Sanata mai wakiltar Edo North, Adams Oshiomhole, ya bukaci Gwamnatin Tarayya ta dauki matakan tattalin arziki masu tsauri kan kamfanonin Afirka ta Kudu da ke aiki a Nijeriya, sakamakon sabbin hare-haren kiyayya (denophobia) da ake kai wa ‘yan Nijeriya a South Africa.
Yayin da yake gabatar da batun a zaman majalisar dattawa a ranar Talata, Oshiomhole ya bukaci a wuce matakin korafi na diflomasiyya kawai, a rungumi manufar mayar da martani daidai da abin da aka yi (reciprocity).
Ya ba da shawarar musamman a janye lasisin MTN Nigeria, yana mai cewa ‘yan kasuwar Nijeriya za su iya cike gibin da hakan zai haifar.
“Ba na son wannan Majalisa ta rika zubar da hawaye… Idan ka buge ni, zan buge ka. Wannan gwagwarmaya ce ta tattalin arziki,” in ji shi, yana mai cewa irin wannan mataki mai karfi zai tilasta hukumomin Afirka ta Kudu su dauki tsaron ‘yan Nijeriya da muhimmanci.
Oshiomhole ya jaddada cewa ‘yan Nijeriya da ke Afirka ta Kudu masu bayar da gudunmawa ne ga tattalin arziki, ba masu dogaro da wasu ba ne. Ya yi gargadin cewa ci gaba da jure irin wadannan hare-hare na aika sako mara kyau tare da raunana ikon Nijeriya na kare ‘yan kasarta da muradunta.
A cikin kuduri mai maki shida, Majalisar Dattawa ta bukaci Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta fara tattaunawa a matakin koli da South Africa da kuma Ghana domin kare ‘yan Nijeriya a kasashen waje tare da samar da tabbacin da za a iya aiwatarwa don hana aukuwar irin hare-haren a gaba.
Majalisar ta kuma nemi a gudanar da cikakken bincike na gaskiya da zaman kansa kan dukkan hare-haren da aka ruwaito, tana mai jaddada cewa dole ne a gano masu laifi da masu daukar nauyinsu, a kama su, a gurfanar da su a gaban kuliya, sannan a hukunta su bisa doka.
A wani bangare kuma, Majalisar Wakilai ta bukaci Gwamnatin Tarayya ta sake duba dukkan yarjejeniyoyin hadin gwiwa da Afirka ta Kudu, tare da dakatar da bayar da izinin kasuwanci ga sababbin kamfanonin Afirka ta Kudu da ke son aiki a Nijeriya, sakamakon sabbin hare-haren kiyayya ga ‘yan Nijeriya.
An amince da wannan kuduri ne a zaman majalisar na ranar Talata bayan wani kudiri da Donald Ojogo ya gabatar.
‘Yan majalisar sun nuna damuwa kan tsaron ‘yan Nijeriya a Afirka ta Kudu, tare da kira da a dauki matakai masu karfi don kare ‘yan kasa da muradun kasa.
A matsayin wani bangare na kudurin, Majalisar ta bai wa kwamitocinta na harkokin kasashen waje da ‘yan kasa mazauna kasashen waje, da kuma na hadin gwiwa a Afirka, umarni su yi hulda da ofishin jakadancin Nijeriya da ke Pretoria.
Kwamitocin za su taimaka wajen kafa cibiyar ba da agajin gaggawa ta awa 24 da kuma asusun taimakon shari’a domin tallafa wa ‘yan Nijeriya da ke fuskantar matsaloli a Afirka ta Kudu.















Discussion about this post