ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyamar Baki: Majalisa Ta Bukaci Tinubu Ya Janye Lasisin Kamfanonin Afrika Ta Kudu

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
2 months ago
majalisar kasa

Sanata mai wakiltar Edo North, Adams Oshiomhole, ya bukaci Gwamnatin Tarayya ta dauki matakan tattalin arziki masu tsauri kan kamfanonin Afirka ta Kudu da ke aiki a Nijeriya, sakamakon sabbin hare-haren kiyayya (denophobia) da ake kai wa ‘yan Nijeriya a South Africa.

Yayin da yake gabatar da batun a zaman majalisar dattawa a ranar Talata, Oshiomhole ya bukaci a wuce matakin korafi na diflomasiyya kawai, a rungumi manufar mayar da martani daidai da abin da aka yi (reciprocity).

Ya ba da shawarar musamman a janye lasisin MTN Nigeria, yana mai cewa ‘yan kasuwar Nijeriya za su iya cike gibin da hakan zai haifar.

ADVERTISEMENT

“Ba na son wannan Majalisa ta rika zubar da hawaye… Idan ka buge ni, zan buge ka. Wannan gwagwarmaya ce ta tattalin arziki,” in ji shi, yana mai cewa irin wannan mataki mai karfi zai tilasta hukumomin Afirka ta Kudu su dauki tsaron ‘yan Nijeriya da muhimmanci.

Oshiomhole ya jaddada cewa ‘yan Nijeriya da ke Afirka ta Kudu masu bayar da gudunmawa ne ga tattalin arziki, ba masu dogaro da wasu ba ne. Ya yi gargadin cewa ci gaba da jure irin wadannan hare-hare na aika sako mara kyau tare da raunana ikon Nijeriya na kare ‘yan kasarta da muradunta.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

A cikin kuduri mai maki shida, Majalisar Dattawa ta bukaci Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta fara tattaunawa a matakin koli da South Africa da kuma Ghana domin kare ‘yan Nijeriya a kasashen waje tare da samar da tabbacin da za a iya aiwatarwa don hana aukuwar irin hare-haren a gaba.

Majalisar ta kuma nemi a gudanar da cikakken bincike na gaskiya da zaman kansa kan dukkan hare-haren da aka ruwaito, tana mai jaddada cewa dole ne a gano masu laifi da masu daukar nauyinsu, a kama su, a gurfanar da su a gaban kuliya, sannan a hukunta su bisa doka.

A wani bangare kuma, Majalisar Wakilai ta bukaci Gwamnatin Tarayya ta sake duba dukkan yarjejeniyoyin hadin gwiwa da Afirka ta Kudu, tare da dakatar da bayar da izinin kasuwanci ga sababbin kamfanonin Afirka ta Kudu da ke son aiki a Nijeriya, sakamakon sabbin hare-haren kiyayya ga ‘yan Nijeriya.

An amince da wannan kuduri ne a zaman majalisar na ranar Talata bayan wani kudiri da Donald Ojogo ya gabatar.

‘Yan majalisar sun nuna damuwa kan tsaron ‘yan Nijeriya a Afirka ta Kudu, tare da kira da a dauki matakai masu karfi don kare ‘yan kasa da muradun kasa.

A matsayin wani bangare na kudurin, Majalisar ta bai wa kwamitocinta na harkokin kasashen waje da ‘yan kasa mazauna kasashen waje, da kuma na hadin gwiwa a Afirka, umarni su yi hulda da ofishin jakadancin Nijeriya da ke Pretoria.

Kwamitocin za su taimaka wajen kafa cibiyar ba da agajin gaggawa ta awa 24 da kuma asusun taimakon shari’a domin tallafa wa ‘yan Nijeriya da ke fuskantar matsaloli a Afirka ta Kudu.

Majalisa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci
  • Sulaiman
    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
  • Sulaiman
    Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
Majalisa
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
An Bude Taron Karawa Juna Sani Kan Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Na 2026

An Bude Taron Karawa Juna Sani Kan Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Na 2026

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.