan buge ka. Wannan gwagwarmaya ce ta tattalin arziki,” in ji shi, yana mai cewa irin wannan mataki mai karfi zai tilasta hukumomin Afirka ta Kudu su dauki tsaron ‘yan Nijeriya da muhimmanci.

Oshiomhole ya jaddada cewa ‘yan Nijeriya da ke Afirka ta Kudu masu bayar da gudunmawa ne ga tattalin arziki, ba masu dogaro da wasu ba ne. Ya yi gargadin cewa ci gaba da jure irin wadannan hare-hare na aika sako mara kyau tare da raunana ikon Nijeriya na kare ‘yan kasarta da muradunta.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

A cikin kuduri mai maki shida, Majalisar Dattawa ta bukaci Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta fara tattaunawa a matakin koli da South Africa da kuma Ghana domin kare ‘yan Nijeriya a kasashen waje tare da samar da tabbacin da za a iya aiwatarwa don hana aukuwar irin hare-haren a gaba.

Majalisar ta kuma nemi a gudanar da cikakken bincike na gaskiya da zaman kansa kan dukkan hare-haren da aka ruwaito, tana mai jaddada cewa dole ne a gano masu laifi da masu daukar nauyinsu, a kama su, a gurfanar da su a gaban kuliya, sannan a hukunta su bisa doka.

A wani bangare kuma, Majalisar Wakilai ta bukaci Gwamnatin Tarayya ta sake duba dukkan yarjejeniyoyin hadin gwiwa da Afirka ta Kudu, tare da dakatar da bayar da izinin kasuwanci ga sababbin kamfanonin Afirka ta Kudu da ke son aiki a Nijeriya, sakamakon sabbin hare-haren kiyayya ga ‘yan Nijeriya.

An amince da wannan kuduri ne a zaman majalisar na ranar Talata bayan wani kudiri da Donald Ojogo ya gabatar.

‘Yan majalisar sun nuna damuwa kan tsaron ‘yan Nijeriya a Afirka ta Kudu, tare da kira da a dauki matakai masu karfi don kare ‘yan kasa da muradun kasa.

A matsayin wani bangare na kudurin, Majalisar ta bai wa kwamitocinta na harkokin kasashen waje da ‘yan kasa mazauna kasashen waje, da kuma na hadin gwiwa a Afirka, umarni su yi hulda da ofishin jakadancin Nijeriya da ke Pretoria.

Kwamitocin za su taimaka wajen kafa cibiyar ba da agajin gaggawa ta awa 24 da kuma asusun taimakon shari’a domin tallafa wa ‘yan Nijeriya da ke fuskantar matsaloli a Afirka ta Kudu.

Majalisa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Majalisa
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
An Bude Taron Karawa Juna Sani Kan Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Na 2026

An Bude Taron Karawa Juna Sani Kan Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Na 2026

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.